*WANI YANKI NE CAN WAJEN AGADEZ CIKIN JAMHURIYAR NIGER mai sunna TIMIYA*, inda buzaye ne ke rayuwa a garin indai ka ga bakuwar fata to lale bako ne ya zo kuma juyawa zai yi ,
A kauyen nan basu da ruwan pampo sai fan take, wuta bata kai can ba ,
Gari ne mai tarin ni.ima , albarkar noma garake , sannan mota bata shiga domin can cikin sahara ne sai dai a hau rakumi a samu a shiga cikin Timiya
Yan mata ne laye su hudu,
Cikin ukun nan kowace ta kala tamkar ka lasheta dan kyau da daukan hankali sun sha digo digonsu na buzaye da katanga , sai daya a gefensu wace kanta ke sade kasa jikinta na dan rawa rawa hanayenta kawai ake ganni bakin kirin da yafen mayafinta na turkudi (tufafin buzaye )
Shigowa wani datijo ya yi yana dan dukawa dan tsayi ne da shi, da hannunsa yake yiwa mutanen dake bayansa nuni da su shigo domin bashida hausar kirki a bakinsa
Yana dago kansa ya hangota a cikinsu, ya juyo da dan sauri ya ga mazan nan har sun zauna
Rai bace ya nufi dakinsu wajen uwar yaran wato matarsa yana zuwa ya daga hannunsa ya dungurewa yar datijuwar kai ransa bace cikin yaren buzanci ya ce" ban hane ki turo min da wannan bakar yar taki ba? Na aurar da yaya hudu saura uku na cire wannan bakar a yayana, na sha fada maki ni a danginmu ba baki aman kika tashi kika haifo min baka? Na yi na yi ki fada min gaskiyar waye ubanta kin ce ni? Kuma dan bakin ciki an samu elhazawa masu son auren yaren kin tunkudo (turo) mini da ita ko?
Bata ce komai ba sai sada kai da ta yi, har ya gama babatunsa ya juya
Yana komawa ya damki hannunta ya jata kiiiii suna shiga ya hankadata ta tafi tagataga ta duke nan kusa da gadon karagar mahaifiyarta kanta sade, ya aibatata sosai kafin ya juya ya koma wajen bakinsa
Kanta sade hawaye ya ziraro mata, ta dago a hankali ta kali mahaifiyarta da idannuwanta ke rufe ruf tana jin yanda zuciyarta ke suya
Murya a raunane ta ce" *ANNA* (wato mama)
Bata bude idannuwanta ba, bata amsata ba
Ta dan jima a haka kafin take mikewa ta dage rufar da ta yi tana kallon mahaifiyarta da wani irin yannayi, a gaskiya a jikin wannan matashiyar budurwa banda idannuwanta ba wani abu mai hasken fari domin kuwa tana da baki ga kuma tufafinta mai rinar da fata ne wato turkudi
Mamanta ta dago ta bude ido a karo na farko, murya shake cikin yaren buzanci ta ce" kal ki ce komi, ki yi hakuri kawai
A hankali ta juya dan ruwa gidan baba tsoho....
Ku biyo ni garina, *TIMIYA* domin a Niger nake.... ......taku har kulun YAR MUTAN NIGERSAJIDA
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
2⃣
A hankali take tafiya tana dan rabewa, da ta hango gugun yara sai ta labe har sai sun fice idan kuwa wasa ne suke dole sai dai ta canza hanya domin irin wulakancin da mahaifinta da wasu a cikin yan uwanta ya sanya har jama.ar garin ke wulakantata suma suna dubanta daban cikinsu....
A hankali ta karyo kwanar runfar baba tsoho
Sanda take dan karasawa domin bata son haduwa da almajiransa tun bama Ali ba wanda ya so hada shi da ita ya ci mata mutunci yayi mata kwakwaran kashedi na koda wasa kar ta yarda ta nuna tana son sa domin shi dama ya shigo garin Timiya ne dan ya samu buzuwa fara ya aura..to tun daga lokacin sauran almajiran ke tsokanarta suna fadin ta Aliyu *BAK'A*
zaune yake cikin bukarsa, rawani ne a fuskarsa kwaurin hannun sa da na kafarsa ake gani , hakan zai nuna maka tsohon mutun ne, domin fatarsa du ta yi yaba haka gashin dake kwaurinsa du sun yi fari sol sol da su
Waje daya kawai yake kallo, a zuciyarsa kuwa ya afka tunanin yau ina ta yi? Ya aka yi bata zo ta dauki karatu da safe ba? Bata da kawa, bata da wani mai rabata a jikinsa, mahaifiyarta kanta bata mugun sake mata dan tana tsananin tsoron mijinta a kan yarinyar
Shi kam yana cike da zulunmin abinda ya sa bata zo ba
A hankali ta daga kasarin dakin ta yi masa salama
Murmushi ne ya subuce masa yana kallonta kafin ya amsa salamarta
karasawa ta yi tana dan tatare tataren dakin ta kai dubanta wajensa, cike da kaunar tsohon sannan idan tana tare da shi takan ji ta wani iri, bata jin tsoronsa sai soyayarsa, tsohon shi ne kawai mai yi mata murmushi a duniya,
Dan murmushi ta sakar masa ta ce" SOFO (wato tsoho)
Shima murmushin ya yi, ya dan nunota da yatsarsa,
Ta karasa ta duka kasa ta ce" ta gode (gaisuwa kennan)
Turkudin kanta ya shafa a hankali kafin ya ce" Alharasssss
Mikewa ta yi ta gama tatare masa dakin ta dauko tsintsiyar kabar da ta yi da kanta dan share dakins ta shashare ko.ina ta dan dage kasarin ta dauki tulun ruwansa ta fice
Murmushi ya yi, ya bi ta da kallo....a kasan zuciyarsa ya ayanna" Allah ya nuna min farin cikin ki kafin na koma gareshi
Tafe take da tulunta cikin nutsuwa, tana zuwa ta duka wajen diban ruwan , wani dan kewaye ne aka yi shi ba rijiya ba, shi ba teku ba shi dai ruwan ana jayo masu shi ne, sannan kalar ruwan jajajir ne sai kanshin laka , akoy ruwa masu kyau sai dai idan ta yarda ta je wajen sai dai ta dawo ba ruwan ba tulun domin du yawancin yan matan garin can suke zuwa dibo ruwa su kuwa sun ki jinnin ganninta a wajen
Sai da ta cika tulun ta mike ta gyara bakin zaninta da kyau ta daga ta dora saman kanta
Yanda ta bar shi zaune haka ta dawo ta tarar da shi
Ta nemi wajen Tulun ta ajiye tana dubansa cikin yaren buzanci ta ce" baka gajiya da kallon waje guda?
Bai bata amsa ba sai mika mata allonta da yayi yana nuna mata wajen zama
A hankali ta zauna ya ci gaba da koya mata karatu wanda sosai ta nisa kuma shine malaminta tunda ta san shi
Suna gama karatun ya ce" menene tambayarki ta yau?
Ta yi tsai tana kallonsa, can ta nisa ta ce" sofo, shin mutun mai bakar fata laifi ya yi aka halice shi baki?
Da sauri ya kallota, ganni ya yi kanta a sade, tana faman murza hannayenta .....yarinyar akoy zurfin ciki sosai aman wani lokacin sai ta fadi dan abinda ke ranta domin tana gannin abubuwa masu firgitarwa a rayuwarta
Hannunsa ya daga, murya a sanyaye ya ce" ko daya mutun baki da fari du daya ne a wajen Allah
Dara daran fararan idannuwanta ta dago ta sauke kan nasa da sukai dan ja sannan du sun yi yaba irin na tsohon mutun, hawayen da ya taru a idannuwanta ta yi iya kokarinta ta mayar da su , daga haka bata kara komai ba, bata bari ta yu kuka ba ta mike tsam ta fice ba tare da ta kara kalma daya ba
Ajiyar zuciya ya sauke, yana tir da halayen Agali, Agali bashi da hankali da tunani, dan kawai Allah ya yi yarinya an haifeta bak'a cikin y'ayanka sai ta zama abin kyama abin kyankyami abin wulakantawa? Ita ta halici kanta ne?
Ta jima tana tafiya kafin ta karaso gidan iya mai siyar da nono
Har kasa ta duka tana gaisheta
Iya ta amsata kafin take cewa" kin ga nonon nan yana yi min wuya, ban san me yasa idan kin dauka cinikinki baya fice dala dari da ashirin .....sai dai ki maido mini shi haka du an motsa shi sannan in baki salama ni kam yau ki yi hakuri na sararma masu zuwa gida sara, kinga daman tausayin ki yake saka ni na baki dan ki samu dan kudin kashewa
Kanta a kasa ta ce" ki yi Hakuri iya, zan kara kaimi wajen siyarwan ki zuba min kadan yanda zan iya siyarwa
Kanta ta girgiza ta mike ta dauki kwarya ta zuba mata nono dan madaidaici ta mika mata, ita Allah yana ganni dan tana jin tausayin yarinyar ne aman tana da masu siyan nononta a hannu a hannu domin shannunta suna da yawa
Dauka ta yi ta fice a gidan, tana tafe tana jin wata irin juwa na daukanta, bata karya ba, bata ci komai ba sai yanzu ta tuna
Ajiyar zuciya ta sauke ta samu gu ta dan rakube ta daga kanta sama ta afka tunani
Mu je zuwa ci kin labarin *BAK'A CE*
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3⃣
Suna tafiya ya shigo dakin,
Yanda ya barta tunda ya dungure mata kai haka ya tarar da ita
Ransa bace ya nunota da yatsarsa ya ce" ke,
A hankali ta dago kanta ta sauke kansa tana kallon sa
Y.ayana biyu sun samu miji yan albarkana
Wani abu ta hadiye a makogwaronta, a hankali ta ce" wannan karon wa ka siyarwa yaran?
