Kallonta AFIA takeyi tana kore duk wani tunanin abinda tagani ta juyarda zancen da cewa"
Kije kicire kayan kada sanyi yakamaki tunda juice din nada sanyi ga ac Kuma a bayanki Yana aiki.
Kasa wucewa tayi ta matso kadan tana kallon fuskan AFIA din a Dan daburce tace"
Afia Farhat ta turani da jug na juice a hannuna duka abinda yafaru ma mistake ne sbd Ni bansanma meya meya......
Cikin sauri AFIA ta katsetada cewa"
Relax relax ok,kije kicire kayan ki gyara jikinki wannan abin da kike magana is nothing sbd dad tamkar mahaifinki ne so there's no way dama wani tunanin zaishigo kanmu mu duka ki manta komai daga Nan gurin ok??
Jin hakan yasa jikinta Kara sanyi ta juya ta wuce daki,
tana shiga toilet ta nufa acan ta tube tayi wanka ta zuba kayan a washing machine ta fito daure da towel light blue.
Riga da wando na bacci ta Sanya masu kauri tareda hula ash tayi sallar ishai ta kwanta sbd duk Jin ranta take ba Dadi.
Tana kwantawa farhat ta shigo dakin sanye da kayan bacci irin nata ta qaraso gefenta ta kwanta ahankali jikinta tana cewa"
Sorry my Lewa.
Tana Jin farhat din sbd batai bacci ba sai ta gyara musu kwanciya tareda ja musu bargo sukai bacci.
AFIA ma Bata Dade a Palo ba tashigo tayi Shirin kwanciya ta hau gadon ta kwanta tana kallon farhat datake bacci cikin nutsuwa tamkar jaririn dake bacci cikin dumin mahaifiyarsa
Farhat tana yiwa NURU wani irin so da kauna na shaquwar jini Wanda kwata kwata babushi atsakaninta da mum dinsu.
Maida kallonta tayi kan kyakkyawar fuskar NURU dake bacci kamar baby
Takai hannu ta gyara Mata hular kanta cikin kulawa da kaunar NURUn cikin ranta tana cewa"
Sorry NURU,
Kauna da soyayyar mahaifiyata yaso shiga tunanina,
Naji tsoro matuqa a dazun sbd Babu wani gurbi dazan iya gani na mahaifiyata wani ya cikesa dan haryanzu ban cirewa alaqarta da dad Rai ba kiyi hkr NURU bansan meya shiga kainaba har nabari hakan yaso bani tsoro bayan dad is like a father to you Inshallah bazan taba Bari hakan tasake faruwa duk aikin shedan ne.
Lumshe idanuwanta tayi take bacci ya dauketa tana sakejin kaunar NURU.
Washe gari lafiya kalau suka tashi abinsu cikin kulawa da juna Kamar yanda suke,
Ita tayi breakfast Kuma dukkanin abinda tasan dad din naci shitayi aka jere a dining takoma cikin acan tayi nata breakfast din Takoma daki tayi wanka bayan tafara gama Shirin Farhat itama ta shirya tsaf cikin black palazzo trauser da white ladys long sleeve sai black wedges shoes ta fito daukeda handbag dinta tareda afia da itama take a shirye tsaf suka fito driver na jiransu suka shiga suka wuce.
Tunda suka Isa school takejin hankalinta ba'a kwance ba fargaba da tsoron abinda zai iya faruwa takeji idan har Imran yayiwa MALEEK maganar neman aurenta Wanda takega idan hakan tafaru ta take doka me qarfi tareda tsaurin ido da kawo reni.
Dafe kanta tayi tanajin kanta kaman ze buga ta fiddo wayar daga cikin jaka bayan ta fito daga first class dinta ta saka Kiran Imran din.
Cikin kulawa ya dauka da sanyayyar muryarsa me Dadi yace"
Hello baby how are you doing?
Kasa maganar tayi sbd batasan me zatace Masa ba Kai tsaye sbd Babu ta yanda zata iya fada Masa ita negestati ce ta waya.
Hello sweetie are you there??
Dawowa tayi hankalinta daga Nisan datayi a tunani ta gyara murya cikin sanyi tace"
Dama inason ganinkane we need to talk akan maganan jiya.
Gyara zama yayi daga inda yake Yana cewa"
Akwai matsala ne?
No Inason muyi maganar ne dakyau kafin akaita gaba.
Shiru yayi na tsawon mintuna kafin yace"
Ok karki damu koma menene Ina Nan zanyi handling komai yatafi smoothly
Idan kingama ki kirani I will come and pick you up.
Gyada Kai tayi kaman Yana ganinta tareda kashe wayar ta maida jaka ta miqe daga coffee shop din datake zaune takoma.
Sai yamma sosai suka fito kusan lokaci daya da Afia Dan haka Dole tare zasu tafi gidan Dan haka suka bi motar Imran sukace driver yakoma kawai.
Ganin afia na taredasu yasa tafasa Masa magana sai kawai suketa fira su dukansu musamman akan karatunsu da yanzu suka fara nisa sai 'yar soyayyarsu dasuke jefi jefi ta hanyar kallon juna da kalmomin kulawa Wanda duk yake qara burge afia take ganin ba qaramin dacewa sukai da junaba.
Koda suka iso gida dukkaninsu tare suka fito afia na gaba suna bayanta Imran na Mata magana ahankali Yana kallonta kaman ze hadiyeta da so da kulawa.
Ita Kuma dayake duk a Sanyaye take sai yake ganin kaman yangace take Masa duk yasake sukurkurcewa Wanda ba hakan bane agurinta.
Suna shigowa palon farko itace agaba sbd afia tuni ta shige shikuma Yana gefenta cikin dibbin mamakinta da tsoronta MALEEK suka gani zaune a palon abinda bayayi hannunsa riqeda waya yanayi cikin turanci da yarensa na Amharic Wanda yasa su duka fahimtar da gida yake waya dama mahaifiyarsa sbd Jin yafada sunanta cikin yare.
Dukkaninsu sunsan ko zasu rube agurin bazai dago ya kallesuba musamman ma ita da tana shigowa fararen idanuwansa masu girma acikin nata suka fara sauka tayi saurin sauke Kai zuciyarta na harbawa
Bata tsaya wata wataba ta wuce ciki sum sum tabar Imran a gurin Wanda shikuma ya gyara zaman jiran MALEEK sbd gabatarda kansa amatsayin me neman auren NURU da neman izinin turowa a nema Masa aurenta.
Zaman jiran MALEEK ya dasa tsawon lokaci me tsayi Wanda harya fara sarewa sbd ganin kaman lokacin basa ne MALEEK din bayada Amma bazai sareba haka yayita jira har maleek din yagama.
Barka da dare MALEEK.
Kallo daya MALEEK yayi Masa ya maida kansa kan wayarsa dake sake daukan ringing ya gyada Masa Kai alamar amsawa.
Gyara zama da gyaran murya duk yayi lokaci daya Imran din Yana saka nutsuwa a muryarsa yace"
MALEEK Ina neman izini ne na shigowa neman auren NURU idan an...
Dakatawa yayi daga zancen Yana gyara zamansa sbd ganin kaman MALEEK din baiji abinda yafara fada ba.
Sake bude Baki yayi zaiyi magana MALEEK ya dago ya kallesa da kyau a karon farko da yayi Masa kallon tsaf
Ya bude bakinsa cikin dakakkiyar muryarsa me izza da kamewa yace"
Nayi waya da santiano albeiriteo gobe zasu sauka France jibi zamuyi board meeting na signing contract dinsu
Get yourself ready Kaine zaka kula da contract din har gamawansa.
