*Bismillahir Rahmanirrahim*.
Ina mik'a godiya ga dukkanin masoyana. Wannan littafin k'irk'irarre ne, banyishi dan cin zarafin wani ba, ina fatan Allah yasa kowa ya amfana da abinda yake ciki amin.
*LAGOS*
Cike babbar kotun garin Lagos take da jama'a, wasu basu da alak'a da wannan shari'ar, amma yanda ake fad'in yanayin shari'ar da kuma wanda aka maida shari'ar wajensa yasa kowa yake so yaje domin yaji yanda zata kasance.
Kasancewar lauyen da aka maida shari'ar wajensa sabon zuwa ne hakan yasa kowa yake son ya ganshi, domin an sanar cewa wannan zaman shine zama na k'arshe, saboda tsohon lauya ya kasa kawo kwararan shedu hakan yasa shari'ar ta gamsu da shedun abokin karawarsa.
Tsaye mutane suke a bakin kotun suna jiran abasu izinin shiga kafin Alkali ya iso. Wasu Matasa ne da suke gefe guda suke magana akan wannan shari'ar. 'Daya daga cikinsu yake fad'in abokina ko kasan nima ban gamsu cewar gaskiya ce wannan lauyen yake fad'a ba, taya za'ace bayan mutum ya mutu da wata biyar sannan ace matarsa tana da ciki har na wata ukku, kai da gaji ma kasan rainin hankali ne har sai sunzo wata kotu.
'Dayen yace kuma wannan shari'ar kotun musulunci yakamata ace an kaita ba wannan kotun ba, gashinan yau zuwa na ukku ne amma an kasa tsaida mafita, da kotun musulunci ce tuni an wuce wajen amma hada wani sake lauya, ai zaizo muji tashi basirar.
Murmushi wanda yake gefensu yayi yana fad'in wallahi kuna bani dariya, kunsan fa ance shari'a sab'anin hankali, abinda wani yayi ya kasa sai kuga wani yayi, koshi Alkalin sai ya kasa gano abinda wani lauyen zai gano, duk da ance sabon lauya ne babu wanda yasan basirar da Allah ya bashi, kuma ba jiya bane ya amshi shari'ar kusan sati guda kenan rabon mu da nan, kunga kuwa acikin sati d'aya zai iya had'a shedu masu kyau idan yana da basira, koda kotun musulunci aka kai wannan shari'ar ai dole sai da shedu, dan haka muyi masu fatan alkhairi shine zaifi, danni wallahi tausayin matar nakeyi, itace k'arama acikin matan Alhajin, kuma itace ta ukku fa, kasan unguwar mu d'aya dasu babu abinda ban sani ba akan irin zaman da sukeyi da abokan zamanta, kasan halin mata, akan kishi babu abinda bazasu iya ba, kuma nasan halin matar, duk da basu dad'e da Alhaji ba amma mutane suna fad'ar kyan halinta, shiyasa jikina be yarda da wancan lauyen ba, domin ina yawan ganinshi a unguwar mu yazo wajen sauran matan.
Jinjina kai sauran sukayi suna fad'in to Allah ya bayyana gaskiya. Yace amin. Tashi sukayi ganin an fara shiga ciki.
Kowa ya sami waje ya zauna ana jiran shigowar Alkali. Wani Matashin yaro ne wanda bazai wuce shekara 32 zuwa da 33 ba yashigo kotun yana sanye da kayan aikinshi, idanuwansa suna b'oye cikin farin gilashi hannunsa d'auke da k'aramar jaka.
Yanayin takunsa yaja hankulan mutanan da suke zaune a kotun, koda ganinshi kowa ya gane shine sabon lauyen da ake magana akanshi. Wasu da yawa suna mamakin ganinshi a haka, sun d'auka zasu ga wani babban mutum sai gashi sunga Matashi mai jini ajika.
Yana k'arasowa wajen da aka tanadar masu domin zama ya fara mik'a hannu ga sauran 'yan uwansa lauyoyi suna gaisawa. Ko da yazo kan mutum na k'arshe bayan ya bashi hannu sai yaji bai sakeshi ba, d'ago kai yayi yana kallonshi. Babban mutum ne, yasan ya girme mashi a shekaru. Kallon hannunshi ya sakeyi ganin har lokacin bai sakeshi ba kuma murmushi bai b'ace daga fuskar mutumin ba.
Murmushi shima ya sakar mashi yana kauda kai. Sunana *Brr. Nuhu Bajinta*, amma amfi kirana da *Brr. Bajinta*, nine wanda yake jagorantar wannan shari'a, wato abokin karawar ka. Murmushi yayi yana fad'in sunana *Brr. RA'EEZ HAMZA MWD*, nine sabon lauyen daya amshi wannan shari'a.
Jinjina kai Brr. Bajinta yayi yana fad'in muna maka maraba da shigowa wannan babbar kotu mai albarka, Allah ya baka sa'a a wannan aikin namu mai had'ari da wahala. Brr. Ra'eez yace amin nagode.
Zama sukayi suna jiran k'arasowar Alkali. Wanda yake kusa da Brr. Ra'eez ya sake bashi hannu yana fad'in sunana *Brr. JABEER USMAN*, ina aiki a wannan kotun kusan shekara d'aya da farawata kenan, ina maka fatan alkhairi da zuwa wannan kotu. Murmushi Brr. Ra'eez yayi yana fad'in nagode Jabeer Allah ya bamu zaman lafiya. Yace amin.
Shigowar Alkali yasa kowa ya tashi. Bayan ya zauna kowa ya zauna tare da natsuwa. Bayan da Alkali ya gama 'yan rubuce-rubucensa sannan ya bada izinin acigaba da gabatar da shari'ar.
Tashi magatakarda yayi yana fad'in, a yau sha hud'u ga watan oktoba shekara ta 2019, wannan kotu zata cigaba da sauraron k'arar da akeyi akan iyalan gidan Alhaji Bala wanda matanshi guda biyu suke k'arar amaryarsa Amina akan fitowar ciki a jikinta bayan mutuwar mijinsu wanda suka tabbatar ba nashi bane, wannan shari'ar da ake gabatarwa ta tashi daga hannun lauyen da yake kare wacce ake k'ara ta koma wajen sabon lauya mai suna Brr. Ra'eez Mai Wada wanda aka yimasa canjin aiki zuwa wannan kotu.
Risnawa yayi yana mik'ama Alkali takarda. Bayan daya gama dubawa yace ina sabon lauya kotu tana so ka gabatar da kanka.
Fitowa yayi yana fad'in sunana Brr. Ra'eez Hamza MWD, kuma nine lauyen daya amshi wannan shari'a a wajen abokin aikina. Jinjina kai Alkali yayi yana fad'in lauyen da zai fara bismillah.
Komawa Brr. Ra'eez yayi ya zauna dan beyi niyar farawa ba, yafiso ya zauna yaga kamun Brr.. Bajinta. Fitowa Brr. Bajinta yayi yana fad'in ya mai shari'a, har yanzu Amina bata amsa laifin da ake zarginta ba, haka kuma taki furta sunan wanda yayi mata wannan cikin, duk da matanshi sun tabbatar da Alhaji bai tab'a haihuwa ba a duk zaman da suke dashi, kuma sun dad'e atare dashi bai haihu ba, dalilin rashin haihuwar ne yasa ya k'aro aure, har sukayi zaman kusan shekara Amina bata tab'a b'atan wata ba sai gashi bayan mutuwar Alhaji ciki ya bayyana a jikinta har na wata ukku wanda likita ya tabbatar Alhaji baya haihuwa, kuma kowa ya sheda bayan mutuwar Alhaji sannan cikin ya bayyana wanda Alhaji ya riga cikin barin duniya kafin ya bayyana.
Takowa yayi wajen da Amina take tsaye yana fad'in Malama Amina ya kamata zuwa yanzu ki bud'e baki ki fad'a mana gaskiyar wannan al'amari, be kamata kicigaba da wahalar da kotu ba, agabanki aka gabatar da manyan hujjoji, kowa ya aminta da hujjojin yakamata kema ki bayyana wanda yayi wannan cikin domin ki sauk'ak'a ma kotu wahala.
Tashi Brr. Ra'eez yayi yana fad'in ya mai shari'a, bai kamata lauya yarik'a takura wadda ake zargi ba, Amina tana da ikon ta fad'i gaskiya akan abinda ta sani, bai zaima dole dan kowa ya amince da abinda wani ya fad'a ba ace itama dole ta amince. Nagode ya mai shari'a.
Kallon Brr. Barjinta Alkali yayi yana fad'in ka gyara kalamanka. Risnawa yayi yana fad'in za'a kiyaye ya mai shari'a. Iya kar abinda zan fad'a kenan, ina rokon wannan kotu data yanke wannan hukunci domin magada su san halin da suke ciki. Nagode ya mai shari'a.
Tashi Brr. Ra'eez yayi yana fad'in ya mai shari'a inaso nayima Alhaji Kabir babban aminin marigayi wasu tambayoyi. Da sauri Brr. Bajinta ya kalli Brr. Ra'eez jin wata magana da yazo da ita, shi tunda aka fara shari'a beyi tunanin sako aminin Marigayi ba domin yasan beda wani amfani a shari'ar, sai gashi Ra'eez ya gayyatosa a cikin shari'ar.
Alhaji Kabir ya fito gaban kotu.
Brr. Ra'eez... Kotu zata so tasan alak'ar ka da Marigayi.
Alh. Kabir... E to, kowa dai yasan Alhaji bai da amini daya wuce ni, atare muka taso, abotar mu ta wuce abota ta koma ta 'yan uwantaka, sirrina na Alhaji ne, haka shima nashi nawa ne, babu abinda muke b'oyema juna.
Brr. Ra'eez.... A tsawon zamanka dashi ko ya tab'a fad'a maka yana da matsalar rashin haihuwa?
Brr. Bajinta... Ina da ja ya mai shari'a, be kamata Brr. Ra'eez ya maido mana da hannun agogo baya ba, kowa yasan munyi nisa a wannan shari'ar, dan yazo daga baya bai kamata ya maido da komai farko ba.
Alkali... K'orafi bai karb'u ba, Brr. Ra'eez yana da ikon sako wannan shari'a daga farko matuk'ar yana da tabbacin ya kawo hujjojin da zasu gamsar da kotu.
Brr. Ra'eez.. Murmushi yayi yana fad'in nagode ya mai shari'a. Ina jinka Alhaji.
Alh. Kabir... Gaskiya tunda muke da Alhaji be tab'a fad'a mani yana da matsalar rashin haihuwa ba, asali ma duk lokacin da zaije wajen duba lafiyarsa tare muke zuwa, duk lokacin daya tashi zuwa asibiti baya yarda ya tafi da direba, ko bana gari yana hak'ura har na dawo domin muje tare, abu d'aya na sani shine yana fama da damuwa akan rashin haihuwa da Allah be basa ba, wannan dalilin ne yasa shi aure har mata ukku, domin munsha zuwa wajen likitoci daban -daban suna tabbatar mana lafiyarsa kalau kawai lokaci ne beyi ba, wannan dalilin ne yasa na bashi shawarar ya k'ara aure kila adace, sai gashi har Allah yayi masa rasuwa bai samu haihuwa ba, a daren ranar da zai rasu bana gari ina hanyar dawowa ya kirani, tabbas alokacin muryarsa cike take da farin ciki, duk da yana cikin hali na rashin lafiya hakan bai hana farin cikinsa bayyana ba, bayan mungaisa nake tambayarsa dalilin farin cikinsa, jin hayaniya ya gane ina tafiya hakan yasa ya kashe wayar yana fad'in idan na sauka zamuyi waya, bamuyi wayar ba har Allah ya d'auki ransa.
Brr. Ra'eez... Jinjina kai yayi yana fad'in mungode zaka iya tafiya. Juyowa yayi yana fad'in ina so nayima Hajiya Binta uwar gida ga marigayi tambaya. Hajiya Binta ta fito gaban kotu.
Brr. Ra'eez.... Hajiya ko kin tab'a zuwa asibiti aka gwadaki domin a tabbatar da lafiyar ki?
Hajiya Binta... Kwarai kuwa, ni da Alhaji munsha zuwa asibitin nan garin har ma da k'asar waje, duk inda mukaje amsar d'aya ce, matsalar tana wajen Alhaji, sun tabbatar mana bazai tab'a haihuwa ba, alokacin yaso mu rabu amma nace masa ban yarda ba, aurena dashi na saurayi da budurwa ne, ban damu da haihuwa ba matuk'ar muna tare dashi, alokacin na fad'a masa kada ya yarda da maganar likitoci domin ba maganar Allah bace, nice nayi ta bashi kwarin guiwa akan yayi aure kila adace, nayi mamaki da Alhaji Kabir yace wai sunje asibiti ance lafiyarsa kalau, kuma so da yawa Alhaji yana zuwa asibiti shida direba, dan haka maganar Alhaji Kabir ba gaskiya bace.
Brr. Ra'eez. Mungode zaki iya tafiya. Ina so nayima likitan daya tabbatar da awon cikin Amina tambayoyi. Likita ya fito gaban kotu.
Brr. Ra'eez.... Kai ne likitan Alhaji ko?
Likita... E nine.
Brr. Ra'eez.. Amatsayin ka na likitanshi ya akayi baka tab'a fad'a mashi bazai iya haihuwa ba tun yana da ranshi sai bayan mutuwarsa ne kayi rubutu sannan ka kawo kotu? Sannan ya akayi alokacin da ka auna Amina iya cikin kawai ka gani baka gano komai ba?
Likita... Hannu yasa yana goge zufar data zubo mashi kafin ya furta, iya abinda aka umarceni na auna kenan a kotu, kuma dana auna na kawo sakamakon a kotu. Maganar Alhaji kuma kasan ana son a b'oye sharri a bayyana alkhairi, Alhaji ya manyanta, bazaiji dad'i yaji cewar bazai tab'a haihuwa ba, yana matuk'ar son haihuwa har hakan ya jawo yayi aure har so ukku, ganin haka yasa na kasa fad'a mashi gaskiya har sai da buk'atar hakan ta taso a kotu.
Brr. Ra'eez... Amma gashi Babban aminin Alhaji ya tabbatar da sunje asibiti an tabbatar da lafiyarsa kalau.
Likita... E to, ai kasan ko wane likita da yanayin aikinsa, kowa yasan yanda muka dad'e da Alhaji, kuma Alhaji ya yarda da aikina, to bazanyi mamaki ba dan wani likitan yace lafiyar Alhaji kalau ba, domin koni abinda na fad'a masa kenan, kasan mu likitoci masu ceto ne, muna iya b'oye gaskiya domin farin cikin marar lafiyar mu, wannan dalilin ne yasa na b'oye masa gaskiya.
Brr. Ra'eez... Mungode likita zaka iya tafiya. Ya mai shari'a zan so nayima *IYA* mai aikin gidan Alhaji wasu tambayoyi.
A firgice Hajiya Binta ta mik'e tana fad'in ya mai shari'a Iya ta dad'e da barin gidan mu, tun kafin ya rasu muka nemeta muka rasa acikin gidan wai bazata iya cigaba da aiki agidan ba, yau kusan wata bakwai kenan da barin ta gidan.