Da mamaki yake kallon ta, mayar masa da magana ne ta yi? Shi?
Da izgili ya karasa kusa da ita ya nunata ya ce" ke balagazar mace, ke har kin isa ki dube ni ki fda min cewar ni ina siyar da yara? A me kika dauke ni kennan? Matsiyaci? To bara na tuna maki a gidannan daidai da sansannin ( tabar buzaye) da zaki gumtsa sai kin taba tawa ba zaki iya siya ba dan bakya saye bakya saidawa zaune kike dabar ta.kar duwawu komai sai an yi maki,
To yaranna sun samu mazaje sun yi min kyakyawan tayi! Kuma na fada maki idan har na aurar da yaran nan gaba daya ki kuka da kanki ke da yarki dan kuwa ba zai yiwu ya kasance ina ciyar da yar da ban yarda cewa tawa bace bama
Har ya gama bata kara tofawa ba , ya juya ya fice a dakin
A hankali ta zauna kusa da mahaifiyarsu, itama farinta har daukan ido yake,
Hannunta ta kamo ta rike gam ta ce" zan so ki fada mana tarihinmu kafin muma mu tafi kamar su aunty a daina jin labarin mu, ba labari ba aike ba wani motsi.....Allah kadai ya san halin da suke ciki idan suna raye! Ba yace auren wata biyu kawai zan yi, idan na cika wata biyu na kwaso masa kudade na dawo ko ya sake ni ko bai sake ni ba sarki zai hana shi shigowa garin ........ ki daure ki fada mana tarihin rayuwarmu Anna (mama)
Su waye mu?
Ina ne asalin asalin mu?
Su waye dangin mu?
Bamu da kowa ne sai mu da ku?
Idan muna da mai ya sa ba wanda ya taba zuwa inda muke? Ina son sani ANNA
Jajayen idannuwanta ta sauke kan *Gaishat*, wai ita nan mai damar ce domin ita bata hantarar Bak'A, sannan tana kamanta bin iyayen su ba kamar sauran ba
Kwace hannunta ta yi ta hade rai ta yi mata nuni da kofa
Ta san kan zancen dan haka ta mike ta fice daga dakin
Kallonta yake tunda ya kirayeta ta zo turakarsa tana zuwa ta tube du wani abin da sunnansa sutura a jikinta, ta tsaya masa a gabansa wato gashi ka yi ka gama na koma
Kansa ya girgiza kafin yake tsareta da idonsa, ya juyar da kansa ya kuma kallota
Can ya ce" Nadia, haka zamu yi ta rayuwa? Ke ba zaki taba saukowa ki bani kulawar da nake bukata ba?
Saurin zubewa ta yi kasa ta ce" ka yi hakuri Uban gidana, ban san zan bata ranka ba kar ka hada ni da Ba (Aba)
Idannuwansa ya lumshe, a gaskiya Allah ya jarabe shi da matsanancin son yarinyar,
Yarinyar ce ko a cikin bugaje (buzaye) ta fita daban, ta hadu iya haduwa ko ba wanka Nadia mai kyau ce, dalilin haka ya amshi tayin aurenta da Ba dinta ya yi masa bisa sharudan kawar da ido da toshe kunnuwa kan karansa da za.a kawo a cikin garin kan yanda yana tafiyar da rayuwar gidansa, aman ya kasa samun nutsuwa da ita........ya kasance komai zatai masa tana yi ne dan tsoro ba dan soyaya ba
A hankali ya dagota ya jata zuwa ainahin turakar domin yanda yake kwakwarta shi kansa mamaki yake, yanzu dai shekara biyar da aurensu bayanta ma ya kara auren mace biyu ya saki gudar aman har yanzu ta kasa fice masa a rai a kulun yana mai jin zumudin kasancewa da ita.....aman ita ta kasa kontar da hankalinta ko dan matsayinsa na sarkin garin ta murza mulkinta aa tana rabe rabe ne a gidan mijinta
Nadia kennan babar yar *BA*
Ke kin san nawa ne million daya? Jika dari dari har goma fa, an ce Gaishat har million goma sha hudu mutumin ya bada kudin aurenta,
Ke ki rufe min bakin ki, ke fa haka birge ki yake ko? Kina ganni yanda yake aurar da yayan nasa daga sun tafi shikennan ba labari, kudin ya zo bai yi masa anfannin komai ba, daga an kwana biyu ya kashe sai kuma ya fara harin wata a cikin y'ayan nasa, ai sun kusa karewa zamu ga kuma idan wada ya tsanar zai yi shelar ya siyar
Mahaifiyarsu da ta shigo da Buzu (salaya) a hannunta ta kale su ta ce" ke Amina, ki tashi maza ku je ku yi sallah, wannan maganar kun cika yinta bayan kun san ya zama abin gasa a garin nan, sai kun jaza min abinda ya fi karfina ko? Kuma da hakan bata faruwa da ku dan Ba din ku bai yarda da hakan ba, ku kun fi kowa sanni gidajen da basa haka basu fi a kirga a garinnan ba aman zaku zauna mamakin kwaya daya? Kowa ya yi da kyau kai nasa! Ku mike ku bace min a wajen nan kar ku yarda maganar nan naku ta yi tsayi ya zo ya tsige mu baki daya domin ku kun san waye shi !
Sumui sumui suka fice dan zuwa yin alwallah su gabatar da sallah
Sai yama sosai ta kamo hanyar gida,
Tana tafe ne tana dan jin dadin yannayin garin domin sanyin yama ya fara busawa sosai ita kuwa gwanar son sanyi ce sosai
Ba ita ta kai gidan iya mai nono ba sai kusan magariba, ta kai mata cinikin inda iyar ta bata dala ashirin da biyar ta yi godiya ta mike
Har ta kusa fita iya ta kirayeta ta dawo
Ta ce" kin ga , ga abinci nan ki dauka ki ci mana ni na ci na rage, sauran ki yi min halin naki sai na tabatar kina kyankyamina ne na san irin matakin da zan dauka
Fanata ce ta fito daga daki, kmar kulun cikin mahaukacin gayu mai gigitar da jama.ar garin ....Fanata dai y'a ce a wajen yar uwar iya wace ke aure a cikin garin agadez, mahaifin fanata Babarbare ne shi ya sa sunnanta ya fita daban ,
A da fannata ta kasance ita ba fara kar ba ita ba baka ba duda mahaifiyarta farar buzuwa ce,
Aman kasancewarta a can cikin birni, da taraya da kawaye ya saka take shafa mai wanda ya mugun karbarta ta yi fari kar kar kar harma ta fi maman nata farin,
Fannata akoy kyau ga iya daukan wanka
Tana son garin timiya a rayuwarta domin gari ne mai cike da ni.ima
Tunda ta fito take kallonta da mamaki,
Dubanta ta mayar wajen Iya ta ce" iya, yarinyar nan mai maki tallah ce ta girma haka?
Iya ta ce" eh ita dai ce
Fannata ta yatsina fuska ta ce" to aman har yanzu sunnan da ake kiran nata da shi ne? Wato *BAK'A*?
iya ta amsata da kai
Fannata ta kallo wajenta ta kuma kallon iya ta ce" menene sunnanta na gaskiya ne ita wai?
Iya ta kalli Bak'a, ta kalli Fannata, ta ce" sunnan Hajia ne da ita, karfi da yaji Ba dinta ya mayar da sunnanta Bak'a har ake mata kiranye da haka
Da mamaki Fannata ta karasa kusa da ita tana kallonta,
Yarinyar fa nata wani tsararan kyau, boyeyen kyau, duda mugun bakinta ga bakin turkudi na bugajen kauye🙈🤣, ga dati da take fama da shi, aman ita tana hango wani al.amari a tatare da yarinyar, to aman me zai hana ta shafa mai itama? A sanninta ba bakon lamari bane buzu farinma ya shafa mai, kai ba buzu ba yanzu abin ya zama larabawama mai suke karawa shi yasa zaka gan su wani farfarfar da su sunna daukan ido, ba sai dan duniya ke shafa mai a duniyarmu ba, mun dauki mai mun mayar da shi abin kmgyaran fata, ra.ayi ne shafa shi idan ka shafa ba mai yi maka kallon dan duniya a karkarar mu
Abimcinta take ci kanta a sade tana ji yanda Fannata ke aikin tambaya a kanta, tsoro take kar a je mugun kyankyaminta kamar yanda mutanen garin ke yi ya saka take son sannin ko ita wacece dan ta kara samun damar ci mata mutunci, hakan ya sa take sauri dan ta gama cin abincinta ta kara gaba , so take ta siyarwa SOFO goro na dala biyar, ta saka dala goma asusun da take tarawa dan ta bawa Ba ko ya daina tsanarta, Gomar kuwa itama ta ci wani abin
*AGAISHAT*
ta ji sunnanta a sama sama yana yawo, sunnanta na gaskiya aka kiraya,
Da dan sauri ta dago sukai ido hudu da Fannata,
Fannata ce ta kirayi sunnanta na ainahi ba bak'a ba.............
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
4⃣
A hankali ta kai idannuwanta kan Fannata dake kara matsowa kusa da ita
A hankali fannata ta saka hannunta ta dago na Agaishat, kallon hannun take tana jujuyawa, fannata ta fahimci bayan bakinta na halitarta da Allah ya yi, akoy tarin dati ga kuma karin bakin turkudi,
Da sauri Ta janye hannunta tana kokarin mikewa daga cin abincin cike da tsoron menene kuma Fannata ke taba mata hannu?