Yana fadar hakan ya miqe yabar palon Imran yabisa da kallo da idanuwansa dasukai kaman zasu ciko da hawaye,
Shin MALEEK be jisa bane kokuwa zancen ne bai fahimta ba?
Shafa Dan zufan tashin hankalin da fargaban daya tsatsafo Masa yayi duk sanyin AC daya gama gauraya babban Palon Yana girgiza Kai cikin cire negative thoughts yace"
Baiji Mena fadaba gobe zanzo after breakfast nayi Masa bayani daidai.
Miqewa yayi ya fice Yana maida hankalinsa Kuma gurin contract din santiano albeiriteo da MALEEK din ya basa shugabancin handling Wanda bazai taba samun lokacin kansaba tsawon lokaci sbd contact din nada tarin ayyukanda bazasu barka ko lokacin samun nutsuwan bacci me Dadi kayi.,
Tabbas zaizo gobe yakai qarshen maganarsa da NURU agurin maleek kafin aikin yasa yarasa lokaci duk da hakan zai Kira dad dinsa akan maganar.
##MAMUH#
*Assalamu alaikum warahmatullah, shin kinaba amfani da turaren gashi a matsayinki na mace data amsa sunanta idan amsarki aa toga dama tasamu *awwaba scent* *tazomaku* *da turaren fesawa a gashi natural 100% organic *wanda akahada rose water da essential oils tripped action gashi yy kamshi yay kyali kuma moisturiser at *the same time ba anan abun yatsayaba duk wanda yy order zaahada masa da freshener kala hudu ta daki *ta bandaki ta Mopping da turaren wanka a kan kudi 3,000 kacal indai q cikin watan September dinnna ne daganan kuma zasukoma *normal price dinsu, hakanan turarukqn wuta da humra dinmu anyi masu ragi duk me bukata se nememu a 08034236800 ta what's app kokuma ya ziyarci shafinmu a instagram *@turare_by_awwaba mungode*
****************
Washe gari tunda safe yasake dawowa gidan Dan ganawa da maleek Amma sbd rashin sa'a Koda yazo maleek din yafita haka ya juya jiki amace yakoma gida da niyar ya dawo anjima Dan Dole Dole tsakanin yau zuwa gobene damarsa ta qarshe ta ganawa da maleek sbd jibi Ana fara aikin Santiago Babu ranarda zai samu kansa harya samu damar magana dashi.
Ta bangaren NURU itama gabaki daya ta rasa sukuni da walwalarta akan zancen Dan ko abincin kirki tadaina ci kullum saidai tea sbd fargaba da tsoron abinda zai iya kaiwa ya komo
Duk yanda Afia tayi tayi da ita akan abinda yake faruwa takasa Mata bayani dataga kaman ran afian ya baci ne saita fada Mata da Imran nason turowane ita Kuma tana tsoron karatuntane kawai da haka afia ta zaunar da ita tabata wani qwarin gwiwan barin Imran din yayi zancen tahakane zataji idan abin me yiyuwa ne.
Hakan yasa tadan rage damuwar abin cikin ranta tafara jiran tsammani.
IMRAN kuwa Kai yayi mugun daukan zafi sbd duk wata hanyar dazai gana da maleek ta toshe har abin yafara bashi tsoro sai kawai ya yanke shawaran fadawa mahaifinsa Dan shi dakansa ya nema MALEEK din.
Zaune suke a dining suna dinner Kiran FORMER M.AMB JALALUDDEEN yashigo wayarsa yayiwa wayar kallo daya yaci gaba dacin abincinsa a natse harsaida yagama zuwa lokacin yayi Masa Kira kusan hudu sai Ana biyar din ya daga cikin kamewa da ikon sarauta dake yawo cikin jikinsa ya amsa sallamar M JALALUDDEEN suka gaisa a mutunce gaisuwa irinta dattijai manyan mutane kafin M JALALUDDEEN yafara da cewa"
MALEEK nayi kirane akan maganar aure da Imran yakeson yarinyar gurinka wadda yace sunriga sunfahimci juna sosai da ita to.....
Wata nutsatsiyar gyaran murya MALEEK yayi a natse wadda duk wanda yasan mulki da sarauta yasan dakatarwane ga zancen da ake Dan haka M JALALUDDEEN ya dakatar da abinda yake fada
Kai tsaye MALEEK cikin kamewar muryarsa me nuna isarsa yace"
Wannan maganar ba'ayin irinsa a waya.
Hakane tabbas Bata waya bace MALEEK to kabada lokacinda zamuzo sai ayi maganar akai qarshe Inshallah.
Kallon agogo yayi alamar zancen na shiga lokacinsa Dan haka Kai tsaye yace inada tafiya gizah agabana banida lokacin bayarwa idan nasamu time zangani Inshallah.
Daga haka sukai sallama Yana aje wayar AFIA dataji ya ambaci tafiya gizah hankalinta yayi mummunan tashi ta kallesa cikin son tabbatarwa tace"
Dad zakaje delah gizah??
Yana miqewa yace"
Eh Anneti tasamu attack na zuciya yau da safe.
Yana fadar hakan ya wuce gabaki daya.
Bin bayansa tayi da kallo zuciyarta na bugawa tana nanata zancen tafiyar.
Kasa yadda da tafiyar dad dinta zuciyarta tayi dari bisa dari sbd zuwansa zai iya kawo komai na lalacewan faranta da adduar datai shekaru tanayi na ganin dawowar iyayenta tare,
Shin Tata dad zaije delah gizah yanzu bayan zuwansa batareda matarsaba zai bayyanawa duniya cewan sun rabu Wanda hakan daidai yakeda rasa qimarsa da darajarsa hakama Kuma hakan zai jawo kokuma bada damar shigowar wata cikin rayuwar mahaifinsu ko Mata ko negestati.
Dafe kanta dake neman tarwatsewa sbd tsananin tarin damuwa data sawa kanta akan wani irin zazzafan kishi datake jiwa mahaifiyarta Dan haka bazata iya Bari dad yayi tafiyar Nan gizah ba sbd sanin tsananin qarfin iko da dokoki tareda al'adun mulkin irin na delah gizah.
NURU dake cikin Tata damuwar me nauyi tana zaune gefen AFIA din taji yanda takeda sauke ajiyar zuciya alaman Bata cikin kwanciyar hankali ko daya ta bude Baki ahankali cikin kulawa tace"
AFIA kinada damuwan wani abune?kimata sauke ajiyan zuciya.
Kasa waiwayowa tayi takalli NURUn sbd idanuwanta dasukai zuru zuru sbd masifar data sakawa ranta ta kishin mahaifinta ga wata mace
Batareda ta juyoba tace"
Bakomai kawai kaina na ciwo ne shima inaga sbd rashin bacci ne da bansamu nayiba jiyan.
Kafin NURU tayi magana ta miqe ta nufi toilet tashige ta rufo qofa.
Hawaye takeson Yi Amma ta daure tana kallon fuskarta cikin mirror ta rintse ido tana Jin shin mum dinta ta cancanci wannan fadan datake tare Mata kuwa?
Shin idan ta dage ta Hana dad dinta rayuwa da wata mace akan Taya mum dinta kishi tayi adalci a tsakaninsu kuwa bayan mum din itace ta lalata komai tayi watsi dasu ta tafi neman duniya wadda idan ba Allah yasoba har abada bazata samu duniya irinta dad dinsu ba.
Share hawayenta tayi tareda wanke fuskarta ta dauro alwalar azahar datai ta fito tana qoqarin sakewa Dan kawarda tambayoyin NURU akanta.