Bubbuga tebur Alkali yayi yana fad'in ki kama bakin ki nan kotu ce ba kasuwa ba, dan haka kada ki sake magana idan ba kiranki akayi ba. Zama Hajiya Binta tayi tana goge zufa, kallon kishiryata Zainab kawai take, ita kuma ta kasa fahimtar halin da Hajiyar tashiga dan ankira Iya bayan tasan babu abinda ta sani Iyar tayi.
Brr. Ra'eez.... Iya ko zaki fad'ama kotu tsawon shekarun da kikayi agidan marigayi kina aiki?
Iya.... Gaskiya na dad'e ina aiki agidan Alhaji, tun bayan da Hajiya Binta ta cika shekara d'aya agidanshi tasa k'awarta ta samo mata mai aiki amma tafison Babbar mace, kuma bata son 'yar birni ta fison wacce za'a nemo a kauye, hakan yasa k'awarta taje har k'auyen mu da yake katsina wato 'Danja ta samo ni, tun daga lokacin na fara aiki agidan, sosai Hajiya take mani kirki, na d'auketa 'yar uwa, duk da na girmeta amma haka nake bauta mata, itama kuma tana bani hakki na sosai.
Brr. Ra'eez... Amma ya akayi aka wayi gari ba'a sameki agidan ba?
Iya.... Hannu tasa tana goge hawayen da suka zubo mata, kafin tace tabbas na cutar da Amina da Alhaji, nayi kuka wanda beda amfani, naso na nemi yafiyar Alhaji amma Allah be bani iko ba, abu d'aya nasan nayi mashi wanda idan na tunashi nake jin sauki. Kamar yanda na fad'a maka aiki nake ma Hajiya Binta, bayan shekara ukku sai Alhaji ya sake aure, sosai hankalin Hajiya Binta ya tashi, domin likita ya tabbatar mata bazata iya haihuwa ba, alokacin atare mukaje da ita, domin Hajiya ta aminta dani, lokacin da ta fad'a mani abinda likita ya fad'a sai tace na rufe maganar bata so kowa yaji. Bayan da aka kawo amarya Hajiya Zainab sai tazo ba kamar yanda mukayi zato ba, ta kasance mace mai kwantar da kai awajen Hajiya Binta, ganin haka sai Hajiya Binta taji dad'i. K'awarta ce ta kawo shawarar kada ta bari Zainab ta haihu agidan, hakan yasa mukaje wajen wani k'asurgumin Boka ya bada maganin hana d'aukar ciki.
Bayan da muka dawo na rik'a zubama Zainab magani a abinci tana ci, kuma Allah ya taimaka bata d'auki cikin ba. Bayan shekara biyu da aurenta Alhaji ya sake aure inda ya auri Amina, itama mace ce mai hakuri da kwantar da kai, hakan yasa Hajiya Binta taji dad'in zuwanta, anan itama mukayi kokarin bata magani a cikin abinci.
Jin shiru bata d'auki ciki ba yasa hankalin mu ya kwanta, sai dai abinda bamu sani ba ashe ciki ya shiga jikin Amina, nice na fara sanin tana da ciki, a hankali da wayau da dabara irin tamu ta manya na tambayeta rabon data ga al'adarta, a yanda tayi mani bayani yasa na gano cikin watanshi d'aya da kwanaki, anan nayi mata dabara nace kada ta fad'ama Alhaji zaiga rashin kunyarta, ta bari na fad'ama Hajiya Binta ita zata masa albishir hakan zaisa yafi ganin darajarta.
A ranar muka koma wajen Boka, anan ya bamu maganin da za'a rufe mata baki bazata fad'ama kowa tana da ciki ba, zata manta da wani ciki ma ajikinta, sannan Boka ya bamu maganin zubar da cikin, sai Hajiya tace tana tsoron yaki fita, gara dai a kwantar dashi zata san abinyi. Anan Boka yayi mana aiki muka dawo gida.
Tun daga ranar maganar cikin Amina tasha ruwa, bata sake maganar ba, har gwada ta nayi amma ta nuna ita bata san da maganar ba bata da wani ciki. Muna cikin haka Hajiya Binta ta samo maganin da zai kwantar da Alhaji ta bani na zuba mashi a abinci, tunda yaci bai sake lafiya ba.
Wata rana na dawo daga cikin gari kai tsaye na wuce d'akin Hajiya Binta, abinda naji ya firgitani, magana suke da k'awarta akan ta kashe ni, domin ita bata yarda da kowa ba, tunda ina da son kud'i wata rana zan iya juya mata baya idan na samu wasu kud'in. Nan take ta amince akan washe gari zata kashe ni, sannan Alhaji yana mutuwa zata koma wajen Boka ya tashi cikin domin ta jama Amina sharri kuma aki amincewa da cikin jikinta, ita kuma Zainab zata nuna mata soyayya domin ta bata dama su kwarema Amina baya, idan komai ya kammala itama tasa akasheta sai taci dukiyar ita kad'ai.
Cike da firgici Hajiya Binta ta mike tana fad'in wallahi k'arya take, Zainab kada ki yarda da abinda tace makirar tsohuwa ce. Bubbuga tebur Alkali ya buga hakan yasa ta natsu. Kallon tuhum kawai Zainab take binta dashi.
Brr. Ra'eez... Iya cigaba da bayaninki muna sauraron ki.
Iya... Aranar hankalina ya tashi, cikin sand'a na shige d'akina na had'a kayana na bar gidan, ko mai gadi be ganni ba dan yashiga sallah, kafin na bar garin sai da na samu wani yaro da nake mutunci dashi na sashi ya rubuta mani wasik'a, anan na sheda ma Alhaji Amina tana da ciki, alokacin zai kai wata biyu, ban iya fad'ama Yaron komai ba dan bana son ya gano ni, kawai nace masa ina jin kunyar Alhaji nafiso ya karanta a rubuce.
Bayan ya gama nace ya taimaka muje ya bama maigadi kuma ya tabbatar mashi Alhaji zai bamawa. Ina tsaye har Yaron ya bama Mai gadi takardar, bayan ya dawo ya fad'a mani Mai gadin yace zai bama Alhaji duk da baya fitowa amma zaiyi kok'arin kai mashi.
Godiya nayi mashi na bashi kud'i na bar garin, a ranar cikin dare na isa Funtua, a tasha na kwana sai washe gari na isa kauyen mu, ban sake sanin abinda yake faruwa ba sai lokacin da kaje gidana, nayi mamakin ganinka da bayanin da kazo mani dashi, nayi kukan mutuwar Alhaji domin hada ni aka kashe shi, naso na nemi yafiyarsa babu dama saboda banyi ilimin boko ba dana rubuta mashi a wannan wasikar, zuwanka yasa naji kwarin guiwa kuma na amince zanzo na bada sheda akan abinda na sani domin duniyar ta juya mani baya.
Brr. Ra'eez... Zaki iya tafiya mungode. Ya mai shari'a iya kar mutanan da zanyi ma tambaya kenan, wannan takarda ce dana samu a d'akin marigayi alokacin da mukaje gidan bincike nida 'Dan sandan da yayi mani jagora.
Takarda ce mai d'auke da rubutun Marigayi tare da sa hannunshi, tun daga ranar daya samu labarin cikin Amina ya rubuta kwanan watan, ya nuna farin cikinsa, har yayi fatan Allah ya tashi kafad'arsa domin yaga jininshi, atare da takardar da Iya ta aika masa ya had'esu ya b'oye a cikin dirowarsa, Allah ne ya bani ikon ganinta, domin gaba d'aya takardun dirowar an kwashe su, itama daga k'asan dirowar akwai wajen da yake b'oye abubuwan sirrinsa anan ya aje ta.
Mik'ama Magatakarda yayi yana fad'in ya mai shari'a, iya abinda zan fad'a kenan, ina rokon wannan kotu mai alfarma data yanke hukunci ga mutanan da suka zalunci Amina da Marigayi, sannan ta hukunta Likita daya goyi bayan k'arya. Nagode ya Mai shari'a.
Gaba d'aya kotun ta d'auki hayaniya, mutane da yawa Brr. Ra'eez ya burge su, acikin sati d'aya ya gano gaskiya, abinda akayi wata anayi sai gashi acikin sati guda ya gama komai.
Bayan da kowa ya natsu Alkali ya d'ago yana fad'in kotu tana son ganin Hajiya Binta, Iya da Likita agabanta. Haka suka fito jiki a sanyaye, Hajiya Binta sai kuka take dan tasan ta k'are mata.
Kallon Hajiya Binta Alkali yayi yana fad'in kinji shedun da aka kabartar ma kotu, ko kina da ja akan abinda aka fad'a? Girgiza kai tayi tana goge hawaye tace na amince da abinda aka fad'a, amma wallahi sharrin shed'an ne, son zuciya da neman duniya yasa na aikata abinda ban tab'a yi ba, ina rokon wannan kotu da ta mani sassauci.
Alkali yace Likita kana da ja akan abinda aka fad'a? Girgiza kai yayi yana goge zufa yana fad'in na amince, amma wallahi Hajiya Binta ce ta bani mak'udan kud'i akan nayi rubutu akan k'arya kuma nazo na bada sheda, dan Allah arufa mani asiri.
Alkali yace kotu wajen adalci ne, duk wanda kaga yazo kotu to yazo ne domin abi masa hakkinsa, babu batun wani rufin asiri a kotu domin wajen tonon asiri ne, dan haka kowa ya tsaya yaji hukuncinsa.
Hajiya Binta.... Kinfi kowa laifi anan, dan haka kotu ta yanke maki hukuncin d'aurin rai da rai agidan yari, sannan zaki biya Amina tarar dubu d'ari biyar abisa kok'arin ki na b'ata mata suna da kikayi.
Iya.... Kema kotu ta yanke maki d'aurin rai da rai agidan yari, amma kin samu sassaucin aikin wahala abisa kokarin da kikayi na warware gaskiya da kikayi.
Likita..... Kaci amanar aikin ka, an had'a baki da kai anyi rashin gaskiya, dan haka kotu ta yanke maka d'aurin wata biyar agidan yari, kuma zaka biya Amina tarar dubu d'ari biyu abisa b'ata mata suna da kayi.
Wannan kotu tana yima Brr. Ra'eez jinjina akan namijin kok'arin da yayi wajen gano gaskiya, da fatan kowa zai d'auki darasi akan wad'annan mutanan, sannan kotu ta wanke Amina daga zargin da ake mata, ciki na mijinta ne, kuma dole yaci gadon mahaifinsa.... Kotttttt!!!!
Gaba d'aya mutanan mik'ewa sukayi suna ma Alkali tafi, sosai mutane suke son Alkalin su, domin suna ganin shi d'in adali ne, yana kokarin zartar da hukunci akan duk wanda aka kama da laifi.
Hannu Brr. Bajinta ya mik'a ma Brr. Ra'eez yana fad'in ina taya ka murna akan wannan nasara da kayi, ba'a tab'a samun wanda ya kada ni a shari'a ba, sai gashi sabon zuwa yayi mani warwas, duk da ba yaune ka fara aiki ba, anyi maka canjin wajen aiki ne amma duk da haka kayi kok'ari, sai mun had'e wani lokacin.
Murmushi Brr. Ra'eez yayi yana fad'in nagode.
Har kusa da Brr. Ra'eez dangin Amina suka zo suna masa godiya. Brr. Ra'eez yace haba ai bakomai ku godema Allah. Sallama yayi masu suka fita shida Jabeer.
Bayan sunyi sallama da Jabeer ya zo shiga mota yaji ana masa magana, yana juyowa yaga *ALKALI NE,* murmushi yayi yana masa sannu. Alkali yace kaine da sannu, gobe idan kashigo ina son ganinka a ofis. Jinjina kai yayi yana fad'in to yallab'ai. Sallama yayi mashi ya tafi.
Da kallo Alkali ya bishi yana sakin murmushi, a zuciyarsa yana nanata sunanshi (Brr. Ra'eez Hamza MWD), kamar ya san mai shigen sunansa sheru da yawa, sai dai kuma wancan ba haka sunansa yake ba, to me MWD take nufi kuma? Kafad'a ya d'aga yayi gaba.
**** ****
Kai tsaye babbar gidan yari ya nufa, bayan sun gama gaisawa da masu gadin yashiga ciki ya zauna yana jiran akira masa wanda yazo wajensa.
Wani babban mutum ne ya fito yana sanye da kayan gidan yari ajikinsa, da ganinsa daga aiki yake. Yana zuwa Brr. Ra'eez ya mik'e ya bashi wajen zama.
Bayan sun gaisa Brr. Ra'eez yace *KAWU* nayi nasara, yanzu aka gama yanke hukunci anjima za'a kawo masu laifin nan. Murmushi wanda aka kira da Kawu yayi yana fad'in nasan zakayi nasara Ra'eez, an haifeka ne domin Nasara, yanzu kam hankalina ya kwanta, nasan k'arfin ka ya kawo, zaka iya gogawa da kowa, nayi farin ciki da aka maidoka wannan kotu da aiki, nasan aikin *Alhaji Mansur* ne, yana matuk'ar kok'ari akan ka, yarik'e amana, shima Allah bazai barshi ahaka ba.
Brr. Ra'eez yace ai Kawu ban tab'a kukan rashin Mahaifina ba, Abba Mansur ya gama mani komai arayuwa, fatana Allah ya bani ikon saka masa. Kawu yace Allah yasa, kai dai kacigaba da hak'uri arayuwa zaka cigaba da samun nasara, kaje wajen Umman ka kuwa? Brr. Ra'eez yace yanzu dai zan biya.
Kawu yace ka dubata da jiki, sannan ka kiyaye da wannan Alk'alin, zuwa gaba zaka gane nufina, nasan Alhaji Mansur ya fad'a maka wasu abubuwa amma dole kasan komai domin ka shirya yakin kwato 'yanci tare da d'aukar fansar Mahaifinka, kada ka sake ka fad'ama kowa abinda MWD yake nufi har sai burinka ya cika, shiyasa naji dad'i da akafi sanin mahaifinka da sunansa na biyu. Ra'eez yace insha Allahu zan kiyaye. Tashi yayi ya mik'a masa kud'i yana fad'in sai na sake dawowa. Kawu yace Allah yayi maka albarka.
***
*PSYCHIATRIC HOSPITAL* (ASIBITIN MAHAUKATA)
Zaune Brr. Ra'eez yake akusa da wata babbar mace, duk wanda ya ganta yasan tana cikin yanayi na hauka, zaune take tana kallon 'Danta wanda ya bud'e ledar da yazo da ita wadda take d'auke da kayan motsa baki.
Lemu ya d'auko yana kok'arin bud'e mata, da sauri ta warce tana kok'arin fasa kwalin. Murmushi yayi ya mik'a hannu yana fad'in Ummu na bani na bud'e maki kinji. Kallonshi tayi kafin ta mik'a masa kwalin.
Bud'e mata yayi ya zuba mata akofi ya bata. Amsa tayi ta shanye tana mik'a hannu. Aiba ya b'are mata ya bata. Rabi taci kafin ta mik'a masa rabin abaki, amsa yayi ya gutsura hawaye suna zubo mashi.