Fannata ta ce" kin ga, ba abinda zan maki
Kallonta take da mamaki domin da hausa radau Fannata ta yi magana bayan Agaishat kadan kadan take jin hausar itama baba Tsoho ke dan koya mata dan abinda ya iya, yakan ce ba.a san gobe me zatai ba
Goshinta ta dafe ta kalli wajen iya ta ga sai faman gyara Sansanninta take(tabar buzaye), tana dan kukulewa da zare tana ajiyewa gefe tana yin kulin kadago kadago (dala biyar biyar )
Kurumci Fannata ta shiga yiwa Agaishat,
Ta yi mata nuni da hannayenta da fuskarta gaba daya,
Ta yi saurin taba ruwa ta nuna mata alamar bata wanka ne?
Agaishat ta shiga faman saka tsohon takalminta na soso tana faman guduwa domin ta saka a kasan zuciyarta wannan abin zai kare ne a wulakanci da tozarci
*WaRDUGU*
Ta fada tana mai daga murya kamar zata kaiwa gabjejen mutumin dake tsaye a gabanta duka,
Ta kuma cewa" WaRDUGU Odon jidu anna indahan yuna yugusnan gwa ( tun kana yaro yake fama da kai)
Kansa ya dafe, ya kai dubansa kan agogon hannunsa, kallota ya yi ya yatsina fuska, can ya ce "Ayya (wato mama), Ayya inda medi mundu tam (wato mama ke rigimarki ta yi maki yawa)
Hannunta ta dora a goshinta ta shiga kai kawo, kai take tana kawowa, can ta dauki wani ihu ihu tamkar tana buda, ta je ta dawo ta je ta dawo, ta kallo shi cikin yaren hausarta da bata fita da kyau ta ce" shikennan rayuwar bariki (gayu) ta lalata min kai, shikennan na zama uwar da ina fadi ba.a saurarena, ko nima zaka kula zazafar gabar da ni ne kamar yanda ka kula da Abbanka (mahaifi)?
Hannayensa ya jimke ya daki garu da su, kafin yake juyowa wajen mahaifiyarsa,
Taku ya yi zuwa gabanta kafin yake sada kansa, shima cikin yaren hausar sai dai tashi ta fi dan goguwa ya ce" Ayya ba dai saboda wajen wannan bugudin (tsofo) ne kike daga hankalinki harda hada kanki kike min da wannan Bugudin (wato mahaifinsa)?
Kanta ta kawar ta ki bashi amsa hakan ya sa ya mike ya fito daga falon
Yana fitowa ya nufi wani dankareran mashin *ROUTIER* jibga jigban nan masu shegen tsada domin daga million daya abinda ya kai har million shida ne, kuma mashin ne ba mota ba...gudunsu ma daban yake da kananun mashin
Bakin gilas dinsa ya fitar ya saka ya tayar da mashin din ya yi masa wani irin ja wanda kana ganni tamkar dambe ake da mai jan da mashin din domin mugun karfi ne da shi ga kyau
Hangame gate mai gadi yayi don kar ya jawa kansa bali wajen Wardugu
Yana fitowa daga anguwa *Plateau* a birnin Niamey ya nufi *Francophoni* inda gidansa yake
Yana karasawa shima tuni an hangame kofar ya shige da gudun tsiya ya silala wani waje da nan ne ma.ajiyar abinda ya shafi mashin da motoci
Dira yayi ya juya da sauri sauri ya shiga hawa matatakalar bangarensa domin bangare daban daban ne da matarsa mai sunna *GALayn*
Wata yar karamar carte ce ya dora mai dauke da hotonsa ya dora daidai wani detecteur ya bada dan kara titeeee kofar ta bude
Caicaicaicaicaicaicai wash, gidan tubawa kamshi, wayo gidan batube ni.ima, bale mai auren gimbiya hajiar hajia, sarkin tsafta, sarkin ado, kwaliya ba dai a nuna mata ba, ta kasance cikin kamshi wanda indai kai ka ce zaka kwaikwaya sai dai ka tashi da mura (gaisuwa yar baba)
Sanyi mai hade da kamshi ne ya buso shi, sanyi mai sanyaya zuciya
Terrace din dakin fara kal kal kal haka take daukan ido ta sha guga,
Tafka tafkan salon ( kujeru) ne irin na zamani masu kalar fari kal kal sai dan coussin kananuwa sosai su kuwa masu kalar baki kamar yanda mauquette (capet)
Rido (wato labulaye) yen dakin suma kalar fari ne, sai dai farin ba kar ba kamar yanda kujerun suke , shi ya fi ruwa da kalar peinture (colern) dakin, shima an saka abinnan na daure labule baki wanda kana ganninsa ka san ba karamin kudi bane dakin ba wani tarkace aman komai ka kai dubanka ka san karshe ne sannan ya bada kala ta mamaki,
Nan ya yada zango, ya daga kansa sama ,
Iska ya furzar yana jin yanda takalmin matarsa ke tahowa kwaskwaskwaskwas
Kamshin da take fitarwa shima na daban ne, ta shafa turaruka har ta gaji,
Tunda ta fito take kallon yannayin fuskarsa, a cikin ranta ta ayanna" wani masifafe kuma ya hargitsa min yannayin miji?
Bata yi kasa da gwuiwa ba ta karaso kusa da shi ta daga damatsunnan hannayensa ta shiga masaging a hankali tana kara kallon yannayinsa
Murya can kasa ya ce" *ADIBIRA* (Matata)
Tsai ta yi tana kallonsa kafin ta ce" qu'est-ce qui ne va pas mon Bb? (Me ke faruwa Baby?)
Kansa ya kawar gefe kafin ya janye hannunta a hankali ya mike ya nufi uwar dakansa
Bakinta ta tabe, Galayn akoy saurin fushi, mace ce iya mace aman bata tunnanin zata tsaya tana wani bibiyar namiji ko waye shi balatanna wardugu? Wardugu zuma ne ga zaki ga halbi, wardugu ko a cikin tubawa tsoronsa ake, mutumin da idan ransa ya baci idan bai samu ya damki mutun ba yake suma? Mutumin da ya wawuri ogansa ya daga sama ya nana da kasa ogan nasa bama na niger ba domin a niger ba marichal, bako ne da kowa ke tsoro yana shayi, gardama kadan ta hada su General Wardugu ya daga shi ya nana shi kasa a gaban yaransa da kuma yaran general, wannan abin ya jaza masa da mukaminsa da komai shugaban kasa ya tsaya kai da fata aka tura shi daji can wajen mali sai da ya yi wata hudu ya sauko, aman maimakun abin ya yi sauki sai kara gaba da yayi, mutumin dake gaba tukura da mahaifinsa , fada yayi gwa da gwa cewa abansa ya kiyayi hanyarsa kan laifin da ya boyewa kansa sai shi sai mahaifiyarsa suka sani, ita a wa zata tsaya ta bi bayan wardugu da idan ransa a bace ka bashi hakuri yake hucewa kanka? Du irin yanda yake ikirarin shi yanzu ba ruwansa da fada da mutun na gugar jiki karya ne ! Ka yarda ka yi gigin kai masa wargin baya ce masa komai ya ciro daya daga cikin wukaken dake jikinsa ya burma maka idan ya so a kashe shi, Wardugu nada zuciya ta ainahin tubawa....
Mu je zuwa labarin *BAK'A CE*
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
5⃣
Mikewa Galyn ta yi ta fice itama ta bi ta babar kofar danma ya san ta yi tafiyarta ta je ta kara bada turaren ruwa a jikinta ta fito ta je wajen da kys din motoci suke ta dauki guda ba tare da ta tsaya zabe ba domin kuwa kaf ciki manya ne
Tana fitowa ta shige motar ta tayar ta fice abinta wajen auren kanwar kawarta tana mai duba carte dinta ta bank dan ta tsaya ta ciro yayan banki na kari a wajen wasa....
Wannan kennan
Ya yi kai kawo ya fi a kirga, ya dafe kansa yana tunanin irin nacin mamansa kan abu, ita yanzu dan wani tsoho can daban zata dame shi kan sai ya kaita, shi ya san wani bai isa ya bashi lafiya ba aman har fadi take shi ya taimake shi yana yaro, an dai dudura masa itatuwa haka kawai za.a kashe masa kwayoyin jiki
Tsaki ya ja mai karfi, ya mike ya shiga cire kayan jikinsa masu nauyi ya rage masa culotte kawai
Da dan gudugudu yake kara taka matatakalar benen bangarensa har ya karasa bangaren da piscine dinsa take
Ba tare da wani tsaye tsaye ba ya fada cikin ruwan nan ya shiga iyo tamkar wani kifi yana kai yana kawowa ba wani alamun gajiyawa a tatare da shi
Ba ita ta kai gidansu ba sai can dare har wajen karfe tara abinka da jeji shiru garin sai kukan tsuntsaye sai jefi jefin samari da yan mata ana tadi domin sukan kai har goma suna tadinsu
A hankali ta shige gidan nasu ta samu ta leka kanta
Fitilar kwai a kunne, sai dai tana jiyo minsharin Abansu dan haka a hankali ta kutsa ta nufi dakinsu yan matan gidan
Mahaifiyarta ta gani zaune saman abin sallah, da alama ita take jira duba da irin yanda ta tsareta da ido
Jiki a sanyaye ta karasa kusa da ita kanta duke ta ce" ANNA
Bata amsata ba sai kureta da ta yi da kallo,
Ta jima duken nan, aman bata mike ba domin ta san wani abu guda da mahaifiyarta keda na buzaye tamkar wata yar gidan sarauta koda yake du buzuwa ko buzu haka ne dadaya ne basu da shi wanda mutane ke jifansu da sun cika *Ashak* ,
Can kamar ba zatai magana ba ta ce" kin ga, ko wani hali zaki shiga, ko wace rayuwa zaki fuskanta *AGAISHAT*, ki guji sabawa mahalicin ki, ki rike mutuncin ki , ki ci gaba da hakuri watarana sai labari
Kanta take gyadawa, kuma wani dadi ta ji har cikin ranta, ko ba komai ta san a duniya bayan baba Sofo Annartama bata kyamatarta, tana kawar da kai a lamuranta ne dan gudun fitina, irin yanda Abanta ke binta da shari kwararo kwararo ya sa mutanen garima haka, ba mai kulata da daraja, ko magana za.ai mata ba.a mata ita a mutunce, ya kasance ko gaishe da mutun ta yo sai ya yi mata yatsina domin Abanta bai barta haka ba har shari ya yiwa annarta kan cewa ko dai wajen baba Sofo take zagayawa gannin irin yanda ya damu da ita ?