NURU dake binta da ido ganin babu damuwar komai a kan fuskan AFIA din sai tabar tamabayarta tana sauke numfashi Dan harta fara shiga tunanin kodai maganartane da Imran tazama matsala tunda tasanma kila zuwa yanzu yagama fadawa MALEEK komai.
Farhat ce tashigo daukeda littafi a hannunta tayo gurin NURU ta zauna kan cinyarta tana cewa"
Lewa nakasa gama wannan dubamin kigani.
Sallah Afia ta tayar tana dauke tunaninta daga kansu sbd Sam Babu Wanda zai gane abinda takeji.
Tana idar da sallar tadawo cikinsu suka cigaba da abinda sukeyi da ita Dan tasamu ta fitarda tunani da damuwardake azalzalar ranta.
Har dare tana sintirin yawo tsakanin Palo da 'dakinsu akai akai sbd tanason ganin dad dinta akan ko tafiyarsa delah gizah na Nan.
Har suka kwanta Bata samu ganin dad dinba sbd bai dawoba koya dawo ya wuce sama ya shige Bata saniba gashi tana Kiran Mr Omar Amma wayan Bata shiga haka ta hakura ta kwanta badan taso ba.
Washe gari da safe daga NURU har Farhat sun wuce makaranta ita kadaice Bata tafiba sbd ta sakawa ranta zata zauna harsai tasamu yin magana da dad dinta.
Guraren 11 na safe kuwa saigashi ya sauko qamshinsa na gauraya palon ahankali ahankali sai kyakkyawar fuskarsa dake kame kamar koyaushe
Tai Masa kallon qaunarsa amatsayinsa na mahaifinta datake tsananin kauna da alfahari dashi ta miqe tsaye tana aje laptop din dake kan cinyarta tana amfani da ita ta saki wani siririn murmushi tana qarasawa gurinsa tace"
Good morning dad,barka da fitowa.
Kallon kyakkyawar fuskarta dake yanayi da tasa yayi Yana alfahari da ita sbd juriyarta da iliminta tareda hakurinta ya bude Baki da muryarsa me amon iko yace"
Morning li'iliti(princess)
Murmushi tasake saki tana kallon dining din dayake qoqarin zama tace"
Dad can I join you?
Batareda ya dagoba yace"
Sure princess.
Janyo kujeran dining din tayi ta zauna tana cewa" thank you abal.
Tsit gurin ya dauka suna cin abinci Babu me mgnar sai ita dake cin abincin ahankali sbd son fara kawo zancen tagaji da wasi wasin yin zancen ko kartayi kawai saita kasa dannewan ta aje spoon din hannunta a natse ta kallesa da taushin murya tace"
Dad Yaya jikin Anneti(sarauniyar mahaifiya/mahaifiyarsa)
Zaka tafi tafi gizah kenan dad?
Dan kallonta yayi tareda sassauta fuskarsa ya gyada Mata Kai.
Sake gyara zama tayi cikin tausasa harshenta da bayyanarda damuwar data Dade da dannewa cikin ranta da biyayyarta ga dad din nata tace"
Dad maganarku da mum zai fito fili idan kaje....shiru ta Dan Yi tana kallon kamewar fuskarsa ta daure taci gaba da cewa"
Idan zancen ya bayyana cewan mum ta tafiyarta tabar...... kallo daya yayi Mata da fararen idanuwansa takasa qarasa sauran zancen ta marairaice fuska tace"
Dad please ko zaka duba kagani kodan sunan mum da naka dazai iya baci.
Tissue ya dauka ya goge bakinsa tareda Miqewa tsaye ya kalleta yace"
Take care princess"ya wuce.
Kasa motsawa tayi kanta na toshewa sbd hakan na nufi zancenta be karbu ba agurin dad dinta sbd hakan da yayi shine rashin amintarsa ga zance idan ankawo Masa.
Miqewa itama tayi tabar gurin Takoma daki ta zauna ta jawo waya ta Nemo numbern mum dinta tafara tunanin takira ko karta Kira,
Fasa Kira tayi tai wurgi da wayar tareda Miqewa tsaye ta sauya Kaya ta fito tashiga mota ta fice daga gidan Dan zuwa dauko NURU datasan yanzu ta Isa gamawa tunda ita yau Bata samu zuwaba.
Tunda suka dawo taketa qoqarin cire damuwarta sbd kada NURU tagane saidai NURUn tana lure da ita saidai batason takura Mata da tambaya sbd batasaniba ko matsalar ta sirrice.
Kwana sukayi ahaka suka Kuma yini ahakan har akai kwana biyu
cikin kwana biyun duk ta Hana kanta sukuni da tunanin al'amarin Wanda take ganin rushewa familynta zaiyi idan wata tashigo cikinsu amatsayin matar dad dinsu ko negestati
Itadaima tafi son iyayenta su shirya koma menene hakan yafi shigowar wata cikinsu.
Ganin dai dagaske AFIA na cikin damuwa me qarfi boye kawai take yasa NURU kallonta bayan sun kwanta tace"
Afia koma menene abindake damunki please ki rage idan bazaki iya ciresaba ko hakura dashiba sbd wannan damuwan naki bamajin dadin ganinki ahaka ko farhat dake qaraman yarinya tafara cewa menene akaiwa AFIA.
Please AFIA kicire koma menene kibarwa Allah a rayuwa dama akwai hakan duk da nasan ke koma menene damuwan ba wani babba bane sbd Babu wani abu najin dadin duniya da Kika rasa Dan Allah ki cire damuwan please baby.
Tunda tafara magana afia ke kallonta sbd wani tunani daya shigota na sha'awar bin dad dinsu gizah Dan koma menene tafison tanacan zatafi samun saukin hanawa kokuma handling maganar rabuwar iyayenta taqi barin ta fita Dan kuwa tasan daga lokacinda maganar ta fita MALEEK na gizah bazai qara awa ashirin da huduba Batareda Matar aure ko negestati ba Dan haka zasu bishi Dan toshe yiyuwar hakan Dan kuwa idan hakan tafaru dad dinta bazai karbi mum dintaba har abada Wanda ita Kuma akan hakan ko kamawa tayi tayi amfani da NURU zatayi Dan Hana wata shigowa rayuwar dad din daidai NURU tayi hkr but she'll have to use her innocence.
Wani numfashi mara karfi ta saki tareda kallon NURUn cikin kauna da kulawa ta riqo hannunta ta rungume tace"
Thank you my NURU" ta rufe idanuwanta ahankali bacci na daukanta.
Washe gari haka ta tashi cikin walwalarta da sakewarta har hakan yasanya NURU da farhat farin ciki sosai har wasan ruwa da basketball sukai yau da yamma a playground Wanda duk abinda sukeyi dad dinsu na gidan dan haka Koda daddare yau taredashi sukai dinner Banda NURU dataqi fitowa tea kawaima Tasha sbd karatun data duqufa dayi Dan gobe tanada zuwa wani court yin wani aikin 4hours dake cikin karatunta.
Acan dining kuwa AFIA ta sanarwa dad dinta sunason binsa Dan Suma su dubo Anneti.
Kallonta yayi kadan tareda maida kallonsa kan farhat dake cewa"
Yes daddy Nima zanje Kuma zamuje da Aunt NURU ma ko AFIA?
Kallon bakin farhat din dako yaushe yake furta sunan NURU ko lewa yayi tareda dauke Kai Yana goge bakinsa yace su zama ready jibi ne tafiyar.
Cikin murna dukkaninsu sukace thank you dad.