Hannu tasa ta goge masa hawayen tana fad'in Likita yace adena kuka, yace Alhaji zai dawo, ba dai sun kashe shi ba? Idan na fito zamuje mu kashe su dukan su, ai dai zaka siyo mani wuk'ar Makka ko? Kasan ita kad'ai ce zata iya kashe su.
Murmushi yayi yana fad'in Ummu bazan kyale jinin Abbu ya tafi abanza ba, zanyi kwakkwaran bincike, akwai rud'u acikin wannan lamarin, dole sai nasa natsuwa kafin na gano su, bazaki dawwama ahaka ba, Allah zai baki lafiya.
Dariya tasa ta kamo hannunshi tana fad'in nima binshi zanyi, kai kad'ai zamu bari ai, sai kaje makka kasiyo wuk'a ka kashe su. Wani likita ne ya k'ara so. Bayan sun gaisa Brr. Ra'eez yace nagode likita, kana kok'ari akan Ummu na. Likita yace haba bakomai, tana samun kulawa sosai, yanzu ma lokacin shan maganinta ne, kasan tana sha take bacci. Jinjina kai Brr. Ra'eez yayi yana fad'in nima tafiya zanyi, nagode sosai likita. Hannu ya bashi yana fad'in Allah ya baka lada Brr. Ra'eez, hakika da wuya asamu irin ka da yawa aduniya, kana kok'ari akan Mahaifiyarka. Hawaye Brr. Ra'eez ya goge yana fad'in dole nayi Likita, duk wanda yasan darajar *UWA* zaiyi fiye da abinda nakeyi, Uwa ba abun wasa bace.
Likita yace haka ne gaskiya, Allah yayi mana jagora. Brr. Ra'eez yace amin. Sallama sukayi ya wuce yana kallon Ummunsa.
Kai tsaye gidanshi yawuce da yake unguwar ( *APAPA*). Kwance yayi a falo hawayen da suka zamar masa jiki suna kwaranyo masa, gaba d'aya baya jin dad'in ranshi, duk lokacin da ya kai ziyara wajen Ummunsa haka yake kasancewa, kuma duk da haka baya iya faashi wajen zuwa ganinta, can ne kad'ai yake zuwa yaji dad'i aranshi. Runtse ido yayi yana fad'in Allah gani gare ka, Allah kayi mani jagora akan wannan al'amari, bani da gata sai kai ya Allah, kashige mani gaba wajen gano gaskiyar wannan al'amari, Allah ka tona asirin wad'an da suka aikata ma Mahaifina wannan abun, Allah ka tona asirinsu ta yanda bazasu iya k'aryatawa ba. Juyi yayi yana sakin kuka marar sauti.
*GA DUK WANDA YAKE SON CIGABAN WANNAN LABARI ZAI TURO NAIRA 200 KACAL, MTN CARD TA WANNAN LAMBAR.. 08147669770, SAI KAYI SCREEN SHOT KA TURA TA WHATSAPP A LAMBAR K'ASA, IDAN KUMA BANK TRANSFER NE, KA TUNTUBE NI TA WHATSAPP NO 08028525263 ZA'A SAKA GROUP DIN DA ZA'A RIKA POSTING. NAGODE. SAI KUYI HAKURI DA YANDA LITTAFIN YAZO.*
Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[3/10, 8:38 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kud'i ne. naira 200 kacal, MTN card ta wannan lambar.. 08147669770, kayi screen shoot ka tura ta whatsapp a lambar k'asa, idan kuma bank transfer zakayi sai ka tuntube ni a whatsapp ta wannan lambar. 08028525263*
0⃣2⃣
Da kyar ya tashi yayi wanka, bayan yayi sallah ya fita zuwa gidan Kawu dan can ne waje na biyu da yake d'ebe masa kewa, duk da Kawu ya so ya koma can da zama amma yaki komawa, acewarsa yafi son kad'aici.
Da sallama yashiga cikin gidan, a tsakar gida ya iske matar gidan tana kok'arin kauda kayan da suke a tsakar gidan. Amsa sallamarsa tayi tana fad'in Ra'eez sannu da zuwa.
Zama yayi yana fad'in yauwa sannu da aiki Mama, ina *RUMAISA* kike aiki ke kad'ai? Murmushi Mama tayi tana fad'in na aiketa siyen kayan miya ne shiyasa nake rage aikin kafin ta dawo.
Jinjina kai yayi yana fad'in Kawu yana gaishe ku. Mama tace ka je kenan? Ra'eez yace naje na sanar dashi yanda shari'ar tamu ta kasance ne. Mama tace ikon Allah, ashe fa yau ka fara shiga babbar kotu ko? Ina fatan dai komai yayi dai-dai? Ra'eez yace Alhamdulillahi Allah ya amsa addu'ata, komai ya tafi yanda ya kamata, domin nine nayi nasara.
Mama tace kai amma naji dad'i, Ubangiji Allah ya baka ikon yin nasara akan shari'ar da zaka fara nan gaba domin kwato hakkin mu da aka danne.
Ra'eez yace amin Mama. Hannu tasa ta goge kwallar data zubo mata tana fad'in ina Kawun naka babu dai abinda yake damunsa ko? Ra'eez yace lafiyarsa lau yace agaishe ku ma.
Mama tace amma yana cikin wahala ko? Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in Mama ki daina damuwa, sam basa sashi aikin wahala domin akwai mutane na acikinsu, muna mutunci sosai hakan yasa suke sauk'ak'a masa, addu'a itace abinda zamuyi masa.
Mama tace haka ne, shiyasa fa bana son zuwa wajensa, duk lokacin da naje ina dad'ewa kafin na warware, ya jikin Ummun ka? Duk'ar da kai Ra'eez yayi yana fad'in kamar kullum Mama.
Girgiza kai tayi tana fad'in Allah ya bi mana hakkin mu, an zalince mu an tauye mana hakkin mu, Allah ne kad'ai zai iya saka mana, Allah ya baka ikon jure wannan jarabawa Ra'eez, hakika an zalince ka, an rabaka da Mahaifinka, ga halin da Mahaifiyarka take ciki, Allah ya baka ikon gano gaskiya kuma ya baka sa'a akan kosu waye suka aikata hakan, babu abinda zamuce da kai sai godiya, Allah ya saka maka da alkhairin abinda kake mana, karike mu amana tamkar jininka.
Ra'eez yace amin Mama, amma bana so kina mani wata godiya, kun wuce duk yanda kuke tunani a waje na, bani da kowa a garin Lagos sai ku, duk da bamu had'a komai da ku ba amma Allah ya had'a mu, ku da Abba Mansur kun zame mani 'Yan uwa na jini, ku kad'ai nake kallo naji dad'i arayuwata, ta silar Mahaifina Kawu yashiga halin da yake ciki, tunda babu Abbu dole na maye gurbinsa awajen ku, domin nasan da yana raye shi mai rik'e ragamar gidan ku ne, dan haka kada ki sake mani godiya, ke Uwace agare ni.
Jinjina kai Mama tayi tana goge hawayen idonta tace haka ne Ra'eez, hakika kai 'Dah nagari ne, ko wace Uwa zatayi alfahari da samun ka, kada ka sake cewa ta silar Mahaifinka Malan yashiga wannan halin, dama can Allah ya rubuto masa K'addararsa a haka, fatan mu Allah ya bashi ikon cinye wannan jarabawar. Ra'eez yace amin.
Sallamar Rumaisa ce ta katse su, amsawa sukayi. Da sauri ta k'araso tana fad'in Yayana sannu da zuwa. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in Rumaisa ya gidan? Tace lafiya lau, an gama shari'a lafiya? Ra'eez yace lafiya lau nayi nasara.
Tashi tayi tana murmushi tace naji dad'i Allah ya k'ara d'oraka akan makiya. Ra'eez yace amin 'Yar K'anwata. Mama tace an samo komai ko? Rumaisa tace an samo.
Tashi Mama tayi tana fad'in bara na tayaki naga lokaci ya kure. Da sauri Ra'eez yace aa Mama kinyi aikin ki, yanzu mune zamu shiga ofis. Dariya sukasa, Mama tace ai shikenan ayi aiki lafiya bara naje na gyara cikin kafin Abdallah ya dawo makaranta.
Ra'eez yace ina ruwan Autan Mama, ina fatan dai yana karatun sosai? Rumaisa tace ai Abdallah ba wasa, dana fad'a masa zaka zo sai kaga ya dage. Ra'eez yace saura ke, tunda kin gama makaranta.
Turo baki Rumaisa tayi tana fad'in Yaya kaima dai ka san ra'ayina ai. Harara ya wurga mata yana fad'in wannan tsohuwar magana ce, dan haka dole kiyi karatu.
Duk'awa tayi tana hawaye tace dan Allah Yaya bana son karatu. Murmushi yayi yana fad'in Rumaisa kina nan da ra'ayinki, da ace baki da kok'ari da bazan takura maki ba, kada ki manta kece zakara a makarantar ku fa, tun kafin kishiga makaranta fa kike da kok'ari, meyasa baza kiyi amfani da iliminki ba? Kece babba agidan nan, kina ganin halin da Mahaifinki yake ciki, ga Abdallah k'aninki yana makaranta, baki so yayi koyi da ke? Idan yaga baki karatu shima sai abun ya fice masa arai ai.
Hawaye ne suka zubo ma Rumaisa. Ra'eez yace ba kuka nasa kimun ba, gaskiya nake fad'a maki, a zamanin nan kowa yana son auren mace mai ilimi, ko ba dan kanki ba zaki taimaki yaranki, Rumaisa duk kok'arin ki matuk'ar baki wuce karatu ba wata rana zaki nemi ma'anar kalma d'aya ki rasa, domin shi ilimi sai ana tilawarsa yake zama, duk da kinayin islamiya amma zakisha wahala matukar bakiyi karatun boko ba, bance dole kiyi aiki ba, amma idan kikayi karatun wata rana kwalin zaiyi maki amfani, kin ganni nan bazan iya auren macen da iyakarta sakandire ba.
Da sauri Rumaisa ta d'ago tana kallonshi. Jinjina kai yayi yana fad'in da gaske nake, nafison na auri mai ilimi kodan saboda yaran mu, idan kuma auren kike so badamuwa ki fito da wanda kike so ni zan maki aure.
Mama ce ta fito tana fad'in gara dai kayi mata fad'a, kullum maganar da nake mata kenan amma ta toshe kunnanta, tunda Rumaisa ta taso take fad'in baza tayi karatu ba bayan ta gama sakandire, ada na d'auka yarinta ce ashe har zuciyarta abun yake, ko auren da kake magana ai bata kula kowa, na rasa inda tasa gaba.
Ra'eez yace barni da ita Mama, kada ki sake mata maganar karatu, nima bazan sake mata ba, kuma dole tayi aure. Murmushi Mama tayi ta shige tana fad'in aiko zan fara shirin biki.
Da sauri Rumaisa ta tashi tana dire-dire ta nufi kicin tana gungunai. Dariya Ra'eez yasa yana rufe baki. Tashi yayi yana fad'in bani alaiyahun na yanka maki. Baki ta murgud'a tana fad'in bana so. Dariyar da yake b'oyewa ce ta kwace masa, sosai yake dariya. Kayan miyar ta d'auka ta cigaba da aikinta tayi banza dashi.
Tashi yayi yana fad'in bara na d'auko maki tsarabar ki amota na manta. Bata kulashi ba yayi waje. Bayanshi tabi da kallo hawaye suna zubo mata, dole ma ta amince tayi karatu matuk'ar tana son Yayanta, da sauri ta d'auko wayarta ta rubuta mashi ya samo mata makarantar aikin lafiya ta unguwar zoma (Mid-Wife) zatayi karatun.
Tun a zaure Ra'eez yake dariya, sai da yasha dariyarsa kafin yashigo ciki, dama yasan idan ba haka yayi mata ba baza tayi karatun ba, yana matuk'ar son Rumaisa amma yafi so ya auri mai ilimi, kamar tasan yana son mace tayi aikin asibiti ta zab'i haka. Ciki yashiga ya fara taya ta aiki be nuna mata yaga sakon ta ba.
**** ****
Kwankwasa k'ofar ofis d'in Alkali yayi kusan sau biyu kafin daga ciki aka bashi izinin shiga. Tare da Brr. Bajinta ya iske Alkali. Murmushi Alkali yayi yana fad'in kaga d'an halak d'in ma, yanzu muke maganar ka ashe kana hanya.
Hannu Ra'eez ya mika masu suka gaisa cike da girmamawa. Kujera Brr. Bajinta ya nuna mashi yana fad'in bismillah. Zama yayi Alkali yace ba dai yanzu kashigo ba? Ra'eez yace tun d'azu nazo nasan baka shigo ba shiyasa na zauna a ofis.
Alkali yace ya gajiyar aikin jiya kuma? Ra'eez yace Alhamdulillahi. Brr. Bajinta yace ai jiya Brr. Ra'eez ya caza mana kwakwalwa, na rasa yanda akayi ya iya had'a wannan aikin acikin sati d'aya.
Alkali yace shiyasa nace ya sameni domin naji yanda akayi yayi wannan kok'arin, gaskiya ban tab'a samun mutum irinka mai hazaka ba, shiyasa tun ajiyan nayi masa jinjina. Brr. Ra'eez ko zaka fad'a mana yanda akayi kayi wannan aikin haka? Kada ka damu nasan ba hurumi na bane nayi maka wannan tambayar, kawai dai naga kok'arin ka ne shiyasa zan so naji daga gareka.
Murmushi Ra'eez yayi ya kauda kai bece komai ba. Tashi Brr. Bajinta yayi yana fad'in Yallab'ai zanje ana jira na a ofis. Alkali yace to badamuwa nagode.
Bayan ya fita Ra'eez ya d'ago kai, dama saboda Brr. Bajinta yaki yin magana, taya Alkali zai tambayeshi agaban abokin aikinsa bayan yasan tare suka kara.
Alkali yace yi hak'uri nayi maka tambayar da bata dace ba. Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in haba ba komai. Alkali yace kawai ina so naji yanda akayi ka iya gano gaskiya ne dan gaskiya ka burgeni, zan so ka saki jiki dani, ka d'auke ni tamkar d'an uwanka dan gaskiya ka burge ni, da alama ba'a garin nan kake ba ko? Kai Ra'eez ya girgiza yana fad'in a garin nan nake, sai dai ba anan nayi karatu ba shiyasa, nayi aiki a babbar kotu da take kano na kusa shekara d'aya kafin na nemi canjin wajen aiki aka maido ni nan.
Alkali yace zuwanka alkhairi ne a kotu ta, domin ina da buk'atar mutane irin ku, domin tunda na saurari bayaninka na gano kana da gaskiya, dan haka kacigaba da rik'e gaskiya dan ita ce cikar darajar mutum.
Ra'eez yace nagode da wannan karamcin daga gare ka, kuma insha Allahu ba zaka sameni da rashin gaskiya ba. Hakika lokacin da nazo wannan kotun na kawo takardar canjin aikin da akayi mani aranar na iske wannan shari'ar, zaman da nayi ina jiranka alokacin na tsinci kad'an daga cikin shari'ar, alokacin Lauyen da yake kare Amina naji yana fad'in bazai iya cigaba da shari'ar ba, domin yayi iya bincikensa ya kasa gano komai, gashi Brr. Bajinta ya fishi sanin makamar aiki bazai iya gogawa dashi ba, yaso ya taimaka ma Amina amma dole ya hakura har ya fad'a mata ta samu wani lauyen kafin lokaci ya kure mata.