Wannan wutar kafin ta mutu sai da aka sha tashin hankali, baba tsoho ya yi kuka sosai aman bai daina kula Bak'a ba domin tana da mutunci yarinyar, shi Allah bai azurtashi da yin auren bama domin bashi da lafia ko ya yi ba anfani hakan ya sa yake jin yarinyar tamkar yar da ya haifa, itama tana mutunta shi tamkar mahaifinta
Mamanta na gama fadar haka ta yi shiru kanta itana a saden tamkar tana gaban sarakuwarta
A hankali ta mike ta nufi dakin su
Tana zuwa ta tarar du sun yi baci abinsu dan haka ta dauro alwallah ta shige ciki ta tayar da sallah ta shiga ramuwar wa.inda batai ba , tana so du rintsi ta ringa samun gurin sallah sai dai tana tsoron mutane da kwagirar su, yanzu za.a wulakantata dan haka take bari idan ta zi gida sai ta yi wanda bata samu ta yi ba
Tun karfe takwas na safe Aba ya fice bayan ya canza rawaninsa daga baki zuwa maroon turkudi sabo fil, ya sayi tufafi ya sayi rawanininka harda waya, ya fito sabo kudi sun fado shikennan a haka zai fada su tamkar wuta shima ya dankaro aure daga an cinye kudin shikennan ta gudu abinta
Bai jima sosai a wajen ba ya dawo,
Daidai lokacin Anna na fitar da dawar masararsa a ruwa wace ra jika dan tana son yin garin tuwo
Bai yi mata magana ba ya zarce dakinta dake baban daki idan ka cire nasa a gidan, daman dakuna uku ne, da nasa da na Anna da na yan matan gidan
Bai yi wata wata ba ya shiga kwasar kayanta yana kaiwa dakin yan matan yana jibgewa gefe guda,
Ba wanda ya tanka shi ko ya yi mamakin lamarinsa domin sun san halinsa, haka yake du idan zai yi aure dakin mahaifiyar su yake fitar da ita ya hadeta da su ya kawo amarya, bama zai barta a dakinta ba sai dai ya hade su ya kawo amarya su sha shagalinsu ba wanda ya isa ya yi magana yanzu zai cici masa uwa ko waye
Ko kallo bai isheta ba, don ta daukarwa kanta alkawarin in dai ba mutunci ne lamarinsa toh ba zatana kai kanta yana wulakantata ba gaban yayanta.
Sai da ya gama fitar da komai kafin yake fita ya shigo da magini
Sosai aka gyara dakin ya yi tas da shi
Tare suka fita , sun jima sosai kAfin yake dawowa
Wannan karon kuwa masu shigo da kaya ne
Mariama dake wanke fuskarta bayan ta shafa kurkum ta yi tsai tana bin kayan da kallo,
A gaskiya siyayar idan ka yita a kauyen ka isa ne, tun daga gado har kayan abinci na gayu ya kwaso abinsa sai dai abin haushin babu rabonsu a ciki na amarya ne, domin idan ka auri jar buzuwa ko duniya zaka kai gidansu nasu ne ba za.ai mata komai ba sai dai a kawo maka ita daga ita sai butarta (a kauye fa kar a ce inji sajida🤣)
Sai da suka gama kawo kayan tsaf Mariama ta je faban mahaifinta ta tsaya masa kerere a gabansa, somin kuwa in dai haihuwar rashin mutunci ne ya haifa Mariama ta isa ta iya tsayaya tamkar mahaifinta
Ido tar cikin nasa da yaran buzanci ta ce" Aba ya haka? Na ga ka fara kwaso kaya alamun aure zaka yi? Ya baka fitar da mu ba? Baka ba anna kudin siyayar kayanmu ba?
Kun san wasu iyayen sun fi son yaya masu tsayayar nan, domin Aba yana dan shayin lamarin yar tasa domin a yanda yake gani tama fi shi rashin mutunci dan haka ya dan gyara rawaninsa irin zai yi magana ya ce" wani siyaya kuma? A sanina cikakiyar buzuwa ba.a yi mata kayan daki?
Ta yatsina bakinta ta ce" sai kuma cikakiyar buzuwa ana yi mata sutura
Karya ne Mariama, ya fada yana matsowa kamar zai doke ta, ya ce" ku ne yayan zamani kuke zuwar mana da abubuwan da suke neman fin karfin tunanin mu, ko uwarki haka aka bani ita, haka ake kai ku daga ku sai turkudin amarci da buta, kudin auren ku kuwa mu iyayen ku ke siyan maku kadara mu ajiye maku a nan wanda idan kun waiwaya zaku ji dadin su
Wani malalacin murmushi ta saki tana kallonsa
Ya ci gaba da fadin" ke da kin ga minister ne ya turo a nemi aurenki, ya saya maki komai, sannan ke da auren wata shida ne zaki yi ki kwashe komai ki dawo mini mu more da kudi?
Tar ta kara saka idannuwanta cikin nasa kafib take juyowa ta ga mahaifiyarta ta fara daka dawar da ta wanke ta baza a rana ta sha iska tana so ta mayar da ita gari kennan , ta kuma kai dubanta wajen yayarta *BAK'A* dake ta dirzar wankin yan matan gidan harda na su kanenta ita dai burinta idan sun tashi su bata konce, ta kuma kallon mahaifinta dake kokarin shi dole sai ya yi mata wayo, wai wani harda cewa wai ya siyar masu kadara, shi? Kudin aurwnsu bai taba wata a hannunsa ba komin yawansu zai kashe su ne ya dawo talakansa marar mutunci, yan yatsunta biyu ta hade ta yi tap tap da su suka bada dan sauti kafin ta ce" ka kirga kudi, ina so ka bawa Anna kudi har million shida a cikin kudin da ka karba na auren mu domin na sani cinikinmu kake tamkar abin siyarwa baka amsan kasa da goma, ka bamu shida mu je birni tare da Anna mu siyo kaya mu dawo idan baka yi haka ba zan shiga duniya na saka ka a matsala kai da wanda ya kawo kudin aurena, ka san ni horonka ce
Yana tsaye bami bude har ta fice a gidan, kallonsa ya dawo wajen Anna, da sauri ya karaso ya ce" kina jinta kika yi tamkar baki gani bayan kin san tana jin nauyin zuciyarki? Ko ke kika kitsa mata a taru a cuce ni? Har million shida? Ai kudin sun kusa karewa idan na baku haka!
Bata bashi amsa ba ta ci gaba da dakanta , nan ya juya wajen Agaishat ya ga shi take kallo
Ke dan ubanki daina kallona da wasu tula tulan idannuwanki masu kama da na mayu, shegiya da aka kwaso cikin ki a waje aka yayaba min, dan bakin jini ko almajiri na yiwa tayi guduwa yake, zan zo in kwakwale miki idannuwan nan in baki a hannayen ki ki je ki kaiwa tsohon dan iskan nan da kike zuwa kina wuni wajen shi wama ya san ko me yake maki a bukar nan
Da sauri Annan ta juyo wajen shi, ta kai dubanta wajen Agaishat da ta sada kanta jikinta na bari, tausayin yarinyar ya kara dirar mata, nan ta kara gane shi ya sa idan ta fice take cika dare dan kar ta hadu da mutumin dake mahaifinta aman ya zamo makiyinta , ta rasa da wata kalma zata kirayi mutumin dake miji a gareta, ta san ya yi karatu, sai dai son kudinsa ya fi imaninsa yawa
A hankali ta ce" ki je kawai zan idasa maki aikin
Da sauri ta ajiye wankin ta warware mayafinta na bakin turkudi butubutu da shi ta yane jikinta gaba daya ta fice har tana hardewa tana waiwayen gidan nasa
Bakin wata bishiyar mangwaro ta zauna ta fashe da wani matsanancin kuka mai karfin gaske
Ku mu je a labarin Bak'a ce na sajida
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
6⃣
Kuka take tana murza goshinta a kan cinyarta dake lulube da turkudi, hawayen nan ya jika turkudin ya yayakune sannan ya gogun mata a fuska ya kara rinar da fuskar ya kasance wani waje ya fi wani wajen duhu sosai fuskar du ta yi jirwayi da ita
Sai da ta ci kukanta har kanta ya fara ciwo kafin take yin shiru, mangwaron nan ta kuma kallo gannin du ya yi jajajir ya nuna ya saka ta mike ta gyara zaninta da kyau ta kama kokarin hawa ,
Da kyar ta hau bakibakin ta kamo wa.inda ke kusa ta tsintsinka ta diro ta zauna nan tana gogewa da hannunta sai kuma ta sha abinta, yau bama zata iya zuwa wajen tsoho ba ta san yana da ruwa goronsa kuwa ta kai masa gobe sai ta yi safiya ta je wajen shi
Wardugu, yanzu yanzu?
Kansa ya dafe ya ce" Ayya ko kin fasa tafiyar ne?