Bayan fitarsa NURU tafara wucewa court kafin afia ita Farhat yau Babu zuwa school dinsu.
Sai yamma sosai suka dawo duk su dukansu Koda ta shigo tana waya da Imran da duk yabi ya sukurkurce Mata da cewan amatse yake da MALEEK yabawa su dad dinsa lokacin zuwa.
Murmushi kawai tayi sbd Bata taba tunanin maleek daya Bata ingantacciyar rayuwa tareda 'yayansa zai Bata ingantacciyar rayuwa ta har abada ba ta hanyar bada damar azo neman aurenta Dan tunda haryace idan yadawo zai Basu Daman zuwa ayi magana kenan da yiyuwar barinta tayi aure da rayuwar aure kaman kowaba babban mamakinta data kasa yadda dashi shine yau itace tasamu damar ace MALEEK na Delah gizah guda shine da kansa zai bada aurenta tabbas wannan tunanin idan yafado Mata kanta da tunaninta kasa dauka suke.
Ga tarin dibbin mamakinta tana shigowa Palo Imran suka tarar zaune Yana sako Mata murmushi da wani irin kallon Sonta daya gama yiwa tunaninsa da zuciyarsa mugun kamu saiyakejin kamar bazai iya rayuwa Babu itaba Dan kuwa komai zai iya faruwa dashi idan bai samu NURU ba amatsayin matarsa uwar 'yayan dazai Haifa.
Afia na ganin hakan ta wuce ciki tana Masa dariya da cewa"
Uncle Imran take it easy fa kada ka rasa 6sense dunka akan soyayya mu shiga uku barr IMRAN jalal ya zauce.
Da wata Yar dariyar qarfin hali yabi afia da zancenta idanuwansa suna Jan NURU dake tahowa cikin dogon wando da farar riga sai black scarf daure kanta duk da agajiye take sosai kyawunta ke bayyane tana qarasowa gap dashi ya miqa Mata cup din drink me sanyi da aka kawo Masa Yana cewa"
Have this my love kingaji ko?
Murmushi tasakar Masa takai hannu takarba takai bakinta ta kurba kenan idanuwanta suka sauka cikin na MALEEK dake tsaye da waya a kunnensa yanayi daga Palon ciki take ta qware da qarfi tana sakin tari ta miqawa Imran cup din tarinta na tsananta sosai
Cikin sauri da kulawa ya miqe Yana qoqarin Kai Mata cup din ruwa bakinta Tasha kozata ji sauki sauki sai kawai yaji anriqe cup din ya juyo da sauri sukai ido biyu da Mr Omar dake kallonsa cikin ido Ras ya Dan sake fuskar wata gantalalliyar murmushi tafito Masa yayiwa mum Sarah dayazo da ita kallo daya tayi saurin kallon NURU tana riqota tana Mata sannu tajata sukai ciki
Saida suka shige ya dago ya kalli Imran cikin girmamawar data so kularda Imran yace"
Barr IMRAN idan Babu damuwa zamu iya zuwa palon baqi dake gefen wannan sashen sbd dokokin gidan sun Dan qara tsauri yanzu Babu me sake shigowa sashen MALEEK dagashi sai 'yayansa.
##MAMUH#
_ZAFAFA BIYAR_💖💖💖
_Alkiblah--SAFIYYAH HUGUMA_
_Makauniyar qaddara--BILLYN ABDULL_
_Dalaal--MISS XOXO_
_Mabudin zuciya--HAFSAT RANO_
_Ubayd Maleek--MAMUH GEE_
_DUKA KUDIN WANNAN DADADAN BOOKS DIN SUNA KAN FARASHIN NERA 700. WATO KUDIN PAGES KENAN. DOCUMENTS IDAN AN KAMMALA SUMA KUDIN SU DABAN.._
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
*_Mamuhgee 18_*
Oumahmad collection's
07014488636
Kitchen utensils
Fabrics
Shoes nd bag
Phones
Veils
Children's wears
Furnitures
Dubai,china,India,turkey,Malaysia
Kano hotoro
Fcbk Maryam muhd.
**************
Shiru Imran yayi yana bin Mr Omar da ido baice komaiba sbd Kamar bai gama fahimtar me Mr Omar dinba yace Kuma baiyi abinda yace mishi yayin ba, kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya juya ya fice daga Palon Yana fita harabar gidan ya shiga motarshi ya fice Dan Yana buqatan samun iska me kyau Dan yayi refreshing kwakwalsa dayakejin kaman ta toshe baya gane komai.
Mr Omar mabayanshi yabi da wani irin kallo mai ma'anoni da dama, ciki kuwa harda na tausayawa dan ya hango tsantsar soyayyar Nuru a cikin kwayar idonshi wadda yasan abin kamar da wuya Dan kuwa zancen me girma ne dayafi qarfinsu su 'yan qasa qasa Dan kuwa yana da tabbacin aure tsakanin Nuru da Imran ba abune me yiwa ba duk da dai fadan hakan ba huruminsa bane.
Dan
A bangaren Nuru kuwa karfin hali kawai take har lokacin gashi AFIA ta nace Mata akan tafiyar da zasuyi sai anje da ita Wanda takega kaman ta wuce huruminta Binsu delah gizah ziyartar kakarsu uwa sukutum ta MALEEK,
Amma ganin batada zabi na kanta ko ikon kanta Dole ta shirya 'yan kayanta da basuda wani yawa yawancima dogayen riguna ne Dan Bata dauki me wando ko dayaba da zai nuna tasamu dama da sake da yawa.
Tana zaune jikinta a matukar mace tana qarasa hadawa Farhat kayanta cikin nata pink akwatin me hoton frozen sisters saiga Farhat din ta shigo da gudu ta zauna kan jikinta tana cewa"
My Lewa please kumana pancakes me Honey and chocolate.
Kallon bakinta NURU tayi tareda sake murmushi tana kamo fuskanta tayi kissing goshinta tana cewa"
Kome farhat din aunt NURU takeso za'a Mata.
Muje cikin din yanzu bada dadewaba zakici pancakes sweetie.
Kicin suka nufa tana riqeda hannunta suna shiga ta dorata kan kitchen island ta zauna ita Kuma tafara hadawa farhat din na tayata fira.
Bayan sun gama a kitchen din suka ci nasu saidai na AFIA suka aje Mata a dining.
dakinsu ta nufa ta tararda Afia a kan doguwar kujera rigingine idanuwanta a lumshe ta kifa littafi saman cikinta da alama karatu take bacci ya dauketa batare data sani ba.
Murmushi Nuru tayi ta gyara mata kwanciya ta lullube bargo me taushi kafin tayiwa Farhat wanka ta shiryata cikin kayan bacci marasa nauyi ta kwantar da ita anan dakinsu itama ta nufi toilet din tayo wanka tareda dauro alwala tayi sallar ishai kafin ta Sanya kayan bacci irin na farhat din riga da wando dogo saidai rigar batada hannu sai siriri hakama kayan nada roba ajiki sai suka kwanta jikinta sbd kusan kayan baccinsu su duka ukun duk za'a siyo iri daya ake siyowa saidai banbancin size.
Ta hau gadon zata kwanta farhat ta motsa cikin bacci tace"
Aunt NURU water please.
Kallonta tayi da idanuwanta dasuke Jin bacci tace"
Ruwa farhat??
Yes aunt.
Numfashi ta sauke tareda zuro qafafunta qasa ta saka slippers din dasuke yawo dashi cikin gida ta miqe tsaye tareda daukar qaramar hula ta saka akanta dabai rufe dukaba ta fito.