Bayan dana gama jin firarsu bayan da kazo nashiga muka gama komai kasa a nuna mani ofis d'in mu shine naje nayi masa sallama na gabatar masa da kaina na nuna masa naji firarshi ko zai iya bani dama na amshi shari'ar da yakeyi? A lokacin da nayi masa magana sosai farin ciki ya bayyana a fuskarshi, babu b'ata lokaci yashiga warware mani komai akan shari'ar.
Aranar bayan na koma gida banyi bacci ba, yanda ya bani labarin na zauna na fitar da komai, washe gari na nufi gidan marigayi nida lauyen, bayan munje muka samu Amina ya fad'a mata nine zan karb'esa.
Sosai tayi farin ciki anan tashiga bani labarin gaskiyar abinda ta sani, bayan nayi mata tambayoyi anan na gano mai aikinsu bata gidan da dad'ewa, shine nace mata ina so ta fad'a mani inda zan samu Iya, shine ta fad'a mani 'yar asalin 'Danja ce, sai dai bata san gidanta ba, amma ta tab'a fad'a mata gidanta yana bayan kasuwa wata rana da suke fira.
Bayan na gama jin labarin Iya sai na nemi da ta fad'a mani aminin Alhaji data sani, shine ta fad'a mani sunan Alhaji Kabeer, nan nace mata zan tafi tunda babu lokaci, ina so naje can garin su Iya. Haka mukayi sallama da ita muka tafi.
A ranar nabi jirgi zuwa kano, washe gari na nufi funtua sai da na huta daga can naje garin su Iya, cikin ikon Allah bansha wata wahala ba na gano gidanta, alokacin da naje mata da bayanin daga Lagos nake nasan tayi aiki agidan Alhaji k'ark'ashin Hajiya Binta.
Fad'ar sunan Hajiya Binta yasa Iya ta fara kuka tana fad'in ba laifinta bane, tun anan na gano akwai wata ak'asa, hakan yasa na lallab'ata nace ta bani labarin abinda ta sani domin Alhajin ya rasu.
Haka ta warware mani komai tana kuka, na tausaya mata domin naga nadama a idanuwanta, nan na roketa akan ta biyoni idan har ta yarda tayi nadama kuma tana so ayi mata hukunci a duniya.
Babu b'ata lokaci ta amince, domin ta fad'a mani gara a yanke mata hukunci akan rayuwar da takeyi agarinsu, duniyar tayi mata zafi koda banje ba ta yanke shawarar barin garin ta koma wani gari ko zata samu sauki. Naji dad'in maganarta, aranar muka nufi Funtua da ita, dole ta mota muka dawo saboda naga zamu b'ata lokaci.
Bayan da muka dawo naje na samu 'Dan sanda yayi mani jagora zuwa gidan Alhaji domin a bayanin Iya ta fad'a mani ta aika masa da takarda, bayan munje na tambayi Amina ko an samu wata takarda a d'akin Alhajin wadda aka fad'a masa tana da ciki? Sai tace gaskiya bata sani ba, ganin haka yasa muka nemi izinin Hajiya Binta muka shiga d'akin, cikin sa'a na samu wannan takardar dana gabatar.
Haka muka tafi na nuna masu ban samu komai ba. Bayan nan naje na samu Alhaji Kabeer, shima mun dad'e muna tattaunawa dashi kafin muka rabu, ana saura kwana d'aya a koma kotu na kammala had'a shedu na, cikin ikon Allah nazo na gabatar dasu kuma nayi nasara. Kaji yanda akayi na gano komai cikin lokaci.
Jinjina kai Alkali yayi yana fad'in gaskiya Brr. Ra'eez kai na daban ne, basirar ka daga Allah take, kayi aiki da ilimi, sai kwararren lauye ne zai iya abinda kayi, sai gashi baka dad'e da aikin ba amma ka tafiyar da wannan shari'ar mai rikitarwa, gaskiya dole na yaba maka, kayi abinda ya kamata, kuma daga yau ka zama babban lauya a wajena, insha Allahu zan rik'a aiki da kai, domin ra'ayin mu iri d'aya ne, ina son mutum mai son zakulo gaskiya a duk inda take.
Murmushi Ra'eez yayi yana fad'in nagode Yallab'ai. Alkali yace karik'a kirana da Abba kamar yanda Yarana suke kirana zanfi jin dad'in hakan domin nasan zakayi sa'an 'Dana na biyu, duk da banyi aure da wuri ba da nasan sai dai kazo ana ukku ma.
Ra'eez yace to Abba nagode. Alkali yace a ina kake da zama ne? Yace a Apapa nake. Alkali yace kayi aure ne ko kana zaune da Iyayen ka? Murmushi yayi yana fad'in banyi aure ba ni kad'ai nake zaune. Alkali yace Allah sarki, Iyayenka ba anan suke ba ne? Baki Ra'eez ya bud'e zai bashi labarinsa sai kuma ya tuna da maganar Kawu ( *Ra'eez ka koyi b'oye sirrin ka, a ciki hada labarin zuri'ar ka, kasan dai yanda kake kok'arin gano wad'an da suka aikata ma Iyayenka wannan abun, kuma nasan dole asan Mahaifinka agarin nan tunda babban mutum ne, kuma ana da tabbacin akwai sa hannun manyan mutane a kisanshi, a ciki hada lauyen da nake zargi domin Mahaifinka ne ya hanasu sakewa hakan yasa suke kokarin ganin bayansa, bani da sheda a hannu amma ina zarginsu domin sune abokan fad'an mahaifinka, dole ka b'oye labarinka har sai komai ya kammala domin gujema matsala, bana son kowa yasan ko kai waye, dan haka bana son ka fad'ama kowa labarin ka.*)
Gyara zama yayi yana fad'in Iyaye na suna Gombe ni kad'ai ne anan. Alkali yace Allah sarki, lallai kayi nisa da gida, bakomai ka d'auke ni tamkar Mahaifinka, idan ka tashi kajira ni sai muje na gabatar da kai a wajen Iyalina domin karik'a zuwa kuna gaisawa, ina zaune a *SURELERE*.
Ra'eez yace bakomai zan jira ka. Alkali yace nagode zaka iya tafiya. Wayar Alkali ce tayi k'ara, sallama Ra'eez yayi masa ya fita. Bayan ya d'auka suka gaisa, alamu sun nuna abokinsa ne ya kira. Shiru yayi yana jin bayanin da yake masa. Kai ya jinjina yana fad'in haba *Alhaji Marusa* wannan ai ba abun tada hankali bane, shikenan na gane bayanin ka, insha Allahu bamu da sauran matsala, na kammala shari'ar da nake fad'a maka kuma an gano gaskiya, sabon lauya ne ma ya gano komai, ai ina fad'a maka yanzu ya bar ofis d'ina, gaskiya yaron yana da hazak'a, dan haka abinda ya kamata zan rik'a bashi, sauran kuma sai aba Brr. Bajinta saboda kasan shine namu bazamuyi saurin nuna fuskar mu a wajen sabon zuwa ba. To shikenan sai kazo. Wayar ya aje yana murmushi.
Tunda Ra'eez ya shiga ofis ya gama duba takardun da suke akan teburinsa ya janwo hoton da sukayi shida Iyayenshi, alokacin bai wuce shekara takwas ba, yana tsakiyarsu suna dariya aka d'auki hoton. Koda yaushe yana tare da wannan hoto dan shine yake d'ebe masa kewar Mahaifinsa.
Zaroshi yayi daga cikin jakar da yake ajeshi (wallet) aranshi yana fad'in dole ya maidashi gida ko dan gudun b'acin rana, tunda Kawu yace ya kikaye barin duk wata alama da zata nuna koshi waye har sai ranar da burinshi ya cika.
A hankali yasa hannu cikin dabara ya goge hawayen da suka kusa gangaro masa ta gefen gilashinsa, tashi yayi yasa hoton a aljihu ya d'auki mukullin mota domin yaje ya aje hoton agida dan hankalinsa yaki kwanciya akan ya kara ko mintuna biyu a wajenshi, hakan yasa ya fita domin yaje gida ya adana hoton.
A waje suka had'u da Brr. Bajinta ya rako wasu manyan mutane, da ganinsu ba sai an fad'a maka naira ta zauna masu ba, har sun gaji da kud'i a yanayin jikinsu, motar da suke tsaye ajiki kad'ai abun kallo ce bare kuma suturar da take jikinsu. Yanda yaga Brr. Bajinta yana wani risna masu ya k'ara tabbatar masa da su d'in wasu ne.
Kai tsaye wajen daya aje motarsa ya nufa ba tare daya sake kallon su ba, maganar Kawu ce take masa yawo akan tsohon ma'aikacin wannan kotu mai suna *Brr. Barau*, akoda yaushe yafi tsayama masu hannu da shuni akan talakawa, hakan ya nuna masa yana danne gaskiya akan k'arya, tunda ya kasance shine ya tsaya har aka yanke ma Kawu hukunci amatsayin ya kare hakkin Mahaifinsa wannan ya nuna akwai wata ak'asa, duk da hakkin mahaifinsa ya kare amma kuma ai ba Kawu bane ya aikata laifin meyasa ya tsaya har sai da yaga an yanke masa hukunci? Gaskiya dole ya fara bincikensa akan Brr. Barau, to wai ma yana ina? Yasan dai zuwa yanzu kila ya aje aiki ko kuma ya zama shugaba, gashi kuma Kawu bai fad'a masa komai akansa ba, ko hotonsa bai sani ba bare idan ya ganshi ya ganeshi, amma zai tambayi Kawu inda yake.
Haka ya isa gida da wannan tunanin. Bayan ya adana hoton ya zauna yana tunanin hanyar da zai fara bibiyar Brr. Barau domin ya gano hakikanin gaskiya, dole ta kanshi ne zai fara aiki hakan zaisa ya gano komai, domin lokacin da aka kashe mahaifinsa bai bari kowa ya kai k'ara kotu ba yayi saurin amsar shari'ar Mahaifinsa yayi tsaye har sai da yaga an gama komai cikin k'ank'anin lokaci.
Saurin tashi yayi ya d'auko wani k'aramin littafinsa, sunan Brr. Barau ya fara rubutawa aciki kafin ya b'oye littafin ya kwanta yana kallon sama. Dole ya gano masu hannu akisan Mahaifinsa kodan ya sama ma Mahaifiyarsa lafiya domin ta silar mutuwarsa ta samu kanta acikin wannan hali. Ta ina ya kamata ya fara kenan? Dole yaje wajen aikin Mahaifinsa yasan zai samu wani abu, sannan lokaci yayi da Kawu zai bashi labarin Mahaifinsa, saboda Abba Mansur ya fad'a masa Kawu ne kawai zai iya bashi labarin komai. A zabure ya tashi ya d'auki mukullin motarsa ya nufi gidan Yari, bazai iya jira a k'ara kwana ba tare da yasan labarin Iyayensa ba.
Yaci sa'a alokacin da yaje suna hutawa, hakan yasa akayi kiran Kawu suka samu waje suka zauna. Kawu ya kalleshi cike da mamaki yana fad'in Ra'eez lafiya? Wannan zuwan fa? Kuka Ra'eez yasa yana fad'in daga wajen Alkali nake, yace mani yana son yarika aiki dani, gashi na gama duba sunayen ma'aikatan wajen banga sunan Brr. Barau ba, dan Allah Kawu ka bani labarin komai.
Murmushi Kawu yayi yana fad'in wannan Alkalin ai shine Brr. Barau, na fad'a maka ne saboda kasan ta yanda zaka cigaba da tarayya dashi, kuma tunda yanzu ka kawo girma dole na baka labarin komai saboda ka fara shiryama doguwar shari'a, yanzu zakaji komai......
*ASALIN LABARIN*
Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:38 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kudi ne, naira 200 kacal, MTN card ta wannan lambar.. 08147669770, kayi screen shoot ka turo a whatsapp ta lambar k'asa, idan kuma bank transfer zakayi ka tuntub'e ni a whatsapp ta wannan lambar 08028525263*
0⃣3⃣
*ALHAJI HAMZA MAI WADA* shine cikekken sunansa, asalinsa d'an *MAIDUGURI* ne, aiki ne ya fito dashi daga garinsu, ma'aikacin *KWASTAM* ne, yayi aiki a garuruwa da yawa, tun yana a k'aramin matsayi har Allah ya d'agashi, mutum ne mai gaskiya da amana, kowa yasan yanda halin masu irin aikinsu yake a wannan zamani, duk wanda aka ce maka yana aikin Kwastam da wuya ka sameshi mai gaskiya, zaka sameshi mai dukiyar gaske musamman idan akace ya kai babban matsayi, kafin ka samu mutane masu irin wannan aikin da gaskiya a wannan zamani zaka sha wahala, akwaisu sai dai basu da yawa.
Alhaji Mai Wada ya kasance acikin mutane masu riko da gaskiya da amana, wanda hakan ya jawo masa bakin jini a wajen manyansa da kuma manya a najeriya, yayin da ya jawo masa farin jini a wajen masu k'aramin k'arfi musamman masu shigo da kayansu ta hanya mai kyau.
Saboda halinsa yasa ake yawan canza masa wajen aiki, wannan dalilin ne yasa yayi zama garuruwa da yawa, hakan ne ya jawo masa rashin yin aure da wuri, domin yana ganin akwai zalinci yayi aure ya bar matar ya tafi wajen aikinsa.
Sai da 'yan uwansa suka matsa masa kafin ya amince su zab'a masa wata daga cikin danginsa dan baya son yaje wani waje ya samo mata. Kasancewar zuri'arsu akwai had'in kai, dan zaune suke a waje d'aya, katafaren gida ne mai b'angarori da yawa hakan yasa duk 'yan uwan suke zaune awaje d'aya, dama basu da wani yawa a zuri'arsu.
Cikin lokaci k'ank'ani aka sama masa mata mai suna *BILKISU*, mace ce mai hakuri da juriya, masaniya ce a karatun addini, iya karta diploma a fannin girke-girke, lokacin da aka mata maganar anyi mata miji babu b'ata lokaci ta amince dan dama yana burgeta.
Bayan anyi bikinsu da wata d'aya aka sake masa canjin wajen aiki zuwa Kano. Haka ya tafi ya kwashi kusan wata biyu kafin ya dawo, da zai koma Mahaifinsa yace daga yanzu duk inda aka maidashi ya d'auki matarsa su tafi, be amince masa yarik'a barinta ba, da ace tare suka tafi kila da yanzu ta samu rabonta, amma ya tafi har wata ukku taya zai tara zuri'a a haka.
Haka ya d'auki matarsa sukayi sallama da 'yan uwa sai kuka Bilkisu take kamar kada ta bishi. Haka suka tafi cike da kewar gida. A wannan karon ya dad'e a Kano ba'ayi masa canjin wajen aiki ba.
Har Bilkisu ta haifi d'anta namiji suka koma gida domin ayi suna acan. 'Yan uwa sunyi matuk'ar farin ciki, domin Alhaji Mai Wada shine babban 'Dah a zuri'arsu, kuma gashi Allah ya bashi magaji. Anyi taron suna na gani na fad'a, anyi hotuna kowa yayi farin ciki, inda aka sama yaron *RA'EEZ*.