Da sauri ta mike ta nufi dakinta tana dafe kanta, yaron nan akoy kagauta , bashi da hakuri yanzu in ba rigima ba a kai tsayen nan ya zo yace su yi tafiyar da a yanda ake bata labari garin can cikin jeji ne? Aman ba komai irin yanda take mafarkin mutumin nan abin ya tsaye mata a rai, tana tune sun yi da shi idan yaro ya samu lafiya sai ta bashi salama da abinda ya sawaka sai dai ta zo tana yiwa Wardugu magani da magungunnan aka tashe su daga garin aka maido su Capital tun daga shi bata kara ganninsa ba domin ta neme shi sosai, sai kwanan nan take jin lanarin yanzu tsufa ya kama shi sosai baya yawo yana garinsa na haihuwa harma an fada mata sunnan garin , tana son sauke nauyi domin kuwa tun daga kan maganin wajensa Allah ya aminta wardugu bai kuma Huka ba sai tana gannin haki ne ta je ta sauke ba wanda ya san gawar fari
Nade ta fito da lifaya mai ruwan ja da kyalkyalin zaiba, lifayar sai baza kanshi take , Ayya ta kwana biyu a duniya aman karshe ce, akoy iya ado da sannin hakin turare, idan ka ganta sai ta birge ka gata da saka zinare tamkar ba da kudi take siya ba, danta ya bata damar murza mulkin da ta ga dama
Tafiyar manya ba.a kwasan tufafi, mai aikinta baturiya ce ta fito da wata yar valise (yar akwati) yar karama wace a ciki ta saka du wani abin bukatarta ta nufi kofa dan kaiwa cikin mota
Gaba ya yi yana amsa waya da aminiyarsa, kawarsa, wace du duniya itace babar kawarsa sai wa.inda ba za.a rasa ba, itace basa fada, ta iya tafiyar da lamarinsa ta iya zama da shi , sannan du irin yanda ya ki jinnin jajayen buzaye ita wannan baya iya kyamatarta , ba.a shaifar mutun aman shi zai bigi kirji da halayen *ALHINAYETT*
Kana nufin yanzu yanzu? Bama zan yi maku bankwana ba?
Wardugu ya ce" Alhinayettt bafa wani jimawa zamu yi ba, ke dai ki yi mana adu.a
Yana fadin haka daidai yana zama cikin motar Hilux tamkar wani daki tana fa fadin waje,
Sai fa ya gama wayar ya dubo AYYA da ta tsura masa ido
Kallonta yake da alamar mamakin kallon domin irin kallon nan ne na tsare mutun idan ya yi karya
Bakinta ta dan turo ta ce" kuma ka ce ba budurwarka bace, mutunci ne bakwa wata soyaya da ita,
Murmushi ya yi do.in daman ya saka a ransa wannan ne, ya dan sasauto ya riko hannunta ya ce" Anna, aa, Alhinayett aminiyata ce, wace bani da amini ko aminiyar da ta kai ta
Yatsina fuska ta yi ta ce" karyar banza wai aminci mace da namiji ? Ai ba shi sai idan soyaya ake
Kawar da kansa ya yi ya ce" kin ce a lokacin da ya baki magungunnan da aka dura min ma tsofo ne, kuma har yanzu kina da tabacin yana raye? Ni din ma fa na jima a duniya
Murmushi ta saki ta mika hannayenta masu saye da zobunnan zinariya ta dankwashe masa kansa dan ta san yana so ta yi zuciya ne ita kuwa ba zata yi ba, halayensa tana gannin sai dai ta fada masa domin tun bai san kansa take tafe da shi ba
Sun Dauki hanyar airport dan zuwa garin Agadez daga nan kuma ya nemi abinda zai kai su garin da suka nufa
Mali yaro ne ke wasa a wajen auren kawar Walyn ,
Tunda ta shigo wajen wasan yake kofata da kiran General wande, Walyn kin fice yaro (Matar general),
Tunda ta nemi wajen da tana iya gannin kowa kowa na iya ganninta ta hakimce ta dauki kafa daya ta dora saman daya, ta karkace kadan ya kasance dankareriyar sarkarta ta zinari ta fito sosai, ta dora hannunta guda saman cinyarta awarwarayenta ma suka fito radau da su, takan dan saki dan murmushi hakoran makarta su bayanna, ta dan juya ta kuma juyar da kanta tana karewa mata da yan matan wajen kallo tana auna su daya bayan daya,
Kari ake masa na hauka aman hankalinsa du ya karkata kanta, ya sani ne udan ta zuge bakin wannan jakar nata mai shegen kyau sai ya yi kwasa, jakar a yashe take kusa da kafarta tamkar ba komai na anfani ciki bayan kuwa a cikinta kudane da dankara dankaran wayoyinta na kece raini
A haka har aka fito daga salar isha.i bata mike ta je ta yi sallar ba suna zaune sun zagaye mawakin da yakan silalewa ya bar yaransa da basu san ciwon kansu suma ba ya je ya gabatar da sallah ya dawo ya dora daga inda ya tsaya
Wannan dawowar da ya yi bai zame ko.ina ba sai gabanta domin ya lura yau yan mulkin ne, yan na isan ne, tana son nuna bambanci tsakaninta da sautan matan wajen,
Yana zuwa ya shiga kodata, yana waketa, yana wake jarumtar mijinta
Kanta ya fashe , ya yi gingirigin
Ai kuwa ta dauki jakar nan ta yage bakinta ta shiga zuba masa masu aku wato jika goma goma tana dangalar masa tana yi irin bata san ciwonsu ba sai da ta karar da jimki biyu wajen ya cika da ihu wata kawarta guda na daukanta vidio dan ta tura mata
A wannan rana an jima ana wasa wanda Walyn bata bar wajen wasan nan ba sai da aka gama sai da ta ga karyar ko wace yar karya kafin take mikewa ta dauki jakarta kawayenta masu mata fada suka biyo bayanta har sai da ta shige dankareriyar bakar motarta bayan ta wankesu suma da kudi ta tayar ta halba bakin titi a lokacin har karfe goma sha daya ta buga na dare
Garin niamey capital ta niger du wanda ya taba shigota ya san gari ne dake baje ta ko.ina da polisai
Basa wasa kame suke tun karfin su, in dai ka kuskura ka taka doka toh fa zasu damke ka ne ba sasauci
Tukinta take cikin nutsuwa,
Danja ce ta tsayar da ita bakin inda polisai shida ke tsaye suna duba takardun mota na mashin, da kuma takardar shedan kai wanene
Hankalinta konce take jira danja ta saki domin ta san sun san number motar general ko sun kurbi giyar bera ba zasu tunkareta ba koda kuwa ta taka dokar domin ta tsira tunda ta hau motar *DOKA* gabadaya
Kwonkwonkwon karar kwonkwasa motarta,
Da mamaki ta dubi wajen
Wani saurayin police ne fuskarsa daure tamau ba alamun wasa a tatare da shi
Da yannayin rashin mutunci ta sauke gilashin motar ta sauke masa idannuwanta masu nuni da baka da wayo
Shima fuska a daure ya ce" madame vous etes en état d'arrestation, veillez sortir calmement nous nous occuperont de la voiture (Madame mun kama ki ki fito cikin nutsuwa zamu kula da motar)
Da mamaki take yi masa kallon sakarai, baki bude ta nuno shi da yatsarta ta ce" kai aman kai sabo ne ko? Waye kai? Ka san ko wacece ni?
Sadowa ya yi sosai ya saka idannuwansa cikin nata ya ce" eh mun san ko ke wacece, umarnin mijinki ne in dai kika kai karfe bakwai a gari du wanda ya hadu da ke ya kai ki cel ki kwana da safe karfe goma a sake ki daidai gari ya cika kuma a rubuta a jarida!
Dum dum dum take jin maganar tamkar saukar aradu, quoi? (What), ita? A cel? Prison! Ita Walyn? Wardugu wardugu ta fada tun karfinta tana dukan sitiyarin motar ta .........
Ohk
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
7⃣
Ita Wardugu xai yiwa wannan wulakancin? Ta kwana a cikin kaso, batai sata batai komai ba? Dan kawai ta cika dare?
Wayarta ta warta a cikin jakarta ta shiga laluben numbersa wace ta sam zata same shi
Ta yi kira ya fi a kirga daidai lokacin polisawan sun zagayeta tamkar dai ta yi wani gagarumin laifi
Hanjaki kwonce ya daga domin lokacin yana hakimce kan gadon hotel din da ya sauka ita Ayya tana can gidan sarkin Agadez matarsa uwar gidan ce kawarta ta kusa sosai, shi kuwa ya ki sauka a nan ya je hotel , bayan ya gama harkar kasuwancinsa ne kiran Walyn ya shigo wayarsa, domin Wardugu na sana.a.o.i ya san dadin nema , yakan ce ba dole ya nema ba shi mai Ayya da Walyn
Murya irin ta yan duniya ya ce" adibinira (wato matata ) (readers kar ku manta a wannan nvel yare hudu ne, buzanci, tubanci, french da kuma hausa )
Murya ta sasauta tana tura hannunta cikin kannanuwan kitson da ta sha domin dai tubawa basa wasa da kitso ta ce" Haba mijina ya haka wannan tsatsauran hukuncin?
Murmushi ya yi jin yanda ta sasauto, kennan dai sai yanzu ta nufi gida ko? Muryarsa yanda take ya ce" hukuncin ya yi tsauri ne? Ko bai kai daidai da laifinki ba?
Idannuwanta ta lunshe tana jinsa har cikin ranta ta ce" matarka guda a prison? Ko laifi na yi ina tunanin na fi karfin nan sai dai ka hukunta ni a gida a dakin mu a saman gadon barcin mu ka rungumeni ka matseni ka haukatani da lamuranka , na san ina cika dare kuma baka so aman mutun ai ajizi ne, ka yi mini uzuri Wardugu
Murmushi mai sauti ya sakar mata, ya ce" bara dai mu gwada wannan idan ya so na dawo daga tafiar da baki tsaya kin ji ina zan je me zan je yi ba zamu yi magana
Fashe masa ta yi da kukan kisa , ta ci gaba da lalaba shi dan ya yarda ya yi masu magana su sakar mata hanya ta karasa gida dare na yi
Lumfashi ya sauke ya ce" ki bani daya daga cikin su
Cike da murna ta mikawa wanda ya fi kusa da ita tana zabga masa harara
Yana kara wayar ya kame yana sara masa tamkar yana gabansa
Murya a kausashe ya ce" wasu sutura ne a jikin matata?