Al'adarshi ce fitowa cikin dare ya duba inda ya kamata saboda tsaro da fita hakk'in na k'asa dashi, yana kula da ransu da lafiyarsu, dan duk da Maleek ya kasance mutum mai izza da mulki hakan bai sashi ya manta dokokin Allah dake kanshi ba, yana k'ok'arin sosai wajen kaucewa hakk'in mutane, dan haka lokuta da dama yana fitowa cikin dare ya duba lafiyar iyalinshi da sauran mutanen gida.
Ba ruwanshi da lek'awa d'akin kowa dan yasan muhimmancin Privacy sosai iyakacinshi kawai ya duba inda ya kamata.
Ganin haske a cikin yasashi kallon hanyar tareda nufowa cikin nutsuwa saidai bai qarasaba sbd tunda take rayuwarsa nai taba shiga cikinba tun girmansa a iya saninsa Dan haka sai ya tsaya iya dining musamman dayaji kaman motsi a kicin din.
Itakuma daukeda robar ruwa biyu a hannunta ta fito batama lura da komaiba tabi ta gabansa ta wuce saidai taku daya ta qara ta tsaya cak zuciyarta na sauya bugawa sbd idan hancinta yajiyo Mata daidai qamshin MALEEK taji agurin.
Juyowa tayi ahankali Wanda yayi daidai da qarasowarsa zaibar gurin jikinsu ya hadu da sauri tayi baya tana sauke kanta kafafunta na son daukar rawa yayi Mata kallo daya ya wuce yabarta tsaye jikinta na neman yin sanyi sbd Tama rasa halin me tashiga a tsakanin tsoro da firgita.
Daqyar takai kanta daki ta tayarda farhat din zaune tana Bata ruwan abaki tana cikin Sha AFIA ta farka ta tashi zaune tana 'yar guntuwar hamma ta miqe ta nufi toilet.
Farhat data gama Shan ruwan da NURUn ke Bata ta daga Kai ta kalli NURUn tana sake shaqar jikinta tace"
Aunt NURU kina qamshin irin turaren daddy.
Cak Afia dake gaf da shiga toilet ta tsaya batareda ta waiwayo ba ta Kira Jin amsarda NURUn zata fadawa farhat din.
Kasa cewa komai NURU tayi sbd batasan mezata fada ba saidai jin alamar AFIA ta tsaya yasata bude Baki daqyar a Sanyaye tana kamo abinda zata samu cewa tace"
No sweetie hancin kine sbd kila kinyi mafarkin daddy yanzu da kikai bacci.
Kwantar da ita tayi tana cewa"
Koma bacci kinsan gobe akwai zuwa school da wuri gakuma tafiya gizah.
Ajiyar zuciya kusan suka sauke tareda AFIA ta zame ta kwanta gefen farhat din tana rufe idanu ba shiri itama Afian toilet din tashige tana sake sauke numfashi me sanyi.
Washe gari tun 8 ta fice zuwa school bayan tagama breakfast da Shirin farhat data wuce school itama ta wuce sbd Kira da massages dinda Imran keta danno Mata gabaki daya hankalinsa a tashe yake musamman data fada Masa cewan daita za'aje gizah din saiyakejin kaman ya bisu Dan har zuciyarsa tafara bashi shawarar aje contact din Nan daya riqesa Wanda ya Hana rayuwarsa shaqat bare sukuni.
Tana Isa makaranta a can ya tarar dashi harya rigata Isa da kallon mamaki daga ita har afia suke binsa musamman ganin duk yayi wani iri idanuwansa sunyi laushi kaman ma kwana yayi bai rintsa ba.
Cikeda tausayinsa suke kallonsa duk su dukan hardai ita NURUn da idanuwanta sukai rau rau hawaye na neman cikowa cikinsu sonsa na qara shigarta ta tsaya daf dashi tana kallonsa cikin kulawa me tsanani da taushin murya tace"
Im lafiyanka kuwa?
Kana lafiya?
Bakayi bacci ba ko?
Kasa Bata amsa yayi sai kallonta dayakeyi kaman zai hadiyeta afia na ganin hakan ta wuce tabarsu anan tana yar dariyarsu.
Motarsa suka koma suka jingina anan yafara zayyane Mata shawarar dayakeson yankewa ta ajiye aiki sai bayan aurensu tukuna ta girgiza Masa Kai tana cewa"
Karkayi haka im idan muka saka gaggawa a al'amarin zai iya zuwa da tangarda,
Dan Allah kabi komai a hankali.
Murmushi kawai yayi Yana kallonta Yana cewa"
Idan kuka tafi zanyi missing dinki my love.
I will miss you too im Amma fa ka ajiye maganar aje aikin Nan please.
Gyada Mata Kai yayi kaman qaramin yaro sai hakan yabata dariya ta murmusa tana Dan juyar da kanta gefe daganan ya suka fara fira yanata sake langwabe Mata.
Ranar ko wani karatun kirki batasamu yiba sai yamma dasuka dawo Wanda shine dakansa ya dawo da ita tun a gate yana ajeta ya juya ya wuce.
Batajin yunwa Dan taci abinci a makaranta Dan haka wanka tayi tai salloli tana idarwa tasake hada sauran kayansu na tafiya Dan yau da daddaren zasu bi jirgin Daren zuwa gizah.
Kasa zaune tayi takasa tsaye gabaki daya batajin nutsuwar zuciya data gangar jiki daurewa kawai takeyi Amma wlh tana cikin wani hali na tsoro da shakka na zuwanta can din sbd sanin matsayinta Kuma idan taje can Dole tayi bauta kaman sauran bayi matuqar ba maganar zamtowanta negestati zai fito fili ba kuma idan hakan ta fito fili Dole amiqata ga NEGES dinta Wanda duk wannan cigaban rayuwar data samu zai tashi a banza.
Daga ita har afia qarfin haline kawai sukeyi suna sakewa Kamar suna cikin farin cikin tafiyar Wanda kowaccensu cikin ranta a matuqar tsorace take kaman zuciyoyinsu zasuyi tsalle su fada kowa da bikin zuciyarsa.
Qarfe Tara na dare jirginsu zai tashi Dan haka suna sallame sallar ishai suka fito masu aiki na janye da akwatinansu dasuke kaman set Dan duk iri dayane,
Ita doguwar rigace purple ajikinta sai gyale light purple data daura sai handbag da wayarta da sauran Yan abubuwanta qananu dasuke ciki
Qafartama flats Versace ne black a sanye sai face mask data Sanya Dan kaman iska iska takejin yamata yawa.
Mota daya suka shiga su biyu itada afia farhat Kuma motar daddynta tabi.
Har aka Isa airport Babu me doguwar magana acikinsu sai yaqen Dole dasuke zabgawa.
Kai tsaye angama komai nasu suna zuwa ta baya qofar 'yan first class aka bi dasu suka shige duk da hakan maleek nata inda basa ganinsa Amma shi Yana ganinsu da haka jirginsu ya daga massage din Imran na shigowa ko budewa batayiba tasaka wayar flight mode ta saka cikin jaka.
Doguwar tafiya sukayi me nisa ta tsawon awanni masu Dan yawa kafin suka Isa lokacin har qarfe bakwai yayi na safiya.
Airport din cike yake da wasu irin matakan tsaro na musamman da aka baza koina sbd saukowar MALEEK da familynsa.
Motocin daukarsu guda hudune sukazo daukarsu wainda suke na musamman ne Dan kuwa dama Dan maleek aka siyesu zamansa suke duk lokacinda yazo Kuma duk shekara ake sauya Masa su ko ya zo kobai zoba.