Bayan suna haka ya tafi ya barta anan sai bayan tayi arba'in kafin ta koma. Kwanan su talatin da biyar Mahaifinsa yayi masa waya akan yazo ya d'auki matarsa.
A washe gari ya taho. Bilkisu kuka tasa da taji zasu tafi dan asonta tayi kwana hamsin, sauran matan ma hakuri suka bama Mahaifin Alhaji Mai Wada amma yace sai sun tafi baiga amfanin zamanta ba ta bar mijinta shi kad'ai.
Haka suka tafi sai kuka takeyi. Tafiya suke Alhaji Mai Wada yana tunanin maganganun da sukayi da Mahaifinsa adaren da zasu taho, haka kawai yake jin jikinsa yana sanyi.
Bayan komawarsu da sati biyu fad'a ya kaure a Maiduguri, gaba d'aya babu wanda ya tsira a gidansu. Lokacin da suka samu labari sumewa Alhaji Mai Wada yayi, kwanansa biyu a asibiti kafin ya farfad'o.
Bilkisu ma duk ta fita hayyacinta. Babban aminin Alhaji Mai Wada wato *ALHAJI MANSUR*, shine wanda yake tsaye akansu, shima d'an Kano ne babban d'an kasuwa ne, tunda Alhaji Mai Wada ya dawo Kano ya tab'a taimakonsa akan wasu kayansa da wasu suka so dannewa, tun daga lokacin suka kulla abota, sun zama tamkar 'yan uwa, matarsa *AISHA* suna zumunci da Bilkisu sosai, dan halinsu yazo d'aya.
Bayan da aka sallamesu Alhaji Mai Wada yaso su tafi can garinsu amma Alhaji Mansur ya hanashi dan garin a hargitse yake. Sai da aka rik'a had'a masu da rokon Allah kafin suka samu natsuwa.
Sai da akayi watanni da faruwar abun kafin suka je domin su duba ko akwai wad'an da suka rayu. Haka sukaje ofishin 'yan sanda anan suka samu labarin yanda abun ya kasance. Lokacin da sukaje unguwar su sunsha kuka, dan kamar ba'a tab'a gini a wajen ba. Sun sha kuka haka akayita basu hakuri.
Kasa zama agarin sukayi aranar suka koma Kano. Tun daga lokacin Maiduguri ta fitar masa arai, bai sake tunanin zuwanta ba, domin babu abinda zeyi bayan zuri'arsu sun mutu babu kowa, be tab'a tunanin yaje ko Allah zaisa wasu sun tsira ba, dan har lokacin ance ba'aga gawar wasu ba kuma ba'aji labarinsu ba kawai yacigaba da rayuwarsa da matarsa da d'ansa.
Lokacin da Ra'eez ya isa sawa makaranta haka aka sashi tare da d'iyar Alhaji Mansur *LABIBA*, tare ake kaisu a maidosu tare. A lokacin ne kuma Alhaji Mai Wada ya samu k'arin matsayi inda aka maidashi Lagos aka bashi matsayin shugaban Kwastam acan.
Alhaji Mansur yafi kowa shiga damuwa shida matarsa, domin sun shaku dasu Alhaji Mai Wada, Bilkisu hada kukanta, duk da ta rasa danginta sai Allah ya had'ata da Aisha, tana jinta tamkar 'yar uwarta, sai gashi kuma yanzu zasu rabu.
Ganin halin da suka shiga ita da Aisha har ma da Alhaji Mansur sai Alhaji Mai Wada ya yanke shawarar barin Bilkisu anan domin Ra'eez ya k'arasa makarantarsa. Lokacin da sukaji haka sosai sukayi farin ciki, duk da Alhaji Mansur yaji dad'i amma kuma zaiyi rashin amini nagari.
Haka Alhaji Mai Wada ya tafi cike da fatan nasara, duk lokacin da akayi masa canjin wajen aiki yana sawa ayi masa sauka da addu'oi saboda neman tsari daga mahassada.
Tun farkon zuwanshi Lagos ya fara gano ta'asar da akeyi a wajen aikinsu, baiyi yunkurin hanawa ba duk da ya kasance shugaba, domin abinda ya sani shine ba'a saurin nuna ma mai laifi kuskurensa musamman idan kana bakon waje, ba kamar gari irin Lagos, domin ya dad'e da sanin garin, babu labarin da bai sani ba a hukumar Kwastam ta Lagos, tun kafin yazo garin yake da labari hakan yasa yayi masu kwanciyar b'auna domin ya gano komai cikin sauki ta yanda zai san yanda zai b'ullo masu.
Kowa yasan yanda aikin Kwastam yake, kowa baya da buri wanda ya wuce ya tara abin duniya. Haka ya kasance a wajen da Alhaji Mai Wada yake, akwai mataimakinsa mai suna *ADEBAYO*, d'an *kudu* ne, Allah yayi masa son kud'i ga karb'ar cin hanci kamar me, yana harka da manyan mutane na garin Lagos har ma dana waje, duk wani wanda ake shigo masa da kaya yasan da zaman Adebayo, kafin a canza ma shugabansu wajen aiki shima jirgi d'aya ne ya kwaso su, shiyasa alokacin masu kaya basa jin dad'in abinda ake masu, domin ana karb'ar kud'i awajensu sosai, idan bakaci sa'a ba wani lokacin a kama kayan ka, sai ka saki kud'i masu yawa kafin a sakar maka su.
Da yawa ma'aikatan da suke aiki ak'ansan su basa jin dad'insu, domin idan suka samu sai abinda sukaga damar yaga masu, wasu suna fatan a kawo masu canji yayin da wasu sunfi buk'atar abar masu su kodan samun na cefane da sukeyi.
Tun bayan zuwan Alhaji Mai Wada ya amshi komai a rubuce daga wajen Adebayo, sai rawar jiki yake dan yana so ya samu shiga awajenshi.
Bayan da Alhaji Mai Wada yayi wata guda a wajen sai ya canza wanda yake kula da karb'ar haraji domin ya gano ta wajenshi ana babbar b'arna, haka ya canza wanda yake kula da shigowar kaya da saukesu, haka duk ya tarwatsa kowa Adebayo kuma yace ya tsaya a matsayinsa baya so yana shiga abinda ba aikinsa ba.
Tun daga wannan rana daya tarwatsa kowa mutane da dama sunji zafinsa, yayin da wasu sukaji dad'i, wasu daga cikin wad'an da ake shigo masu da kayansu sunyi farin ciki da zuwan Alhaji Mai Wada, yayin da wasu suke bakin ciki.
Hatta da direban da ya iske wanda yake tuk'ashi sai da ya canza, domin Alhaji Mai Wada bashi da saurin yarda da mutane, tunda ya lura direban yana da kusanci sosai da Adebayo yaji bai kwanta masa ba, domin yasan wasu daga cikin halayyar Adebayo.
Ya dad'e yana tuk'a kanshi kafin ya samu direba mai suna *MALAN SANI*. Ya had'u da Malan Sani wata rana bayan ya dawo daga ofis da dare wajen k'arfe goma da rabi, ya tsaya domin ya sayi biredi sai kawai ya hango Malan Sani ya fito daga wani lungu da gudu sai waige -waige yakeyi, yana tsaye har yazo ya wuceshi sai yaga ya b'oye a bayan motarsa yana lekowa yana kallon hanyar daya fito.
Bayan daya gama siyen biredin sai ya zagayo domin yashiga mota, sam baiji tsoron komai ba ya dafa Malan Sani, a firgice ya jiyo jikinsa yana rawa. Alhaji Mai Wada yace kwantar da hankalin ka babu abinda zanyi maka, zan tafi ne kuma naganka ajikin mota ta shine na tab'o ka.
Hannu Malan Sani yasa ya goge zufar data keto mashi kafin yace na rokeka da Allah ka taimaka mani na fita daga wajen nan, wallahi kashe ni zasuyi. Cike da mamaki Alhaji Mai Wada ya kalleshi, har zai masa tambaya sai kuma yayi saurin bud'e bayan motarsa yana fad'in shiga amma ka duk'e kada aganka.
Yana shiga yaja motar suka bar wajen, babu wanda yayi magana har sai da suka iso unguwar da Alhaji Mai Wada yake kafin ya tsaya agefen hanya ya juyo yana fad'in Malan anan nake da zama kai ina zakaje? Tashi Malan Sani yayi yana kallon inda suke, ajiyar zuciya ya saki yana fad'in ai nazo gida Alhaji, nima anan unguwar nake gidana yana can layin baya.
Alhaji Mai Wada yace nima ga gidana can idan bazaka damu ba mu k'arasa akwai abinda nake son na tambayeka. Malan Sani yace Alhaji yanzu dare yayi, kaga har goma ta wuce, nasan Iyalina suna can cikin damuwa dan bana wuce goma awaje, amma muje ka nuna mani gidan ka ni kuma nayi maka alk'awarin gobe da safe zanzo na sameka.
Kallon Malan Sani Alhaji Mai Wada yayi na wani lokaci, tabbas haka kawai yake jin ya yarda dashi, domin beyi kala da macuci ba, magidanci ne sosai yana da fuskar kamala. Ajiyar zuciya yayi yana fad'in kana da gaskiya, nima bani da iyali shiyasa banyi tunanin dare yayi ba, badamuwa muje kaga gidan nawa.
Har bakin gate suka isa kafin suka fito. Kallon Malan Sani yayi yana fad'in sunana Alhaji Hamza Mai Wada, kuma ni mutumin Maiduguri ne, sai dai Iyalina suna zaune akano, banfi wata d'aya dana dawo nan ba dan anyi mani canjin wajen aiki nine shugaban Kwastam na wannan garin.
Jinjina kai Malan Sani yayi yana fad'in ikon Allah, dama kaine naji ana ta magana a wajen aikin mu? Wallahi ko d'azu naji ana maganar sabon shugaban da aka kawo a wajen da naje. Ni sunana Malan Sani, d'an Katsina ne ni, neman kud'i ya kawo ni Lagos nafi shekara goma sha biyu anan, tun ina k'aramun aiki har Allah ya bud'a mani na samu aikin tuki a kamfanin Fanta, da buga-buga har Allah yasa nayi gidan kaina.
Murmushi Alhaji Mai Wada yayi yana fad'in lallai Malan Sani ka zama d'an Lagos, bara na barka kada ashiga hakkin Iyali, tunda gobe asabar babu inda zanje zanyi jiranka dan akwai abinda nake son ji daga gareka.
Malan Sani yace insha Allahu wajen k'arfe goma zanzo nasan zuwa lokacin ka tashi. Dubu biyu Alhaji Mai Wada ya mik'a mashi yana fad'in ga wannan kayi cefane. Malan Sani yace haba Alhaji ka bar su nagode da wannan taimakon ma da kayi mani. Alhaji Mai Wada yace bafa roko na kayi ba, dan haka ka amsa dan Allah. Amsa yayi yana fad'in nagode sosai Allah ya k'ara bud'i.
Sallama yayi masa ya tafi cike da farin ciki, har sai da kwallar farin ciki ta fito masa. Allah mai jink'ai kenan, ko sisi be tashi dasu ba yau, haka ya fita domin neman aiki har dare be samo komai ba sai rayuwarsa da akaso illatawa, gashi yayima matarsa laifi, ya b'oye mata sallamarsa da akayi daga aiki kusan kwana ukku kenan, a nufinsa idan Allah yasa ya samu aiki yau sai kawai ya fad'a mata ya canza wajen aiki, sai gashi bai samu ba kuma ko kud'in abincin safe bedasu, sai gashi Allah ya kawo masa wannan Alhajin ya bashi har dubu biyu bayan taimakonsa da yayi. Lallai mutanan kirki basa k'arewa duniya.
Haka ya nufi gida cike da farin ciki, yaji dad'in samun kud'in nan domin yana tausayin matarsa saboda tana da tsohon ciki.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋[3/10, 8:38 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kudi ne, naira 200 kacal, MTN card ta wannan lambar.. 08147669770 kayi screen shoot ka tura a whatsapp ta lambar k'asa, idan kuma bank transfer ne ka tuntube ni a whatsapp ta wannan lambar 08028525263*
0⃣4⃣
Da sallama Malan Sani ya shiga gidanshi fuskarsa d'auke da fara'a. Matarsa tana zaune a tsakar gida tana hutawa bayan ta gama shan fatan tsakin da tayi, amsa masa sallamar tayi tana kok'arin tashi tana fad'in sannu da zuwa Malan.
Saurin k'arasowa yayi ya kamata suka zauna yana fad'in haba *HALIMA* kada ki wahalar da kanki kina fama da jikin ki. Murmushi tayi tana fad'in ai bana jin komai. Malan Sani yace ai dai kinyi nauyi kidena yunkurin tashi da sauri haka.
Halima tace Malan hankalina yau ya tashi ganin ka dad'e a waje na d'auka ma ko kunyi tafiya waje mai nisa ne. Murmushi yayi yana fad'in wallahi nima hankalina yana wajenki musamman da nasan ke d'aya ce agidan, yau nayi wani aiki ne shiyasa ban dawo da wuri ba, a hanyar dawowa ta kuma na had'u da wani Alhaji har ya rago mani hanya, layin gaban mu yake da zama shine sabon shugaban Kwastam d'in da aka kawo, to shine fa na tsaya dashi mukayi fira kamar mun san juna.
Halima tace Allah sarki, wallahi har hankalina ya kwanta na d'auka wani abun ne ya faru da kai, musamman da naga yanayin daka fita da safe, baka tab'a barina babu kud'in cefane ba sai yau, acikin kwanakin nan sai nake gani kamar akwai abinda yake damun ka.
Murmushi yayi yana fad'in babu abinda yake damuna kawai kicigaba dayi mani addu'a ina so na canza wannan aikin da nakeyi. Da sauri ta kalleshi tana fad'in ba dai korarka sukayi ba? Murmushi yayi yana fad'in basu kore ni ba kawai nagaji dayi masu aiki ne saboda basu da lokacin tashi, kina ganin kullum idan na fita sai dare nake dawowa, gashi yanzu kinyi nauyi bana son ki haihu ace ina barin ki ke kad'ai, gara na canza aiki kema kirik'a samun kulawa keda abinda zaki haifa.
Halima mun dad'e da aure Allah be babu haihuwa ba, yau gashi Allah ya amshi addu'ar mu kinga dole na tsaya na rik'a kula daku, duk da kince d'iyar yayarki zata zo cikin sati mai kamawa amma nafison ace nima ina kusa da ke.
Murmushi tayi tana fad'in to Allah ya zab'a maka wanda yafi wancan alkhairi, Allah ya kareka daga sharrin ko wane aiki da zaka samu. Hannunta ya kamo yana fad'in amin Halimatus Sa'adiya.
Tashi tayi tana fad'in bara na kawo maka abinci yau dai faten tsaki nayi da wake sai nasa alaiyahu. Malan Sani yace baiwar Allah, ubangiji Allah ya biyaki da aljanna, nasan dai akwai abinci agidan, amma ban bar na cefane ba ashe kin samu kinyi? Halima tace d'azu ne *JAMILA* ta aiko mani da d'ari biyun dana ara mata shine nayo mana cefane dasu.