Murya a ladafce ya ce" aa oga, mu mun isa mu kali matarka? Bamu kala ba bamu san irin suturar jikinta ba
A ransa ya ayana han, kafin yake cewa" idan ta ki ta fito ku zauna da ita a nan har safiya ta yi , har karfe goma sha biyu na rana kowa ya kasance ya ganta, sannan ku gayaci jarida ku bada cikaken labarin abinda ya faru, kar ku taba jikinta aman bata wahala, ka rike wayarta a hannunka sai goben ka bata! Sannan kar ku nuna mata wasa idan ta so kawo maku tsayaya ku tsoratata da bindiga
Da " a vos ordres ya amsa kafin yake katse layin ya saka a aljihun rigarsa
Wa ya ga zafi biyu 🤣
Karfe uku ne fa na dare aman ji kake gam gam gam ana dukan yar kofar gidan nasa
Da sauri *Tibillal* wato mahaifiyar su Agaishat mata a wajen *ALGABIT* mahaifin su Gaishat ta zabura ta kai dubanta wajen *AGAISHAT* dake zaune tsuru tun bugawar farko ta fara tana kallon kofar shigowar su
Mayafinta ta ja da kyau ta fito ta nufi dakin mijin nata
Tana zuwa ta tarar da shi a kwonce tamkar mai baci bayan ya farka ya yi tsuru daga kwoncen yana tsoron mikewa ma
Girgiza kafafuwansa ta fara ta ce" Algabit, Algabitt, ka tashi ana ta buga gidan nan
Hannunsa ya saka ya bige nata ya ce" naki na tashin, bayan a gari an san na amshi kudin auren yaranna , in na bude wani mugu ne fa? Koma waye ya yi hakurin safe mana aman a wannan tsofon daren? Ba zan bude ba!
Gannin ya tashi sai balbaleta yake da fadan da hujojinsa na karya ta mike ta nufi kofar wanda ya saka ya hantsilo ya rarumi wukarsa ya ja tunga yana fadin" kar ki bude mana, koma waye a daren nan ba bakon alkhairi bane!
Janye sakatar ta yi ta bude kofar,
Fado mata ta yi a jiki tana kuka, jikinta du sai rawa yake, ga sanyin garin aman wata yar ficiciyar riga ce a jikinta, mutumin da ya kawota a rakumi ne ya ce" na ga gidan zan dawo da safe a bani salamata!
Da tashin hankali Anna ta janyota cikin gidan tana ta kokarin kara dagota tana duba fuskarta dake da balshe ko.ina a tsannanin tashin hankali ta ce" *FATIMATA* fatimata , fatimata
Gaba daya mutanen gidan suka fito jin muryar Anna cikin tashin hankali
Da sauri Algabitt ya karaso ya janyota ya ce" Ke Fatimata, meye haka? Daga ina kike? Ya haka a tsiyace jiki a lalace? Ina mijin naki yake????
Dago kumburanrun idannuwanta ta yi ta sauke su kansa, da haushi haushi ta budi baki tun karfinta ta ce"'""" Aba, sai na kashe shi, kuma ko zaka kashe ni sai na hana ka kara bada kannuna a irin auren da ka yi mini!
Idannuwa ya zaro ya daga wukar nan nasa ya. Nufota ya saro daidai ita sai aka yi rashin sa.a Anna ta saka hannunta ta tare wukar ta yi mata muguwar sara a gefen hannunta ta yanketa sosai nan da nan jini ya bale
Ihu yayan suka kwasa, da sauri mariama ta karbe wukar ta yi jifa da ita ta hayayako masa da mugun bacin rai da nuni da zata iya aikata komai ta ce" ka je, kar jini ya biya jini!
Juyawa ya yi da sauri yana mamakin Kaf yayansa idan ya yi magana a da jiki na bari suke aikata abinda yake so aman kwanakin nan yana haduwa da hari kala kala da wajaje daban daban a cikin yayansa bale Mariama yarinyar na da zuciya ........
Labari bak'a ce labari ne kirkirare bisa lamarin da ba kirkirare ba, labarin yana tafiya ne bisa gaskiyar lamarin abinda ke faruwa , tabas na shiga kuma sai na fada......ku mu je zuwa a labarim bak'a ce in sha Allah
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
8⃣
Yana fita Bak'a ta cire daurin dake kanta ta daure hannun mamansu da fan kwalin du suka zauna jigum jigum suna kallon Fatimata
A hankali ta dora kanta kan cinyar mamansu da take jin zuciyarta na yi mata nauyi sosai ta ce" a ranar da aka dora ni saman Amale (Rakumi) daga ni sai mata hudun da suka zo a matsayin fagin mijin da aka aura mini muka tafi
Mun shiga garin agadez daga nan muka dauki hanya muke tafia tamkar ba zamu tsaya ba
Sai da muka je Damagaran daga nan muke mike muka dauki hanyar kano
Muna zuwa kanno muka kwana guda muka dauki motar asuba suwa Abuja
Tafiyarmu tamkar ba zata kare ba, tsakanina da su ido ne su basa jin yarena nima bana jin nasu ya kasance muna tafiyar kurame ne sai dai abinda na lura da shi tamkar masu jin haushina domin ko abinci zasu bani sai dai su wulo mini su fadi wata kalma sannan su yi mini nuni da in ci
Ba mu mu isa garin nan ba sai da safe domin da mukai dare muka tsaya muka waye a wani garin kafin mu karasa
Gida ne tafkeke, ya tsaru, ya hadu iya haduwa
Muna zuwa kowace ta yi tafiyarta aka barni a wani tankamemen falo ina zaune ni guda
Ban jima sosai ba na fara gannin wasu mata masu kyau suma kowace ta sha kwaliya sai baza kamshi take sun fifito sun layu saman kujera gefe da gefena hakan ya saka na takure waje guda
Ba.a jima ba wanda aka aura min da sunan mijina ya fito ashe yana cikin dakin du zaman nan da na yi ya zo ya zauna saman kujerar dake kallon tamu ya dora kafa daya kan daya
Walahi Anna mutumin sam ba annuri a tare da shi, mumuna ne, garjejen kato ne fuskarsa ba anuri ba fara.a ba haske ko kadan a nan ya kuna taba domin ba sigari bace taba ce ya kuna ya shiga ja wace nan take wajen ya garwaye da warin kwaya
Wasu maza ne suka fara shigowa, suka zauna suma inda suke hangen mu da kyau abin mamaki matan nan sai su ringa mukewa daya bayan daya su jujuya gaban mutanen nan wasu har su dakan masu duwawu su mamatsa a gabanmu a gaban kowa shi kuwa yana hakimce idan mace ta yi maka sai su hau ciniki cikin jarshen turanci a dauki mace a tafi da ita kwana wato Bariki
Nan wani yace wannan fa? Wato ni domin sun ga sabuwa ce a wajen
Da sauri na mike domin nunoni ya yi kafin yake yin maganar, koda ban ji me yace ba idannuwana sun nuna mini abubuwan da suka faru na ga komai na gane komai
Magana ya yi masu wace ban san me yake nufi ba suka gama kasuwancinsu ya cashi kudinsa sosai kafin suke tafiya
Sai da ya gama shaye shayensa ya taso kusa da ni sosai da muryar mashayi ya ce" ke fa sai na yi maki filafila dan kuwa an caje ni kudi kafin a bani ke kuma dan iskanci aka kawo ki daga ke sai wannan bakin kayan
Tashi ki tube
Da mamaki nake kallon shi, in tube, wai ina ne nan? Me hakan ke nufi? Matan nan su waye? In tube haka kai tsaye ai ko matarka ce ni koda mun saba da sannin juna fitsara ne gatsal ka kale ni ka ce mini tube
Mikewa na yi da yarena na rufe ido na shiga zazaga fitsara ina son sannin inda ya nufa
Ta yi shiru tana sauke ajiyar zuciya kafin take kara sakin wani kukan mai karfi ta ce" Anna matan nan da suka fita bayan ya amshi kudaden karuwanci da zasu fita su kwana da karti ashe gaba dayan su suna zaune a matsayin matansa mace har bakwai ni ta takwas cikinsu ba daya ta yarwa sannan ba daya da ta san hanyar gidansu
A wannan ranar da katsa ya dake ni kafin yake zuwarmini da wata irin sufa yayi anfani da ni ba imani yana gamawa ya wawatsa kafafuwana ya goge gaba daya najasar nan ya shafe a fuskarsa harda jini jinin nan ya side hannayen nasa ya fice
Anna a wannan ranar.kafin gari ya waye sau tara yana zuwar mini
Mariama ce ta dauko kwan fitilar sosai ta haska wajen kafafuwan Fatimata, ruwa ne ke yawo wanda ya saka Mariama cewa" Anna ruwan nan kuma na menene?
Fatimata ta ce" fitsarina ne ba ruwa ba, haka fitsari ke zubar mini bama na sannin yana binna
Anna ta fashe da wani irin kuka kafin ta ture kan Fatimata ta mike ta yi dakin yaren da sauri hannayenta duka biyu saman kanta, *YoYo, YoYon fitsari Fatimata ke yi*!