Cikin motocin alfarma aka daukesu daga airport din motocin tsaro suna gabansu da bayansu aka nufi babbar masarautar delah gizah dake daukeda babban tarihin arzikinda ko Ina aka sani musamman sbd qarfi da girman mulkinsu.
Duk yanda ake fadar delah ta gizah NURU hankalinta yayi mummunan tashi sbd yau idanuwanta sun gane Mata Dan kuwa duk yanda take tunanin gizah ta wuce Nan,
Tsorone da kamewa suke shigarta dataga tsagwaron dukiyarda idanuwa basa iya gama kalla Dan kuwa ita ayau taga abinda Bata taba ganiba arayuwarta,
Delah dinsu ta can dasuke ganinta aljannar duniya sbd tarin dukiya da zallar mulki Ashe ba komai bace akan Nan asalin delah gizah.
Matakan tsaro ne tako Ina da askarawa da bayi kowanne akan tsari sbd mulkin na wayayyun Kaine mulkine na masu ilimin turai da addini,
Rayuwar masarautar delah gizah tafi tsauri da matakan mulki da zuba zallar ikon sarauta shiyasa duk inda ta kalla saita sauke Kai taji jikinta yayi sanyi musamman dataga yanda ake bawasu afia girma Kamar za'a musu sujjada sbd girmamawa hakama duk Wanda ka kalla ko a kuskurence Babu Wasa ko Sanya ga dukkanin wani Wanda yake qarqashin masarautar Dan kuwa ko doguwar sakin fuska babu tsakanin jinin sarautar 'yan delah gizah din da bayinsu kokuma masu aikinsu basusan komaiba sai rayuwar mulki da iko cikin wadata da arzikinda basusan Yaya zasuyi dashiba.
Babbar masarautace datayi hudu zuwa biyar din delah ta garinsu wadda wannan komai nata ma basai anfadaba kana shigowa zaka kame kanka da kanka sbd Wasa ko laifi kadan saiyayi sanadinka ashafe labarinka.
Komawa tayi ita abiye kawai take dasu afiyan dandai duk tagama Shan jinin jikinta ta kame kanta farhat ce riqeda hannunta Taki saki sbd ita duk Bata wani Saba da kowaba Anan din sai Anneti AFIA ce kawai tasan kowa ta Saba da kowa harma da rayuwar mulkin itama ta iya tsaf Ashe akwai a jininta Dan kuwa take itama ta rikide Takoma li'iliti AFIA UBAYD MALEEK dinta Wanda yasa NURU sake Kama kanta.
Shi maleek ma sunsan ganinsa ayanzu ko su dasuke 'yayansa abune me tsananin wuya agaresu Dan kuwa ayanzu MALEEK yafi komai tsada da wuyar gani a gizah Dan kuwa tsaron dake hanyar zuwa sashensa ko asalin sashen NEGES (sarki) bai samu tsatsauran tsaro ba Kamar nasa sbd shine asalin MALEEK na kujerar kowa yasan shine sarki kawai dai mulkin baya hannunsane Wanda shine yaso Kuma bai tashi karba bane Dan hakane yasa matuqar MALEEK na gizah to kowane irin tsaro da matakai sun ninku.
Babban sashen dake maqale Dana Anneti mahaifiyar MALEEK anan ne masaukinsu dama Wanda yagama Jin gyaran Jin dadin duniya.
Bayine da masu hidimarsu birjik a qaton babban daki guda dake gefen part din Wanda aka zuba musu gadaje irin na Yan makaranta masu hawa bibbiyu su anan suke rayuwa aikinsu kawai shine duk ranarda iyalin maleek sukazo sune masu hidimarsu.
##MAMUH#
_ZAFAFA BIYAR_💖💖💖
_Alkiblah--SAFIYYAH HUGUMA_
_Makauniyar qaddara--BILLYN ABDULL_
_Dalaal--MISS XOXO_
_Mabudin zuciya--HAFSAT RANO_
_Ubayd Maleek--MAMUH GEE_
_DUKA KUDIN WANNAN DADADAN BOOKS DIN SUNA KAN FARASHIN NERA 700. WATO KUDIN PAGES KENAN. DOCUMENTS IDAN AN KAMMALA SUMA KUDIN SU DABAN.._
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
*_Mamuhgee 19_*
Assalamu alaikum, ina masu son su iya baking da decoration na birthday cake wanda idan aka kalla sai an kara kalla😇
toh ga dama ta samu er uwa kiyi maza kiyi rigista, sannan zaki koyi ydda ake hada whip cream din da yke daukar awanni ba tare da ya narke ba💃🏻
zaki koyi ydda akeyin vanilla cup cake mai dadin gaske😋 er uwa ba'a iya nan muka tsaya ba zamu koya miki ydda akeyin chocolate bar cookie domin farantawa mai gida da baki🥰
kuma duk akan kudi naira 3500 kacal👌🏻
Online class neh full vedios kamar a gabanku akeyi, tare da note da voice note ydda zaku fahimci komai cikin sauki😇
kada kubari wannan dama ta wuceku🤗
Domin neman karin bayani ki kira: 07089621678
I.G handle: Umsad cakes nd more😍
*******************
Zama NURU tayi a makeken royal bed dinda yafi Kama Dana kwanciyar mutum hudu zuwa biyar sbd girmansa ga wani irin ado da komai na dakin yasamu kana shigowa komai na masarautar ma kana gani kasan kana cikin palace.
Sake wani marayan numfashi tayi zazzabin daya kamata Yana sake qarfafa ajikinta Dan kuwa itadai batamasan menene matsayin dazata dauka anan din ba,
Shin me Reno?
Kokuwa baiwa?
Kokuwa negestati?to idan negestatin ne to ta wa?
Dafata AFIA tayi tana zare dankwalin kanta dake nade da dogon gashinta ta zauna tana miqar da hannuwanta a gajiye tace"
NURU Yaya dai?
All okay right???
Dan dagowa tayi jiki ba qwari ta kalli afia din saita sauke kanta tanajin kallon afian ido cikin ido yanzu ba nata bane kila kozasu koma yanda suke sai sun koma gida.
Cikin sanyin harshe tace"
Headache ke damuna Amma inaga na gajiyane zai saki idan na huta.
Cikin kulawa afia tace"
Sorry.
Gyada Kai kawai tayi tana sake dauke kallonta daga kan afia din.
Wanka sukai sauya cikin wasu irin dogayen rigunan alfarma wainda aikene na musamman daga sashen Anneti.
Babban makeken palon suka fito har zuwa dining Wanda yake shaqe taf da kalolin abinci da abin Sha tareda snacks da fruits kowanne sai daukan ido yake yanda aka jeresu kaman mutum goma ne zasuci abincin.
Zama suka farhat na gefen NURU sbd wata irin maqalewa data sameta tun zuwansu sbd farhat din nata rashin son shiga mutane masu yawa irin hakan shiyasa ma ko acan dad dinsu ya Hana bayi ko masu aiki da yawa sbd ko bayan farhat shima bayason guri da mutane da yawa komai girman gurin kuwa.
Cikin nustuwa da kwanciyar hankali sukaci abinci suka koshi suka koma Palo suka zauna aka aika da asanarwa da Anneti zasu zo gurinta kawo gaisuwa Nan da mintuna kadan.