Malan Sani yace Allah yayi maki albarka, kinga nima wannan Alhajin ya bani dubu biyu yace nayi cefane, kuma gobe da safe yana nemana. Halima tace amma mungode masa Allah ya biyashi da alkhairi. Malan Sani yace amin.
Wucewa ciki tayi ya bita da kallon tausayi, baya so ya fad'a mata halin da yake ciki yasan halinta da damuwa, ga tsohon ciki tana dashi idan taji an koresa a aiki zata shiga damuwa, haka idan ya fad'a mata wasu sun biyoshi d'azu hankalinta bazai kwanta ba. Gara ya cigaba da b'oye mata har Allah yasa ya samu wani aikin.
*WAYE MALAN SANI?*
*MALAN SANI HASSAN*, shine cikekken sunanshi, d'an asalin garin Katsina ne, neman kud'i ne ya kawosa Lagos, tun yana kwana a k'asan gada har ya koma kwana a shago, yasha wahala sosai arayuwarsa kafin ya samu na kanshi, kasancewarsa mutum mai gaskiya da amana yasa duk inda yayi aiki ake sonshi, a hankali yarik'a tara kud'i har Allah ya bashi ikon siyen fili a unguwar *AGEGE*. Da kad'an -kad'an ya fara gini, da a kasuwa yake aiki sai kuma ya fara aiki da masu had'a buhun da ake rufe saman babbar mota dashi (TAMPOL) .
Da wannan sana'ar sosai yake samu, yana aikinsa kuma yana cigaba da gininshi, ya dad'e beyi aure ba sai daga baya yayi aure inda ya auri matarsa Halima, itama 'yar Katsina, gidansu gidan rufin asiri ne, mahaifinta d'an kasuwa ne, hakan yasa ta taso cikin tarbiya da sanin rayuwa.
Bayan da yayi aure sai ya barta a gidan Mahaifiyarsa shi kuma ya koma Lagos, sai ya samu lokaci yake zuwa wajenta, sai dai duk wata yana yi mata aike.
Da haka Allah ya bashi ikon kammala gininshi, inda yayi d'akuna biyu ciki da falo sai band'aki da kicin sai tsakar gida, daga gefen tsakar gidan kuma an fitar da wani d'aki sai dai bai fara ginashi ba ya fitar dashi ne saboda zuwa gaba idan ya samu hali ya gina d'akinshi sai ya bar ma Halima wancan koda ta haihu.
Bayan daya gama komai yaje ya d'auko matarsa suka dawo nan da zama. Sun dad'e basu samu haihuwa ba har Allah ya taimakeshi kamfanin Fanta suka d'aukeshi aikin direba.
Sosai yayi farin ciki da wannan aikin daya samu musamman daya maido da Iyalinsa Lagos nauyi ya k'aru sai gashi kuma Allah ya taimakeshi da aiki mai kyau. Haka suka cigaba da zaman rufin asirin su yayin da Halima ta fara sana'ar saide-saide a cikin gida har Allah ya basu k'aruwa.
*Wannan shine labarin Malan Sani.*
***** ****
Washe gari bayan sun gama karyawa wajen k'arfe goma Malan Sani ya fita domin ya cika alk'awarin da yayi ma Alhaji Mai Wada. Tafiya yake yana tunanin dalilin da yasa Alhaji yake zaune a wannan unguwar, yasan dai duk wanda aka kawo aiki na Kwastam ana bashi wajen zama bare kuma shi da ya kasance shugaba, sai gashi yazo wannan unguwar ya zauna. Da wannan tunanin ya isa k'ofar gidan Alhaji Mai Wada.
Yana kwankwasawa Maigadi ya bud'e. Bayan sun gaisa ya fad'a masa yazo wajen Alhaji ne. Murmushi Maigadin yayi yana fad'in Malan Sani ko? Kai ya d'aga yana mamakin yanda akayi har Alhaji ya fad'ama Maigadi zuwanshi.
Wajen zama ya nuna mashi yana fad'in ai tun jiya Alhaji ya sanar dani zuwanka, shiyasa kana zuwa nayi tsammanin kaine, domin babu wanda yake ma Alhaji sallama da safe haka musamman irin wannan ranar da baya fita aiki da wuri.
Malan Sani yace Allah sarki, ai da yake yau asabar ma'aikata kowa yana hutawa ba aiki. Maigadi yace gaskiya banda Alhaji, gobe ne kawai nasan baya fita wajen aiki, amma asabar yana fita sai dai bada wuri ba, sannan baya wuce magriba ya dawo gida sai ya wuce masallaci wajen da suke d'aukar karatun asabar da lahadi.
Gyara zama Malan Sani yayi yana fad'in gaskiya ban tab'a ganin mutum irin Alhaji ba, a sanina duk wanda ya kai matsayi irin nashi musamman a aikin Kwastam gidan kud'i da wuya kaga yana rayuwa makamanciyar tashi, unguwar da yake zaune kad'ai abun mamaki ne, sai irin yanda yake rayuwa kuma.
Maigadi yace indai Alhaji ne yanzu ka fara ganin abubuwan mamaki a wajensa, sam be d'auki duniya da zafi ba, mutum ne shi mai saukin kai, ga addini, kana ganin yawancin masu irin aikinsu yanda suke kasancewa musamman idan akace su kad'ai suka zonan ba tare da Iyalin su ba, sai kaga sun aikata abinda suka ga dama.
Ka ganni nan tun farkon zuwan Alhaji garin nan Allah ya had'ani dashi, yazo unguwar nan yana neman gidan haya mai kyau shine naji wasu suna neman damfararsa, ina gefe sai banyi magana ba, asalima sai na tashi nabar wajen dan bana so su fahimci ina wajen kasan yanda rayuwar Lagos take yanzu zasu far maka.
Bayan da suka gama shima kamar ya san mai suke nufi sai yace masu bara yaje ya dawo, ganin basu samu nasara ba sai suka wuce suka kyaleshi. Har yashiga mota yayi hanyar fita na tarbeshi, bayan ya fito na fad'a masa gaskiya abinda wad'an can mutanan suke da niyar yi masa. Murmushi yayi yace mani ai ya fahimcesu shiyasa ya kyalesu.
Anan yake fad'a mani abinda yakeso, an bashi gida acan wajen aikinsu amma yafiso ya shigo cikin mutane ya zauna kafin ya gama gane komai na garin sai ya canza wajen zama. Jin haka yasa nayi masa jagora wajen mai wannan gidan, domin wani ne ya zauna daya tashi kuma bakowa ciki.
Tunda ya samu gidan nine na tsaya aka gyara komai. Bayan da aka gama sai yake tambayata aikin da nakeyi, shine nake fad'a masa ina 'yar buga-buga ne dan bani da iyali, tunda nayi aure mata ta rasu wajen haihuwa acan garin mu shikenan na taho Lagos da zama saboda ban aje kowa ba.
Jin haka yace kawai hankalinsa ya kwanta dani, idan na amince zanyi masa gadi zai rik'a biya na, amma da sharad'in duk ranar daya kamani da cin amanarsa saiyasa an kulle ni. Jin abinda yace jiki na rawa na amince, domin na samu wajen zama mai kyau, da zakaga inda nake rayuwa ada zaka tausaya mani, bacci kawai yake kaini wajen, da nayi asuba zan fice, sai gashi Allah ya kawo mani Alhaji ya taimakeni, shiyasa nake zaune dashi da gaskiya, yana da dad'in zama sosai, sam beda mugunta, yana kyautata mani, kullum sai ya bani kud'in siyen abinci kuma k'arshen wata ya bani albashi, hatta da mukullin cikin gidan ina dashi, domin duk bayan kwana biyu ina shiga ina gyarawa, d'akinshi ne kawai banda mukullinshi, kalli d'akin da nake zaune yanzu.
Jinjina kai Malan Sani yayi yana fad'in gaskiya ka godema Allah, kuma kacigaba da rik'e gaskiya arayuwar ka, domin itace tasa ka kawo matsayin da kake ayanzu, shiyasa ake so duk inda mutum yake ya kasance mai gaskiya. Sai dai baka fad'a mani sunanka ba.
Maigadi yace sunana *AMADU* amma anfi kirana da *MADU*. Malan Sani yace sannu Amadu suna mai dad'i. Fitowar Alhaji Mai Wada yasa sukayi saurin tashi.
K'arasowa yayi da sauri yana murmushi. Bayan sun gama gaisawa yace lallai Malan Sani kana da cika alk'awari, shiyasa nace bara na leko naga ko kazo nasan Madu bazai kirani ba zaiyi tunanin ko ban tashi ba. Malan Sani yace ai tunda nace zan zo bazan sab'a alk'awari ba, gashi nazo muna ta fira da Madu ma.
Alhaji yace bismilla kashigo. Kallon Madu yayi yana fad'in ina fatan dai ka karya? Madu yace ai tun d'azu naci k'osai da koko. Alhaji yace haka ake so, Malan Sani kashigo.
Bayan sun sake gaisawa Alhaji ya kawo masa shayi da kyar Malam Sani yasha. Kallonshi Alhaji Mai Wada yayi yana fad'in Malan Sani nasan zakayi mamakin kiran da nake maka, ba wani abu bane yasa nace kazo illa abinda na gani jiya, tunda na ganka kawai naji ka kwanta mani, hakan yasa naji ina so nasan kad'an daga cikin labarin ka, domin ajiya naga wasu mutane sun biyo ka da kyar kasha.
Jinjina kai Malan Sani yayi yana fad'in Alhaji wannan labarin ko Mata ta ban fad'amawa ba, domin tana da tsohon ciki, hakika ina cikin damuwa, kuma naji na yarda da kai zan iya fad'a maka koni waye......
Bayan ya gama bashi labarin asalinsa ya d'ora da fad'in, nayi kusan shekara ina aiki da kamfanin yin Fanta, kuma har lokacin nine nake tuk'a motarsu, da farko ban fahimci komai ba, a hankali na fara gano wani abu da suke aikatawa a kamfanin, kuma manajen wajen shine yake da alhakin yin komai, wata rana bayan na tashi daga aiki har nayi masu sallama na tafi sai na manta na sayi biredi na had'a da lemun da ake bamu na aje a mota ban d'auko ba, hakan yasa nayi saurin komawa domin na d'auko.
Kasancewar kullum acan nake barin su Manaja da wasu daga cikin manyan yaranshi, sai su kai sha biyun dare basu tafi ba, ban tsaya bin ta wajen su ba kawai na wuce wajen mota domin na d'auki abinda na manta.
Muryar d'aya daga cikinsu naji yana fad'in akwai kayan da aka kawo masu daga wajen John d'azu, wai daga waje ya shigo dasu kuma lafiya lau aka dubasu a bakin ruwa kuma aka wuto dasu, domin ya saki kud'i sosai shiyasa Kwastam d'in wajen basu binciki kayan ba, yanda naji yana fad'i wasu maganin shaye-shaye ne irin na kwalba kamar dai maganin tari, to irinsu ne ya shigo dasu sai dai kwalinsu na lemu ne irin na waje, idan ba an bud'e ba baza'a tab'a sanin ba lemun bane aciki, yana fad'in zasu samu kud'i sosai da kayan.
Bayan ya gama fad'a masa sai naji Manaja yana fad'in ai sunyi magana da John zasu rik'a siyar da kayan ab'oye tunda kowa yasan harkar lemu sukeyi yan drugs bazasu saka idonsu akan kayan ba, yace zasu rik'a d'ora kayan had'e da katan d'in Fantar da muke d'auka muna kaiwa wajen da ake sara.
Jin wannan abun sai hankalina ya tashi, domin nasan zanyi aiki ne da haramtacciyar abu aciki, alokaci sai na kasa rik'e firgici na har suka jiyo motsi, ganin sun taho zasu duba yasa nayi saurin bud'e mota na d'auko leda ta na fito ina kok'arin b'oye damuwata na fad'a masu mantuwa nayi.
Ganin Manajan ya tsura mani ido yasa na d'an daburce, gashi dama Inyamuri ne, sai kawai ya matso kusa dani yana fad'in tun yaushe nake awajen? Ganin yanda hankalinsa ya tashi yasa nace zuwana kenan. Matsowa d'ayan yayi yana fad'in Manaja nima yanzu naji motsinshi da alama yanzu yazo.
Kallona yayi yana fad'in ka tabbata babu abinda kaji? Kai na d'aga mashi ina fad'in babu abinda naji dan hankalina yana wajen kayana. Kai ya jinjina yace zaka iya tafiya. Bayan tafiya ta bansan abinda suka tattauna ba, ni dai haka na isa gida jikina babu kwari, rayuwata ina tsoron cin dukiyar data fito da haramun acikinta, musamman ace kasan abinda ake kullawa amma kacigaba da aiki a haka, nasan kona je na fad'ama 'yan drugs za'a iya samun masu karb'ar cin hanci a rufe maganar ni kuma na jawo ma kaina, hakan yasa na yanke shawarar barin aikin na nemi wani, duk da Matata tana da tsohon ciki amma naji aikin ya fitar mani, nasan yanda aiki yake da wahalar samu a Lagos, amma ya fiye mani na bar aikin da dai arik'a aikata b'arna dani kuma nasan komai.
A waccan shekaran jiyar ina zuwa wajen aiki na samu takarda daga wajen Manaja ta sallamar aiki wai na manyanta da yawa sunfi son Matasa, gaba d'aya kud'in da suka bani na sallamata dubu talatin ne, ganin haka yasa nayi hamdala ga Allah, ban nuna masu komai ba mukayi sallama dasu, haka naje na siyo komai na abinci, domin nafison na aje abinci da na rike kud'i ahannu na, nasan har Matata ta haihu bamu da matsalar abinci, kud'i ne dai bani dasu a hannu, domin acikin kud'in nayi biyan bashi dan nasan banda aiki bare nace sai na kwashi albashi kafin na biyasu, hakan yasa na biya duk mai bina bashi saura nayi cefanan gida.
Wallahi Alhaji ajiya da muka had'u bana maganin naira biyar a aljihu na, haka na bar gida ko kud'in cefane ban bayar ba, nasan dai akwai abinci shiyasa ban damu ba, sai gashi Allah yasa ka bani wad'an nan kud'in.
Jinjina kai Alhaji yayi yana fad'in to amma su waye suka biyoka jiya? Malan Sani yace wallahi ban san su ba, kawai ina zaune bayan na gama neman aikin yi na rasa sai na zauna bayan nayi sallar isha'i ina jiran wani Alhaji da naji ance yana neman direba, na dad'e a wajen ina jiranshi amma bai dawo ba, ganin dare yayi nace bara na tafi yau na koma kozan dace.
Kawai na taho sai had'uwa nayi da wasu Matasa suna kok'arin yin Lalata da wata yarinya sai ihu take yi, cikin azama nayi kansu ina kok'arin ceton ta, da kyar na kwaceta daga wajen su nasa ta gudu, ganin ta tafi yasa sukayo kaina d'auke da adduna, shine fa na gudo har Allah yasa muka had'u, sauki na d'aya akwai duhu babu wanda ya sheda fuskata bare naji tsoron sake had'uwa dasu. Kaji dalilin da yasa suka biyo ni.