A wannan rana yanda suka ga rana haka suka ga dare inda suka cure gaba dayansu waje guda ba mai yiwa yar uwarta magana sai dai suna bin juna da ido , nan Mariama ta mike ta dauko wata leda baka baba ta shinfida ta dauko zani ta shinfida ta kallo yan uwanta ta ce" ke fatimata taso ki kwonta saman nan, ke Agaishat(Bak'a) tafi wajen Anna, kuma ku taso mu kwonta dare na tafiya kar safiya ta yi mana a nan
A hankali ta samu ta lalaba ta hau, suma du suka samu waje suka kwonkwonta ba dan zasu samu yin bacin ba, sun dai yi zuru ne domin Fatimata bata gama basu labarin irin ukubar da ta sha ba aka ga fitsari na binta hakan kuwa ya tayarwa da Annar hankali bata ma tsaya ta ji sauran zancen ba
Anna ce duke kanta kasa ta kai sujada tana ta sheka kuka ta ce" ALLAH ka san wacece ni, kai ka halice ni, ya Allah ina cikin jarabawarka tun daga yannayin aurena har zuwa yau, na rasa me ke daure da ni da wannan mutumin ainahi Allahna idan ba a cikin sallah ba bana iya tuna wacece ni, menene tarihina, ina da yan uwa ko haka nake ni daya? Bana son a yi min maganar ko wa ya kawo min zancen zan nuna bacin raina ne, Allah yayana, ka bayannar sauran, wa.inda basu da lafia ya Allah ka basu lafia, wa.inda yake niyar aurarwa dan samun abin duniya Idan da alkhairi a cikin auren ka tabatarda, idan kuwa ba alkhairi bane Allah kai ka yi shi ka hana, ka hana ya Allah Allah sannan ka yaye min duhun dake cinkushe min ganina
Ta jima tana kai kukanta wajen Allah kafin take mikewa ta yi tahiya ta salamce ta dora adu.a tana ta yawaita istigfari domin ba abinda ke saurin yaye kunci irinta
Da safe tana tashi ta dauki sansani (tabar buzaye) a cikin nata ta matsa a bakinta ta yane jikinta ta buga safiya ta fice a gidan
Zugum suke ba mai yiwa dan uwansa magana har wajen karfe tara Anna bata dawo ba, Aba daman tun cikin daren nan ya fice basu san ina ya kwana ba sannan bai dawo ba, sun zubawa sarautar Allah ido ne kawai
A hankali Bak'a ta kali gorin tsofo, ta mayar ta kule a harshen zaninta a ranta take ayanna bawan Allah ko a wani hali yake? Ko an dauko masa ruwa? Tabas yana cikin damuwar rashin ganninta yau har za.a kwana biyu, sai dai ba zata iya fita ta bar gidansu a wannan halin ba, a hankali ta rike goron ta ce" sofo ina nan lafiata klau, ka ga na saya maka goro ma kar ka damu ina nan tafe wajenka
..........inna Anna ta tafi?????
Gyara kimtsi, mai zamani dan sarki jikan sarki, Buzu jinnin sarauta, yaro mai zamani, taka lafia bijimin sarki, taka lafiya gagara gasa, kai ne na uku baban Rabatima, ka shigo a hankali yarima, taka sanu sanu sarkina
,
Kirarin da jakadiya ke yi masa kennan tunda ya tunkaro dakin mahaifiyarsa,
dan dakatawa ya yi har ta yi gyaran murya kafin yake saka kai da salama a bakinsa
Dago kanta ta yi tana murmushi ta amsa shi, a hankali ya karasa yana wata irin tafiya idan ya daga kafa daya kafin ya daga dayar sai ya jima
Dukawa ya yi har kasa kansa kasa ya ce" ta gode Anna, ta gode Amy (Wato mahaifiyar Wardugu aminiyar matar sarki....da Amy suke kiranta bisa umarnin mahaifiyarsu,)
Murmushi take sakar masa kafin ta ce" oh son tashi mana, amynka ce fa ko dan ka daina zuwa wajena ne?
Yana murmushi ya mike ya zauna saman kushin dake wajen cikin nustuwa suka shiga gaisawa da harsen freinsh domin ita ce kawai yaren da zasu yi su jima suna hira cikib gane abinda suke fadawa juna
Dan jim ya biyo baya kafin yake cewa " Amy ya labarin Oga ne? Na yi na yi ya siyar min da wata mota aman da yake yan rigimar a kansa cewa yayi aa motar ba ta yara bace, ki ji fa Amy
Dariya suka saka gaba dayansu, Ayya ta ce" Wardugu, Wardugu baya jin magana Aghali, sai hakuri da murdaden halayen Wardugu
Mahaifiyar Aghali matar sarki ta ce" Kawata, wai ina labarin aban Wardugu ne? Ni kam ina mamakin lamarinku, kawai daga wannan dan laifin?
Ayya ta dago tana kallonta, a ranta ta ayanna ban ga laifinki ba, ku baku dauki haka a matsayin laifi ba,
A fili kuwa ta ce" manta
Murmushi Mahaifiyar Aghali ta yi, Ayya akoy mulki wannan da gidan sarauta take da an ji jiki domin mace ce mai mulki da isa, ga jan aji, da yake an dauko hirar da bata so daga haka ta katse hirar ta mike tana yi masu salama dan tana son shiga ciki ta kirayi number Wardugu rabonta da shi tunfa suka karaso jiya ba shi ba labarinsa
...........rashin Comment ne kawai zai saka ni daukan matakin siyar da novel din nan ko na tsayar da shi, 😊
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
9⃣
Ayya na zuwa dakin da aka sauketa zauna ta jinginar da bayanta jikin kujera ta daga kanta sama,
Ta jima tana tunani, kafin take sauke ajiyar Zuciya a fili ta ce " *MARAHUT*, ina ka shiga? Ka san komai ka tarwatsa rayuwarmu, Marahut ina tausaya maka sai dai mutuncina darajata ba zan yarda ka zubda mini ba! Ka zabi wancen rayuwar ko? Ba komai ka je sannu duniya zata koya maka hankali,
Ranta ne ta ji yana suya, yama aka yi ta tabo mata wannan mikin, ta sani da gangan ta tuno mata da maganar domin ta fi kowa sannin abinda ya faru, ita kadai sai Wardugu suka san takamaimai abinda ya faru aman zatana tuno mata da shi , ita so take sai ta yi hakuri bata san ta rufe babinsa ba kuma ko da jaraba sai ya saketa dan bata fatan idan ta mutu ya kasance shine alwalin gawarta (Toh fa😳 tubawa akoy zuciya)
Aghali, dan me ba zaka kara aure ba? Matanka biyu yarka daya mace sai matan daki , ko a cikinsu har yanzu ba wace ta samu ciki bayan ina kula da irin zubin da ake maka ana canzawa du wace ta kwana biyu, ko dai baka zuwa inda suken da gaske? Domin na ji kishin kishin cewar wannan matar taka ta shanye min kai,
Mahaifiyar magajin sarki ce ke fada kan ya ki karo aure bayan tana son ya tara yaya
Murmushi ya yi ya ce " zan kara aure, ki kwontar da hankalinki,
Ajiyar zuciya ta sauke kafin take miko masa yar akwati tana murmushi ta ce" ka ga Amynka ta kawowa wannan mumunar ( wato yarsa jikarta)
Hannu ya saka ya bude ya gani, sarka ne da yan kunaye na zinari masu kyau sosai kirar yara, murmushi ya yi ya ce" zata je ta gaisheta sannan ta yi godiya........ wannan kennan
Sai da ta bude lulubarta suka ga mace ce bayan ta fada masu ita mahaifiyar Gaishat ce , suka je suka shaidawa sarki ya bada izinin a shigar da ita bangaren Gaishat din yana mamakin zuwanta da fadawa zuciyarsa ba lafia ba domin shekara kusan takwas da aurensu bata taba takowa ko aiko da kannen Gaishat din ba duda tana yarta ta fari, itama bata wani zuwa gidan du ta takura rayuwarta da tsoronsa ta mayar da kanta ta daki duda kuwa irin yanda yake daukaka martabarta fiye da iyayen yayansa
Tana shiga dakin ta nemi waje nan kasa ta zauna ta sada kanta , da kujeru da komai aman ta fi fanewa zama a kasan nan
Da sauri ta fito jin sakon Sarki wai mamanta ce ta zo
Tana fitowa ta karaso da gudu ta riko hannayenta a rikice ta ce" Anna lafia? Anna wa ya mutu? Anna na shiga uku me yake damunki? Anna me ke faruwa? Me aka maki Anna? Anna.....
Shiiiiit anna ta fada tana dora yatsarta saman leben Gaishat, itama tana kare mata kallo, yarinyar bata wani karu ba a jikinta na da, sai dan girma daga fuska da ta kara, duda jikinta bai nuna alamar wahala ba aman tana da rama, kanta daure ,
Kunyar Gaishat din ta ji ta kamata, dole ta rikice domin bata taba zuwa alkhairi ko tashin hankali ba, itace ma ke yin kokari idan ta san Abansu baya gari ta leko a tsaitsaye ta koma shima ba wani zantawa suke sai dai su bi junna da ita
Tunani ta afka shin fada mata zata yi ko kawai ta yi shiru ta juya
A hankali Gaishat ta dago habar mamanta, dara daran idannuwanta na gado ta saka cikin nata ta ce" Anna, me ke damunki? Ki fada mani kin ji? In sha Allah ko bani da maganin damuwarki zan taya ki da adu.a
Anna ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Gaishat, Algabitt ne....ya samarwa su Mariama mazajen aure wa.inda bama a niger din suke ba, kin san bani da labari tghmass ita a niger din ma aka bayar da ita, jiya Fatimata ta dawo, mariama fatimata ta kamu da cutar rashin rike fitsari , kin san ba maganinsa a kauye sai asibiti, baki ga fatimata ba, ta dawo wata iri,
Ga irin tsanar Agaishat (BAK'A) , ya sako yarinyar a gaba tamkar ya kasheta dan ya san gardawan da yake zuwa da su dan zaben mata ba zasu zabeta ba, shi ya sa nake kara barinta da datinta, mai yiwuwa ita ta tsira daga muguwar rayuwar da yake saka mini yaya
Shiru ta yi kanta sade tana gursheken kuka daga ita har Gaishat din,
Ajiyar zuciya Gaishat ta sauke ta ce" Anna zan zo gidan kin ji? Sai mu samo abinda ya samu mu samu shiga asibitin
Ido Anna ta zaro ta ce" ta yaya zaki fita Gaishat?