Tunda saqon gasunan zuwa sashenta ya iso Mata farin cikinta ya Dada bayyanuwa sbd a duniya idan abinda tafi so da qauna shine MALEEK dinta da 'yayansa duk da kullum adduarta Allah yaqarowa UBAYD 'yaya masu albarka sbd tanason ganin zuriar UBAYD MALEEK ta yadadu Amma ga dukkan alamu kila hakan bamai yiyuwa bane sbd matarsa kowa ya lura Kuma ya fahimci batason yawan haihuwa.....Dan faduwa gabanta yayi da tunanin wani zancen binciken NEGES yabayar daya fada Mata yana ganin kaman UBAYD MALEEK Bata tareda matarsa.
Saurin rufe fararen idanuwanta da maleek duk su ya sauko tayi cikin wani irin hali na damuwa me tsanani tace"
Ya Allah ya kabar da wannan zancen akan MALEEK dinta Dan kuwa har abada ko amafarki Bata fatan ace hakan yazama gaskia Dan kuwa sbd wannan zancen da NEGES ya fada matane ciwon zuciyarta ya tashi Wanda tasa aka bugawa MALEEK Dan kawai yazo ta tabbatarda abinda hankalinta ya dagu da jinsa.
Saida afia ta tabbatarda zuwa yanzu saqon zuwansu ya isa gurin Anneti kafin suka dungumo zuwa gurin nata.
Tun a hanya NURU ke sake shiga taitayinta tana sake Kama kanta farhat dai na maqale da ita bayi uku na bayansu.
Fadar tsari da kyawun sashen mahaifiyar MALEEK bamai faduwa bane saidai kawai ace Masha Allah da wannan daula.
A babban palonta na kurya suka taddata suna shiga da sallama dauke a bakunansu Banda farhat data saki hannun NURU tayi gurin Anneti da gudu ta fada jikinta cikin tsananin farin ciki.
Farin cikin ganinsu ya Hana Anneti rufe Baki ta budewa afia hannuwanta ta qaraso da sauri ta rumgumeta tana cewa"
Kemiri nafik'akelewi ya Anneti (I miss you so very much Anneti/nayi kewarki sosai Anneti)
Murmushin farin ciki Anneti tasaki itama cikin yare da muryarta me tsananin taushi da dattako tace"
Masha Allah li'iliti takusa zama Mata agurin me gagaruman sa'a
Ya Allah ya albarki rayuwanku ku duka.
Amin sukace dukkaninsu har NURU dake tsaye Dana farko ta kasa qarasowa.
Idanuwa ta zubawa NURU dake tsaye tana kallonsu cikin burgewa suna hada ido tayi saurin sauke kanta tareda zubewa qasa ta durqusa tana cewa"
Barka da hutawa Anneti.
Har lokacin kallonta Anneti keyi sbd kyawun NURU da yanayin kyan fatarta dake haskota yasa take Mata kallon 'yar sarautar delah ce ta bude Baki cikin kulawa ta amsa mata tana maido kallonta kan Afia tace"
Wannan wacece??
Cikin sauri farhat tace"
Aunt NURU ce ta Dade agidanmu taredamu she's family.
Da mamaki tasake kallon NURU tana kallon afia data share zancen Dan batason fadar matsayin NURU na 'yar Taya zama da aka kawo musu ita wadda su tuni suka dauketa 'yar uwa ta jini wadda takewa kallon wani bangare na rayuwarta Dan kuwa qaunace me qarfi a tsakaninsu.
Jawo wani zance afia tayi ta hanyar cewa Nuru ta qaraso ta zauna acikinsu.
A Dan kakkame ta qaraso Amma Bata zaunaba saita zauna a qasa Yana cewa hakanma she's ok.
Ganin NURU da farhat yasa Anneti bataiwa afia maganar mahaifiyarsuba Wanda afia ta lura da hakan hankalinta yatashi sosai matuqa musamman batason ayi tambayar gaban farhat Dan zata fada cewar mum dinsu ta Dade da tafiya tabarsu.
Basu bar sashenba sai dare suna zuwa wanka sukai suka kwanta Banda NURU data fara waya da Imran.
Kasa bacci afia tayi tana saqa da warwara,
Babban abin tsoronta anan shine Dole ita Anneti zata tambaya mum dinsu Dan kuwa MALEEK ko sunyi mgnar da Anneti bazai taba fada Mata komai akaiba ita Kuma duk qaryar dazatayi na kawo wani excuse dazatace ya Hana mum zuwa bazai shigaba Dan kuwa Anneti zata gane komai Daren dadewa Dan haka take buqatan lokaci Wanda zatai amfani dashi ta shirya iyayenta kafin agano.
Da wannan tunanin tayi bacci takuma farka,
Washe gari ma agurin Anneti suka wuni saidai Banda NURU wadda ta Kama kanta ta zauna guri daya sbd yawo ba nata bane acikin masarautar gizah ta yayan masu masarautar ne
Sai washe gari dazasu yawon ziyara cikin masarautar zuwa sashe sashe na 'yayaye da sarauniyoyin gizah shine tabisu saidai tayi danasanin Binsu Dan kuwa sake tabbatarda rashin darajarta tayi shiyasa Bata Kuma gigin binsu ba idan zasu fita acikin gizah din ta Kama kanta ta zauna guri daya sai tunanin gida da iyayenta yadawo Mata Kamar sabo.
Duk yanda Afia ke zamewa Anneti sbd kada tasamu damar yimata maganar mahaifiyarsu yau da kanta taje gurinta Dan tabbatarwa da kaman jita jitan da kaman yakeson fita na rabuwar iyayenta din sbd shekaran jiya da jiya duk sashen dasukaje sai anyi tambayar matar maleek guda ace bataxo duba Anneti ba wane irin uzurine wannan.
Hakan yasa hankalinta tashi matuqa sbd tabbas Kam kowa zaiyi nasa tunanin daban daban ace Annetin delah gizah mahaifiyar MALEEK guda ace matarsa batazo dubata ba tabbas zance yafara bayyana take ta aika sako na musamman ga mahaifinta na cewa akwai karatu me mahimmanci a makaranta sunada buqatan komawa Kuma tana roqonsa daya koma taredasu sbd shine jigonsu bazaso komawaba bataredashiba.
Hakan datayi saiya sake saka Anneti cikin shakka da mamaki sbd sakon MALEEK saiya biyota gurinta yake Isa gurin maleek Dan haka ta aika aje akawo Mata farhat batareda sanin afia din ba.
Agurinta ranar farhat ta kwana da daddare bayan sunyi Shirin kwanciya ta kalli farhat din tana shafa Mata Kai cikin kulawa tace"
Farhat mamanki meyasa bata biyoku ba bayan ga abal dinku dayafita ayyuka yazo dubani??.
Kai tsaye farhat tace"
Mum ta Dade da tafiyanta munata kuka nida afia
Daddy ma da kansa yace idan ta tafi kada tasake dawowa yabata da ita koyaushe.
Wani mummunan bugawa zuciyar Anneti tayi har Saida ta dafe Dan kuwa kiris ne yahana ciwon zuciyarta tashi duk da hakan wani radadin tashin hankali takeji,
Idan dagaske MALEEK yarabu da lailah zancen yafito Babu ta yanda zai karbi mulkinsa Dan kuwa kaf a tarihinsu sarakuna basa sakin matansu wannan wace irin masifa ce.
Cikin tashin hankali tasake sanyaya harshenta tace"
Tun yaushe ne ta tafi?
Tun kafin aunt NURU tazo ne ta tafiyan munata kuka hadda Afia Amma tunda aunt NURU tazo daga delah jekadi takawo Mana ita shikenan muka daina kuka sbd Aunt NURU tana Sona sosai tunda tazo AFIA tadaina damuwa suka zama Best friends tanamun pancakes da komai nakeso Kuma daddy ma tana Masa abinci fa yafi nasu mum Sarah Dadi aunt NURU tafi mum sbd ita Bata barina Ina kuka Kuma tace bazata tafi tabarniba kaman yanda mum tayi idan sunyi aure da uncle Imran ma Dani zata tafi.