Jinjina kai Alhaji Mai Wada yayi yana fad'in lallai Malan Sani ka had'u da jarabawa, tabbas kai mutumin kirki ne, ba kowa ne namiji bane zaka samu wanda yake gudun tashin hankalin Iyalinsa ba, kayi kok'ari daka iya b'oye mata halin da kake ciki, kuma wannan abun da kayi shine akeson mutane surik'a aikatawa, matuk'ar ka gano ana aikata haramtaccen abu a wajen da kake samun na abinci abinda zai fi maka kayi kok'arin barin wajen, musamman idan kasan cewar ko ka fad'i gaskiya baza tayi aiki ba.
Ina mai tabbatar maka da ace wad'annan mutanan sun gano cewar kaji su bazasu barka ba, dole su nemi rayuwar ka domin gudun kada ka tona masu asiri, da yawa yanzu ana aikata kasuwanci had'e da haramtacciyar harka, tun zuwana garin nan na gano abubuwan da suke gudana, kasan yanayin aikin mu, duk kayan da za'a shigo dasu hakkin mu ne mu tabbatar da nagartarsu kafin a wuce dasu, kasancewar gaskiya tayi k'aranci yasa mutanan mu suke son karb'ar cin hanci, domin mutane da yawa suna shigo da kaya ba bisa k'aida ba, wannan dalilin ne yasa suke sakin kud'i ga masu matattar zuciya acikin mu domin su samu kayansu su fito lafiya, tabbas k'asar mu bazata cigaba ba matuk'ar muna da irin wad'annan mutanen, nasan ni d'aya bazan iya gyara su ba, amma ga Allah na dogara, kamar yanda nayi rantsuwa zanyi aikina bisa gaskiya da amana to bazan gajiya ba, zanyi kok'ari wajen ganin na kare hakkin aikina, naci ta hanyar halak d'ina, kuma insha Allahu zanyi kok'ari wajen gano b'ara gurbi acikin yankina.
Malan Sani yace hakika Alhaji kai d'in mai gaskiya ne, tun bayan zuwanka na fara jin labarin ka, duk da baka fara aikata komai ba amma naji wasu daga cikin manya sun fara tsoron kada ace kazo da wani abu daban ba kamar wanda ka canza ba, domin sun riga sun saba dashi, sam basu da wata matsala tun alokacin tsohon shugaban kwastam, tun lokacin da na fara jin magana akan ka nake tunanin ko dai Allah ya kawo mai gaskiya ne, duk wanda kaji ana yawan magana akanshi to akwai wani abu na daban agareshi.
Alhaji Mai Wada yace wannan haka yake, hakika ina tsoron kaidin mutane, wannan aikin da nake son tabbatarwa yana da matuk'ar had'ari, domin duk wanda ya fito a zamanin nan yace yana son ya kauda b'arna to yasa aranshi zai iya mutuwa a kowane lokaci, domin su dai masu aikata b'arnar bazasu so wani ya dakatar dasu ba, domin ayanzu mutane sunfi sha'awar aikata haramun akan aikin halak, domin shed'an yariga ya gama da zuciyarsu, ya nuna masu hanyar haramun tafi kawo kud'i, shiyasa zaka iske kowa yanzu wannan hanyar yake bi sai dai fatan shiriya kawai.
Ajiyar zuciya yayi ya kalli Malan Sani yana fad'in, naji labarin ka Malan Sani, kuma na yarda da kai sosai, zuciyata ta aminta da kai har naji dad'i daka fad'a mani mutumin da yake neman direba baka sameshi ba, ina ganin nine wanda Allah yayi ma zab'in ka shiyasa baka sameshi ba.
Murmushi Malan Sani yayi domin yaji dad'in kalaman Alhaji Mai Wada, saboda tunda yaji labarinsa yaji yana son kasancewa dashi. Kamar daga sama yaji Alhaji Mai Wada yana fad'in idan bazaka damu ba Malan Sani inason ka kasance direba na, domin na yarda da kai, na dad'e ina neman wanda zai rik'a tuk'ani amma tsoro yasa na kasa samu har yanzu, kasan yanayin yanzu amana tayi k'aranci, amma samun ka ayanzu yasa zuciyata ta aminta da kai.
Hamdala Malan Sani yayi yana fad'in ina matuk'ar godiya Alhaji, Allah maji rok'on bawansa, cikin rufin asirinsa ya kawo mani mafita tun kafin mai d'akina tasan halin da nake ciki, hakika naji dad'in samun wannan aikin, domin Mai d'akina zata iya haihuwa a kowa ne hali, ko yanzu akace ta haihu baza ayi gardama ba.
Murmushi Alhaji yayi yana fad'in babu komai Malan Sani, abinda nake so kawai shine amana, Allah ya had'ani da maigadi nagari, na roki direba nagari gashi Allah ya bani, babu abinda zanyima Allah sai godiya. Dan haka inaso ranar litinin kazo ka fara aiki, kud'in albashinka ayanzu naira dubu talatin ne awata kafin zuwa gaba muga abinda za'a k'ara maka.
Zaro ido Malan Sani yayi cike da farin ciki yake godiya, kallon Alhaji yayi yana fad'in na rasa bakin magana, ina d'aukar dubu sha biyar ada sai gashi yanzu Allah ya juya mani, ina dab da samun zuri'a sai gashi Allah ya kawo mani cigaba, nagode sosai Allah ya k'ara bud'i ya kuma bamu zaman lafiya.
Alhaji zaiyi magana wayar Malan Sani tayi k'ara. Saurin d'auka yayi ganin sunan makwabcinsa ne. Bayan sun gaisa ya fad'a masa suna asibiti da matarsa tana nakuda shine matarsa tashiga ta fito da ita ya kaisu a motarsa.
Saurin tashi yayi yana fad'in ganinan zuwa. Kallonshi Alhaji yayi yana fad'in ko haihuwar ce? Kai Malan Sani ya d'aga jiki asanyaye. Tashi Alhaji yayi yana fad'in bara na d'auko mukullin mota mu tafi tare. Sakin baki Malan Sani yayi yana kallonshi jin irin karamcin da yayi masa.
Yana tsaye har ya fito suka nufi waje. Hannu Malan Sani ya mik'a yana fad'in Alhaji kawo na tuk'a mu. Murmushi Alhaji yayi yana fad'in haba yanzu ai baka cikin natsuwar ka, ka bari na tuk'a mu. Madu ne ya k'araso yana tambayarsu lafiya? Alhaji ne yayi masa bayani. Murmushi yayi yana masu fatan alkhairi. Haka suka fice Malan Sani sai addu'a yake Allah ya sauketa lafiya shima yaga kwanshi a duniya.
Ur's.
Nabeelert Lady🖋
[3/10, 8:38 AM] +234 703 008 7807: *Wannan littafin na kudi ne, naira 200 kacal, MTN Card a wannan lambar... 08147669770, kayi screen shoot ka tura ta whatsapp a lambar k'asa, idan kuma bank transfer ne ka tuntube ni a whatsapp ta wannan lambar 08028525263.*
0⃣5⃣
Tsaye suke a cikin asibitin, Malan Sani ya kasa zama duk yashiga damuwa, tsoronshi d'aya kada ya rasa Matarsa, gashi tun kafin suzo aka kawota tana nakuda har sunzo da kusan mintuna ashirin amma shiru.
Alhaji Mai Wada ne ya dafashi yana fad'in addu'a zakayi mata Malan Sani, wannan damuwar bazata amfanar da komai ba, kai namiji ne ya kamata kasa dauriya aranka.
Jinjina kai Malan Sani yayi yana fad'in nagode Alhaji. Fitowar wata ma'akaciyar asibitin ne yasa sukayi saurin matsawa wajenta. Bakinta a washe take tambayarsu sune suka kawo Halima? Da sauri Malan Sani ya amsa mata.
Murmushi tayi tana fad'in Halima ta sauka lafiya Allah ya azurta ta da 'Diya mace, tasha wahala sakamakon dad'ewar da tayi bata haihu ba kuma gashi haihuwar faari, wannan shine ya jawo mata doguwar nakuda amma yanzu suna lafiya.
Hamdala Malan Sani yayi yana mata godiya. Murmushi tayi tace ai bakomai, yanzu ana gyara ta idan aka kaita d'akin hutu zaku iya ganin ta. Hannu Alhaji Mai Wada yasa a aljihu ya ciro kud'i masu yawa ya bata yana fad'in ga tukuicin ki. Amsa tayi tana masa godiya ta wuce tana fad'in idan kun gama kuje wajen likita akwai maganar da zakuyi.
Bayan da aka maida Halima d'akin hutu Malan Sani yaja Alhaji Mai Wada suka nufi d'akin. Sai murmushi yake yana kallon matarsa. Alhaji kuwa yarinyar ya d'auka ya tsura mata ido domin Allah yayi mata kyau tun tana jaririyarta, yana matuk'ar son mace amma Allah be bashi ba.
Mika ma Malan Sani ita yayi yana fad'i kayi mata hud'u ba. Murmushi yayi yana fad'in Alhaji wannan yarinyar da namiji ne sunanka zan saka, domin had'uwata da kai akwai alkhairi acikinta.
Murmushi Alhaji yayi yana fad'in bakomai a hakan ma nagode. Amsarta yayi nan take yayi mata hud'uba da *RUMAISA*, suna ne da Halima take matuk'ar so, tasha fad'in duk ranar data haifi mace wannan sunan za'asa.
Ajeta yayi akusa da Halima yana fad'in Allah ya amsa addu'arki ya baki mace kuma ansa mata sunan da kike so wato *RUMAISA.* Murmushi tayi tana duk'ar da kai dan kunyar Alhaji take ji.
Tare da Alhaji suka fita yace ya mik'ashi wajen aiki sai ya dawo da motar saboda d'aukar matarsa da Rumaisa. Sosai wannan abun yayi ma Malan Sani dad'i, haka yayi ta jera masa godiya kamar zaiyi kuka.
Bayan ya kaishi Alhaji ya miko masa dubu goma yana fad'in ga wannan kasa a aljihun ka nasan zaka buk'ace su. Har k'asa Malan Sank yazo duk'awa da sauri Alhaji ya rik'osa yana fad'in daga yau kada ka sake yunkurin aikata hakan, ni ba kowa bane dan haka ka d'aukeni tamkar d'an uwanka.
Jinjina kai Malan Sani yayi yana goge hawayen farin ciki yayi masa godiya yana fad'in anjima zan dawo na d'auke ka. Alhaji yace kada ka damu zan hau motar haya ka aje motar a wajenka saboda zirga-zirga, idan ka gama zuwa dare sai ka kawo mani.
Rasa bakin magana Malan Sani yayi sai kawai ya fashe da kuka. Murmushi Alhaji yayi ya dafashi yana girgiza masa kai kafin ya shige ofis d'insa.
Wannan abu da Alhaji yayi ma Malan Sani ba k'aramun dad'i yayi masa ba, yanaji aransa duk duniya baya da kamar Alhaji ayanzu, yasa aranshi zai iya bada ranshi akan Alhaji. Haka ya nufi kasuwa domin sayen abubuwan buk'ata kafin a sallame su.
A ranar Malan Sani ya kira gidan su ya fad'a masu haihuwar, sosai sukaji dad'i domin abinda kowa yake fata ne. Nan aka turo wata Gwoggonta da 'Diyar Kawunta suka taho.
Sai k'arfe d'aya kafin Malan Sani yaje amsar sallama. Anan likita yayi masa bayanin kada ya bari Halima ta sake d'aukar ciki yanzu saboda mahaifarta ta wahala akan wannan haihuwar, idan samu ne su bari kamar nan da shekara biyar kafin ta sake d'aukar ciki.
Malan Sani yace to mungode likita, sai ku aunata domin abata abinda zaiyi dai-dai da jininta wanda zai hanata d'aukar cikin. Murmushi likita yayi yana fad'in ina son mutane irin ku masu saurin fahimta, bara na had'aka da wata ma'aikaciyar mu itace take kula da wannan b'angaren, Allah ya bada lafiya. Sallama Malan Sani yayi masa yana masa godiya.
Haka suka tafi gida cike da farin ciki. Lokacin da suka isa har Jamila makwabciyarsu ta sauke ruwan wanka ta kammala girki. Sosai Halima taji dad'i, dama irin abinda take gudu kenan ace ta haihu babu kowa nata, sai gashi Allah ya bata makwabciya tagari.
Sai dare Malan Sani ya maida ma Alhaji motarsa yana sake masa godiya. Alhaji Mai Wada yace haba bakomai, zuwa gobe kazo akwai abinda zaka amsa. Malan Sani yace nagode Allah ya kaimu.
Sai tsakiyar dare Gwoggon Halima suka iso saboda basu taso da wuri ba, Malan Sani ne yaje ya d'auko su. Halima baki yaki rufuwa yau 'yan uwanta sunzo.
Washe gari haka 'yan barka sukayi ta shigowa wad'an da suke mutunci dasu kasancewar unguwar ba laifi akwai hausawa, yaren ma akwai wad'an da suke mutunci.
Sai da akayi azahar Malan Sani yaje gidan Alhaji dan baya so yaje ya tashesa. Malan Sani ya cika da mamakin kayan abinci da Alhaji ya bashi, sannan ya kawo kud'in rago ya bashi hada na cefanan suna wanda zasu ishe sa ya saya ma Halima kayan fitar suna.
Yana hawayen farin ciki yashiga yimasa godiya. Tare da Madu suka d'auki kayan a mota shima yaje ganin jaririya. Bayan ya ganta sukayi sallama Malan Sani ya nufi kasuwa domin ya siyo ma Halima kaya ya k'aro ma Rumaisa kaya duk da sun sayi wasu sai da lokacin basu san abinda zasu haifa ba hakan yasa suka sayi na jinsi d'aya wanda mace da namiji duk zasu iya sawa.
****
Ranar litinin tunda wuri Malan Sani ya isa gidan Alhaji bayan daya gama aje masu komai na buk'ata. Zama yayi wajen Madu suka shiga fira kafin Alhaji ya fito.
Alhaji yana fitowa ya cika da mamakin ganin Malan Sani ganin har yazo shida yake da hidima. Tasowa sukayi gaba d'aya suna gaishe shi. Alhaji yace lafiya lau, Malan Sani ina masu jego? Malan Sani yace suna lafiya. Alhaji yace ai da ka bari sai gobe ka fara zuwa.
Malan Sani yace haba Alhaji nida ba mace ba, na gama masu komai shiyasa na fito, nima bazanji dad'in zama agidan ba, nagode Allah da yasa na samu wannan aikin da yanzu haka zanyi ta gararan ba. Murmushi Alhaji yayi ya mik'a masa mukullin yana fad'in haka ne, gashi muje.
Sallama suka yima Madu suka tafi. Malan Sani yayi mamaki ganin Alhaji ya zauna agaba, kasa daurewa yayi ya kalleshi yana fad'in Alhaji ai daka zauna a baya. Murmushi Alhaji yayi yana fad'in hakan ma yayi nafi buk'atar na zauna agaba. Murmushi Malan Sani yayi yana fad'in Alhaji kai na daban ne. Beyi magana ba yacigaba da duba wasu takardu.
Lokacin da suka isa ofis mutane sunyi mamaki ganin Alhaji Mai Wada tare da wani, sai dai basuyi tunanin direba bane saboda sun ganshi agaban mota.
Sai bayan da suka tsaya Malan Sani ya fito ya d'auko masa takardunsa yabi bayansa sukayi tunanin direba ne. Haka yayi ta gaisawa da mutanan wajen anan ya gabatar masu da Malan Sani amatsayin direbansa. Sunyi mamaki da jin haka domin sunyi tunanin acikin masu aikin wajen zai d'auki direba.
Kai tsaye suka wuce ofis d'inshi, bayan ya aje masa takardu Alhaji yace Malan sani zaka iya tafiya idan ina da buk'atar wani abu zanyi maka waya tunda kana da hidima.
Risnawa Malan Sani yayi yana fad'in nagode, mukullin motar ya d'ora masa saman teburi yana niyar barin ofis d'in. Sunanshi Alhaji yakira yana fad'in idan ka bar motar anan ai babu abinda zanyi da ita, kawai ka tafi da ita kayi abinda ya dace.
Dawowa yayi ya d'auki mukullin yana sake masa godiya. Murmushi Alhaji yayi yana fad'in agaishe da Maijego. Fiya yayi yana murmushi yace zataji.
Kwankwasa k'ofar akayi hakan yasa Alhaji ya bada izinin shigowa. Masinjansa ne yashigo yana gaishe sa. Alhaji yace *Malan Bala* katashi lafiya? Nashigo ban ganka ba nazo da sabon direbana naso in had'aku amma ya tafi.
Risnawa Malan Bala yayi yana gaishe shi kafin yace na zagaya baya ina d'auraye tsumman dana goge ofis d'in ne, amma ai zai dawo ko? Alhaji yace zai dawo yaje gida ne matarsa ce ta haihu.
Malan Bala yace masha Allah, Allah ya raya, gaskiya naji dad'i daka samu direba, domin wasu suna tunanin baka son ka d'auki direba saboda karik'a cinye kud'in da ake fidda masu.
Murmushi Alhaji yayi yana fad'in hada kai acikin masu fad'in haka kenan? Zaro ido Malan Bala yayi yana fad'in haba dai Alhaji, kaima zaka mani shedar kirki ai, wallahi ko d'aya bana maka mugun zato, domin tun bayan zuwanka nan rayuwata ta canza, mezaisa na shiga cikin masu zagin ka? Jinjina kai Alhaji yayi yana fad'in wasa nake ma Malan Bala, kada ka damu da duk abinda mutane zasu fad'a akaina, domin idan kana biye ta mutane bazaka tab'a yin gaba ba, kai dai kasa Allah aranka.
Malan Bala yace insha Allahu. A had'o maka shayin ne? Alhaji yace sai zuwa anjima nasha agida. Risnawa yayi yana fad'in ahuta lafiya. Yana kok'arin fita sai ga mataimakin Alhaji yashigo ofis d'in, gaishe sa Malan Bala yayi kafin ya fita.
Hannu Adebayo ya mik'a ma Alhaji yana fad'in barka da safiya Sir, murmushi Alhaji yayi yana fad'in yauwa Mr. Adebayo ka tashi lafiya? Cikin harshen turanci ya maida mashi da lafiya lau, saboda Adebayo yafi son magana da turanci duk da yana jin hausa sosai, amma saboda bata zauna abakinsa ba yasa yafison yayi magana da turanci koda kuwa abokin maganarsa da hausa yake masa magana saboda yana jin hausa maidawarce take masa wahala.
Zama yayi yana mik'a ma Alhaji wata takarda yana fad'in *Alhaji Marusa* babban mutumin nan mai shigo da kayan na'urori da sauran kayan masarufi na k'asar waje shine ya aiko da wannan takardar akan yana son sa hannunka saboda yana samun matsala da ma'aikatan mu akan kayansa, duk da kowa yasanshi yasan matsayinsa amma ana samun wasu daga cikin ma'aikatan mu suna rik'e masa kaya, wani lokacin kuma suna bincikar masa kaya suna b'ata masa lokaci har hakan ya kan jawo masa asara, kafin zuwanka Oga ne ya tsaya masa, domin kowa yasan irin matsayin daya taka ak'asar nan, to bayan tafiyar Oga sai ya fara samun matsala da mutane, duk da akwai wad'an da suke kular masa da kayanshi amma wannan karon sai da ya kira Oga yayi masa magana, shine ma Oga yakirani akan nazo kasa hannu domin ya zama sheda akan duk wasu kaya da za'a shigo dasu nashi ba sai an bincike su ba tunda ansan abinda yake shigowa dasu.
Tunda ya fara magana Alhaji ya had'e hannu ya jingina da kujera yana kallonshi murmushi kwance a fuskarsa. Jin Alhaji yayi shiru bece komai ba yasa Adebayo yacigaba da fad'in Alhaji akwai babbar sallamar da muke samu daga Alhaji Marusa, sam beda rowa, yasan yanda muke masa mutunci shiyasa yake sakar mana kud'i, kuma munyi bincike babu abinda yake shigowa dashi wanda ya sab'a doka hakan yasa muka aminta dashi.
Wannan karon k'aramar dariya Alhaji yayi ya gyara zamanshi yana fad'in Mr. Adebayo taya kasan cewar baya shigo da kayan da suka karya doka? Saurin kallon Alhaji Adebayo yayi yana motsa baki. Takardar Alhaji ya amsa yana fad'in idan har zamu iya sa hannu akan wasu surik'a shigo da kaya ba tare da an bincike su ba ina ganin babu amfanin gwamnati ta ajemu tana biyan mu anan, idan muka kyale wasu wad'an da muke kamawa kuma su basu da hakki akan mu? Mr. Adebayo ina so ka fahimci wani abu guda, duk abubuwan da suke faruwa ak'asar nan mune muke haifar dasu, idan muka rik'e aikin mu babu yanda za'ayi arik'a shigo mana da haramtattun kaya a k'asar mu, kana ganin k'asashen da suka cigaba sai dai ashigo da kaya marasa kyau ta b'arauniyar hanya, domin ma'aikatansu sun rike gaskiya, mu kuma sai muka banzatar da aikin mu muka rik'a barin ana shigo mana da kaya ta hanyar daya kamata ace mun tsare ta, sam masu aikata hakan basu da damuwar bin b'arauniyar hanya domin sun san mud'in kwad'ayayyu ne, da sun watsa mana tsaba sai mu saki hanya mu koma muna tsintar abinda suka watsa, su kuma sai su koma suna abinda suka ga dama, duk abubuwan da suke faruwa anan babu wanda ban sani ba, wasu tun kafin nazo wajen nan nake da masaniya akan su, wasu kuma bayan zuwa na na karance su, wannan dalilin ne yasa tunda nazo bance komai akan aiki ba, na zuba ido domin na gama karantar kowa, kuma daga yau ne aikina zai fara, wannan dalilin ne yasa na cireka daga bakin boarder domin ba aikin daya kamata kayi ba kakeyi.
Wata takarda ya d'auko yana fad'in wannan sune sabon tsarin dana kawo, kuma yanzu nake jiran kashigo na fad'a maka k'arfe goma akwai taro domin kowa yaji sabon tsari, sai kuma gashi kazo mani da wannan maganar, dan haka ka fad'ama sauran ma'aikata sakona, ina fatan ka fahimce ni? Kai Adebayo ya jinjina zuciyarsa tana masa zafi, dama shi tunda Alhaji Mai Wada yazo haka kawai yaji baya sonshi, shiyasa yafi son akawo masu yaran su sunfi jin dad'in aiki dasu, amma idan aka kawo bahaushe musulmi da wuya ya basu goyon baya musamman idan mutumin bashida had'ama.
Tashi yayi ya d'auki takardar da ya bama Alhaji yana fad'in shikenan zan koma ofis sai zuwa anjiman. Murmushi Alhaji yayi yana d'aga masa kai. Haka ya fita cike da jin haushi. Murmushi kawai Alhaji yayi yacigaba da aikin da yake gabansa.
***
Cike d'akin taron yake da ma'aikatan wajen tun daga masu gadi, masinjoji har zuwa manyan ma'aikata. Bayan an bud'e taro da addu'a Alhaji Mai Wada ya bama Adebayo izinin yayi ma sauran 'yan uwansa jagoranci suyi tasu addu'ar. Bayan sun gama Alhaji ya bama Adebayo takardar yace yarik'a karantowa sai shi yayi bayani.
Zuciyar Adebayo a cunkushe ya mik'e, sai dai da yake d'an duniya ne babu wanda zai iya fassara abinda yake a fuskarsa. Haka ya fara karanto sabon tsarin Alhaji yana bayani d'aya bayan d'aya.
Gaba d'aya wajen kowa yayi shiru, masu jin dad'i sunayi masu jin haushi sunayi. Bayanin da Alhaji yayi na k'arshe yafi d'aga ma wasu hankali, musamman masu aikata irin laifin.
Kallon mutanan wajen Alhaji Mai Wada yayi yana fad'in wannan dokar itace doka ta k'arshe acikin jerin dokokin dana rubuta, shiyasa na barta a k'arshe domin ba abu bane na wasa.
Kamar yanda na fad'a zan sake maimaitawa, duk wanda aka kama da laifin karb'ar cin hanci daga wajen masu kaya za'a dakatar dashi har na wata ukku ba tare da albashi ba, idan aka maidoshi ya sake aikata hakan to kora ce, ba haka dokar take ba, nine na sassautata domin bana fatan na zamo wanda zaiyi silar korar wani daga wajen nan, domin bazanji dad'i ace nine silar katse mashi hanyar abincinsa ba, amma abinda nakeso daku shine ku daure ku bani had'in kai domin mu gyara tare, kowa yasan yanda yankin mu na nan garin Lagos yayi suna, domin mune manya, inaso na kawo cigaba, ba dole sai mun amshi cin hanci zamu samu kud'i ba, akwai mutanan da suke bada kyauta saboda kawai an tsare masu kaya sun sauka lafiya, dan haka kowa yayi kok'arin kiyayewa, insha Allahu zaku sameni mai adalci agare ku.
Sai magana ta biyu, kowa ya tsaya a inda aka ajeshi, duk wanda kayansa suka iso zamu tsaya muyi binciken daya kamata kafin mu badasu, babu wani dalili da zaisa ace baza'a binciki kayan wani ba, komin matsayinsa, komin ikonsa matuk'ar kayansa suka iso dole a tabbatar da ingancinsu kafin a sake su, duk wanda muka kama da wannan laifin zai fuskanci hukunci, ku daure ku tsaya a binciki kaya, gara su dad'e ba'a sake su ba da muyi sauri mu saki kaya bayan akwai haramtattu aciki.
Wannan shine iya sabon tsarin dana kawo, ina fatan kowa zai fahimceni, nasan wasu zasuji haushi, dama haka abun yake, dole sai anyi b'arna kafin ayi gyara, kuma sai an daure kafin a tsaida gaskiya, dan haka wanda beji dad'in wannan sabon tsarin ba ina mai bashi hak'uri haka aikin kwastam yake.
Gaba d'aya wajen ya d'auki tafi, masu jin haushi ma haka suka daure suka tafa masa, Adebayo bazaka tab'a gane yanayin da yake ciki ba. Haka taro ya tashi kowa ya koma wajen aikinsa.
Tsaye Adebayo da Umar suke a jikin mota, gaba d'aya fuskar Adebayo ta canza kala daga fari zuwa ja, zuk'ar sigari kawai yake kamar wanda zai hadi'ye bakinsa saboda b'acin rai.
Dafashi Umar yayi cikin harshen hausa yake fad'in haba abokina kadena damun kanka akan wannan abun, kada kamanta an kawo wad'an da suka fishi tsanani ma amma cikin ruwan sanyi manyan k'asar suka sa aka canza masu wajen aiki, kasan dai wajen aikin mu babba ne, duk wani maiji da kud'i bazai so ace an kawo wanda zai rik'a bincikar kayansa ba, hakan yasa ba'a barin irin su Alhaji su dad'e anan, to ka kwantar da hankalin ka, babu wanda ya isa yazo ya kawo mana wani sabon tsari, yanda muka saba facaka da kud'i taya za'a zo lokaci guda akawo mana wani tsarin banza, kuyi magana da Alhaji Marusa koshi kad'ai ya isa yasa acanza masa wajen aiki.
K'arasa zuk'e sigarinshi yayi kafin ya fara magana cikin harshen turanci"Haba Omar kaima kasan hankalina bazai tab'a kwanciya ba matuk'ar wannan mutumin yana wajen nan, gobe ne kayan Alhaji Marusa zasu iso, kuma kaima kasan akwai abinda za'a sako aciki, gashi wannan Alhajin ya kawo wannan dokar, ya kake tunanin idan ya kama wani abu acikin kayan? Gaskiya akwai matsala, zan kira Alhaji na fad'a masa kada kayan nan su taho gobe, ya jira zuwa nan da kwana biyu kafin su taho.
Jinjina kai Umar yayi yana fad'in haka ne, kawai ka kirashi yanzu. Waya Adebayo ya ciro ya kira Alhaji Marusa, bayan ya d'aga Adebayo yace masa kada kayan nan su taho gobe. Alhaji Marusa yace yanzu nake da niyar kiran ka ai, d'azu muka gama magana da mutanan sunce cikin daren yau kayan zasu iso Lagos, kasan akwai kaya masu muhimmanci da tsada aciki, shiyasa nace zan kiraka naji ko Alhaji Mai Wada yasa hannu a wannan takardar? Adebayo yace akwai matsala fa Alhaji, komai ya b'aci, sabon tsari ya fito, wannan mutumin yazo da sabon tsari, yaki saka hannu a takardar, kuma yace dole a binciki kayan kowa, ina tsoron kada ace ya tsaya da dare idan ya samu labarin kaya zasu iso.
Cike da tashin hankali Alhaji Marusa yace mene? Haba Adebayo, ya zakayi mani haka, kai da nace kayi kok'ari cikin dabara ka shawo mani kansa sai ka fad'a mani bai amince ba, yanzu gashi kaya sun taho, dole nasan abunyi. Umar ne ya amshi wayar yana fad'in Alhaji kawai kayi waya daga can sama kasa ayi kiranshi da dare, idan yaje sai su rik'eshi da magana har kayan su iso idan yaso sai acire abinda ya kamata abar sauran zuwa safiya idan yazo sai yasa hannu a amshi kayan.
Shiru Alhaji Marusa yayi kafin yace maganar ka abun dubawa ce, ka kyaleshi bai isa ya sani cikin tashin hankali ba, zanyi magana da Mr. Kallah.
Kashe wayar yayi yana fad'in ai na fad'a maka Alhaji Marusa bazai bari yayi asara ba. Ajiyar zuciya Adebayo yayi yana fad'in dole ma mutumin nan ya bar wajen nan.
***
Bayan sallar magriba Alhaji Mai Wada ya samu sakon kayan Alhaji Marusa da suka taso. Bayan ya gama aikinsa saiga waya daga Mr. kallah akan yana nemansa k'arfe tara na dare. Cike da girmamawa Alhaji yace zai zo. Yana aje wayar yayi murmushi, tabbas hasashensa yayi dai-dai, dama irin wannan ranar yake jira. Dirowa ya jawo ya d'auko wani abu ya tashi yabar ofis d'in aranshi yana fad'in zanyi maganin ku.