Wuta Anneti ta dauke gabaki daya
Numfashinta yafara yankewa tana dannewa,zufa kuwa kaman tana cikin dakin gashin biredi.
Daqyar ta iya daidaita numfashinta ta kalli farhat tana nazartan zantuttukanta daya bayan daya tana fahimtarsu tana kawowa inda farhat tace jekadi takawo musu NURU daga delah sai kawai ta tsaya anan ta shafa kan farhat din tareda kwantar da ita tana Mata addua har tayi bacci.
Palon hutawarta ta Isa ta zauna tareda daukar wayarta ta Nemo numbern jekadi ta Danna Mata Kira.
Cikin girmamawa me girma jekadi ta dauki wayar tareda zubewa qasa tana jerowa Anneti gaisuwa cikin tsananin girma.
Shiru Anneti tayi na mintuna biyu kafin tace"
Jekadi bayanin komai nakeso na NURU yarinyar dake zaune agidan MALEEK.
Tsit jekadi tayi tana juya zancen zufa na karyo Mata cikin tsananin ladabi da girmamawa tayi kasa da Kai kaman agaban Anneti din tace"
Allah ya taimaki Anneti kimun afuwa nafara tambayo izinin fadar wannan magana agurin KALEEB.
KALEEB?" Anneti ta fada ahankali cikin mamaki duk da tasan dama Dole Saida sanin Kaleeb jekadi ke komai.
Katse wayar tayi ta Nemo numbern kaleeb da kanta takirasa.
Kira uku tayi se Ana hudu ya daga cikin muryar girma da mulki take itama tayi qasa da murya tahau gaisuwa cikin tsananin girmamawa tana sake tambayarsa manyanci.
Shiru tayi bayan gaisuwar tarasa ta inda zata faro har Saida yayi gyaran murya a kame yace"
Kiyi maganarki kada ki damu kaleeb zai duba koma menene.
Cikin sanyin murya tace"
Allah ya taimaki kaleeb idan banyi shishigiba inason sanin wacece yarinyar da jekadi takai gidan MALEEK.
Murmushin manya yayi Kai tsaye yace"
Negestatinsa ce sbd ya rabu da matarsa.
Hawaye ne suka ciko Mata ido tace"
Allah ya taimaki kaleeb nagode Allah yaqara girma ina fatan ban dameka ba da Kiran dare danayi.
Bakomai Anneti Allah ya taimakemu duka.
Maganar rabuwar MALEEK da matarsa kuwa kinsan meya dace kiyi qato shiru sbd fitar hakan barazanace ga maleek.
Inshallah kaleeb ngd ahuta lafiya.
Kasa daurewa tayi Saida wasu irin hawaye me zafi suka gangaro Mata sbd wannan masiface agurinta babba.
Ta Yaya zata Hana fitar maganar rabuwar MALEEK da matarsa.
Jekadi takira anan jekadi ta fayyace Mata komai na yanda rabuwar take Wanda yasa ran Anneti baci sai yanzu ne tagano dalilin qin barin ayi maganar da afia keyi sbd Kare mahaifiyarta kada mutuncinta ya zube.
Ko so daya adaren Anneti Bata rintsaba Dan kuwa ki NEGES bazata Bari yaji zancenba tunda zargi kawai yake zata barshi yayita zargin kawai batareda ya tabbatarba.
Washe gari tun qarfe Tara ta aika cewa tana gayyatar su AFIA cin abincin safe a sashenta tareda ita.
Da farko AFIA taji wani Abu na kwanan da farhat tayi acan gurin Anneti Amma da bataji bayani ko ganin sauyi afuskan Anneti ba saita sake abinta Dan ma kada asamu damar yin maganar saita saka NURU shiryawa Dole suka taho tare.
Tunda suka zauna cin abinci Anneti tayiwa NURU kallon sakanni ta dauke kanta ta maida kan Afia dake cin abinci ba damuwar komai aranta.
Suna gamawa NURU ta fice daga sashen gaba daya sbd kallon da Anneti ke Mata yasa hankalinta tashi matuqa tashiga wani irin matsanancin tsoro.
Kai tsaye Anneti ta kalli afia bayan fitar NURUn tace"
Maleek da lailah sun rabu gaskia ne kokuwa???
Wani irin mummunan tarine ya kufcewa afia ta dago da jajayen idanuwanta ta kalli Annetin cikin tsananin firgici da tashin hankali tace"
Aa Basu rabu ba sunanan tare.
Meya hanata zuwa ita?
Sake dagowa tayi dukkanin idanuwanta na qarasa sauyawa cikin dakewa da qarfin hali tace"
Ayyukane sukai Mata yawa tayi tafiya.
Murmushin takaici na manya Anneti ta sake tana kallon zallar kuruciyar afia da yarintarta tace"
Idan har hakane kuna buqatar uwar dazata kula daku da mahaifinku sbd....
Cikin tsananin tashin hankali da firgici afia ta miqe tsaye jikinta har 'yar rawa yakeyi ta zube gaban Anneti cikin rawar murya da Bata girmanta na uwar MALEEK tace"
Anneti Ina roqanki da kadaki kawo Mana kowa bama buqatar wata uwa sbd munada me kula damu wadda take tamkar uwa.
Kallon tsaf Anneti ta Mata saidai tasan zallar kuruciya kecin afia Amma tace"
Wacece ita?
NURU tafada Kai tsaye.
NURU ba mata bace Matar uba ake magana wadda zata zauna daku har abada.
Rintse ido tayi sbd fadar abinda zata cutatar da NURU saidai Dole zatai hakan Dan kawai abar zancen su samu su taciyarsu batareda wani maganar aure aure ba wa dad dinsu.
Bude idanuwanta dasukai jajir tayi ta sauke Kai muryarta na rawa tace"
NURU da dad zasuyi aure idan munkoma.......
Wani razanannan kallo Anneti tai Mata cikin tsananin mamakin mahaikaciyar kuruciya irin tata,
Wace irin zuciyane da afia dazata yiwa mahaifinta qarya Dan Kare mahaifiyarta?.
Ji tayi zuciyarta ta sosu da abinda afian tayi saidai ta danne bacin ranta sbd gudun shedan yashigo cikin lamarin sbd afia ta dauko wata mummunar sabia me qarfi qararda zance irin wanan akan MALEEK guda idan har Bata dauka matsayinsa na mahaifi agaretaba.
Tabbas yau zata nunawa afia yaro man kaza ne,
Ta dauko magana me girma Dan Kare darajar wadda batasan daraja ba Dan haka yau zatasan ba'a Wasa da magana irin wannan.
Kitashi kije zancenki ya karbu.
Ajiyar zuciya boyayya afia ta sauke duk ganin takashe maganar qara auren mahaifinta duk da zuciyarta bata daina bugawaba kamar zata faso ta miqe ta fice tana istigfarin na neman yafiyar ubangiji.
Bayan fitarta waya Anneti ta daga ta Danna Kiran jekadi Kai tsaye cikeda bada umarnin me qarfi tace"
A isarwa kaleeb saqo daga Anneti cewan muna roqon alfarmar auren NURU daga negestati zuwa Mata ga MALEEK na Delah gizah UBAYD MALEEK.
Da qarfi jekadi ta zube qasa tana yiwa Anneti wani irin kirarin tsananin farin ciki da girmamawa.
##MAMUH#