Gaishat ta yi murmushi ta ce" Anna, ki daina damuwa da damuwata, ni na dorawa kaina, tabas Aba ya yi auren dole da mutumin da bana so, mai mulkin garina aman shi mutumen jira yake in nuna bukatata a wani abin jiki na rawa yake yi min ko menene , bana tunanin fita zata zama damuwa tsakanina da shi
Anna ta sauke ajiyar zuciya, ta dago habar Gaishat ta ce" me ya sa toh ba zaki kyautata masa ki kontar da hankalinki ba? Shekarunnan ba fa kwanaki bane, ya ci ace kin zubar da komai kun fuskanci juna, ke Allah ya taimake ki kina cikin konciyar hankali kar ki bijirewa Allah mana
Gaishat ta sauke ajiyar zuciya tana kallon Anna na kara nade jikinta da fuskarta wato dai tafia zata yi, ita ba zata ki su dawama a nan suna hira da mahaifiyarta ba
Tana ji tana gani Anna ta yi mata salama ta fice a gidan tana fatan kar ta hadu da wani a kusan gidan yarta ta fari , haka kawai take jin kunyar haka .......
Da dare, bayan ya gama salama da kowa ya nufo dakin mai motsa zuciyarsa, ya sani ne ta san sarai itace da shi aman taga damar ya tarar da ta rufe kofarta
Ga mamakinsa yana taba kofar ya tarar da ita a bude,
Turawa ya yi a hankali ya shiga da salama a bakinsa
Kanta ta dago duda tana jin kunya , ta yi kokari ta amsa salamarsa cikin nutsuwa tana dubansa
Da sauri ya karasa inda take zaune, da alama har wanka ta yi, na menene? Taba jikinta ya fara yi hankalinsa a dan tashe ya ce" GAISHAT baki da lafia ne? Me ke damun ki?
Dan bakinta ta turo, kafin take dauke hannun nasa ta kara turo bakin, murya a matukar kasalance ta ce" me ya sa ka zabi aurena ta hanyar baiwa Abanna damar ya ci gaba da tafka tsiya a cikin garinka?
Dakatawa ya yi, ya yi tsai yana kallonta, a hankali ya rungumeta a jikinsa ya ce" ba dai za.a yafe min ba du irin hakurin da nake bayarwa? Ki gane dan adam nake mai cike da izgili da sabo a doron kasa,
Ajiyar zuciya ta sauke ta ce" ina so ka bar ni na je gida
Da sauri ya zabura ya cikata yana kallonta, muryarsa na rawa rawa ya ce" zaki tafi ki barni kennan? Yau kin fitar abinda ke cikinki shine zaki yi nesa da ni? Me yasa ba zaki yi mini adalci ba? Ina sane da du ranar da zan zo gare ki sai kin sha madaciya dan kar ki haihu da ni, na so daukan mataki a kanki aman bana iyawa Gaishat, ki yi mini adalci mana
Dora dan yatsarta ta yi saman lebensa jajaji abinka da jan buzu ruwan sarauta ko na kauye dawisu ne, ta ce" zama da kai yanzu na fara, ina son zuwa gidanmu ne dan kanwata ba lafia, muna son kaita asibiti, ka bani dama da ikon da zan yi bajinta a lamarin
Ajiyar zuciya ya sauke, ya rungumeta sosai har kamar ta yi ihun zafi, ya mikar da ita yana kallonta ya shiga warware lafayar da ta yane jikinta yanai mata kallon maita, haka ya idasa shigar da ita uwar dakanta cike da zumudi, wa ya isa in ba ita ba? Ita kadai yake tardowa har dakinta, hajia Gaishat mai sarkin garin *TIMIYA*
Kamar yanda ya yi alkawari haka ya bayar da rakumi har goma, ya bata kudi masu yawa ya lamunce mata zuwa gari dan kai kanwarta asibiti inda gari ya dauka ana ta lale lale gimbiya ta karbi soyayar sarkinsu, abinka da kauye har yar salah aka yi ta murnar hakan ...................
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
1⃣1⃣
........Niamey.......
Gidan Wardugu
Kawata, dan Allah wai da gadke kike? Gaki ga yan kaso wa.inda suka aikata mugun laifi? Gaskiya oga ya san kan mugunta
Walyn ta ja tsaki ta ce" ke, a dakin nan a nan suke fitsari, mata sai kawai ki ga an dage buje an tsirara fitsari a tsaye, basa kunya basa kyankyamin wajen , kai gaskiya Wardugu ni da shi akoy tashin hankali, ba ni ya wulakanta ba, walahi sai na rama!
Me zaki yi masa? Wardugu ne fa? Kin manta waye shi? Ko mu da muke gari bama rayuwa da shi mun san waye shi, koda kina kema jinnin tubawa ba lale ki iya da rigimarsa ba, ya hada abubuwa da yawa ne, kin ga shine da daya kwalin kwal a wajen iyayensa, shine Wardugu mai sunnan rikitatu a cikin ku, shi ne Batube, kuma shi ne Soja! Wardugu kakarfa, tsayaye, isashe, hamshakin......
Ke meye haka? Walyn ta fada tana kallon kawar tata,
Ta ce" ya zaki tsaya kina koda min miji sai kace wata mai son min miji? Toh bara ki ji mu a yarenmu ba.a yiwa mace kishiya sai ta cika wa.adin yin hakan, duka duka shekarana biyu da aure da mijina, ko na kai shekarun da yana iya kara wata Wardugu haramiyar wata mace ce a nan duniya, ban ki ba lahira idan ya dace da aljanna!
Murmushi ta yi tana kallonta ta ce" dadina da ke saurin hawa , toh yi hakuri ni ban kai abin can ba ..........
Bakinta ta tabe ta ci gaba da shafa cream dinta kan kurajen cizon sauron da suka yi mata cin balaki a cikin cel din nan, rabonta da ta saka kafarta kofa tunda abin nan ya faru, gashi ta rasa Wardugu a waya kwata kwata, !
Dogo ne fari kar, datijo ne christa sunansa Docter Lucien, kwararen likitan mata kennan wanda ya karanci abin kuma ya lakanta,
Allah ya taimaki su Anna sun samu gannin Docter Lucien a dasha kuma tausayin irin ciwon da ya gani bayan ya sha fada ya karbe su ya shirya shiga tiyata da ita a washe gari wanda cikin ikon Allah sai da ya dauki awa shida kafin yake fitowa daga dakin tiyatar da ita shi ya hada zufa hakama masu kama masa wanda ba.a jima sosai ba aka gurgurota a gadon mararsa lafia aka kaita dakin da ake kontar da masu yoyon fitsari
Jigum suke zaune suna mamakin wai asibiti ce haka, su kam tunda suka shigo garin a tsorace suke da yannayin tsarin gari, gini ne kala daban daban bene kai kasa na cin kudin masu kudin birni ....
A hankali ta shiga bukar tana dube dube kafin take kallo shi, a kwonce yake , idannuwansa a rufe kamar marar lafia
Da sauri ta karasa ta ce " Sofo?
Firgigit ya buda idannuwansa ya sauke saman kanta,
Kokarin tashi yake wanda da kyar abin tsufa ya samu ya zauna yana kallonta, murya na rawa irin ta tsufa ya ce" ina kika shiga? AGAISHAT zuciyata ta rikice na rashin gannin ki, na damu na kasa baci, kin ji har zazabi nake dan bana ganninki yata, ina kika je kwana biyu? Kin san ke nake gani ina jin dadi, kece mai daukana tamkar mahaifi, zo zo na ji me akai maki? Wa ya taba min ke ?
Karasawa ta yi tana sakar masa murmushi ta kamo hannunsa ta damka masa goron da ta siyo masa tun wancen ranar, murya a nitse ta ce" mun fuskanci matsaloli ne a gida Sofo, aman yanzu alhamdulilah mun gode Allah, Su Anna sun tafi birni Sofo, muma watarana zamu je? Zaka tafi da ni nima na ga birni?
Ajiyar zuciya ya yi jin ba abinda ya sameta na tashin hankali, ya lalubo karfen gurza goronsa ya mika mata ta mike ta darwaye ta dawo ta raba goron hudu ta maida hankali ta gurje masa shi tas ta mika masa ai kuwa ya hambuda yana tsotsa yana dan juya kai irin ya ji dadin goron
Can ya ce" Birni garuruwa,
A birnima akoy garin da dadi ne da shi sannan akoy wanda sam ba zaka so rayuwa ciki ba indai kai din bako ne
Birni tana tatare da abubuwan firgitarwa, murane sun yiwa abin hawa irin mashin mota yarda, sun yarda da su suna halaka su
Tagumi ta yi ta ce" suna halaka su kamar yaya?
Ido ya dan zaro ya ce" zaki ga dan birni idan zai yi tafiyar da ba wata nisa ba, ba jeji ba, ba abin tsoro a hanya ba, dan tsabar sangarta da son jiki sai ya dare abin hawa abinsa ya tafi a dan kankanin lokaci in abin ya zo da karar kwana sai ya juyeka tamkar tuwon masara nan zigib ka mace shikennan sai kiyama
Murmushi ta yi ta ce" toh ba kace ajali na tarda mutun du inda yake ba? Mutuwa ai kai ka fada min ba.a gudunta kuma ba.a boye mata, kuna Anna ta ce ita mutuwa lokaci ne idan lokacinka ya yi ba tsumi ba dabara zata daukeka ne ko waye kai ko me kake , kai ka ce min mutuwa mai yanke kauna, takan raba da da uwa, miji da mata, kuma kace min kowani bawa da ajalinsa a duniya
Tsofo yama ta murmushi yana dan barin jikin nan na tsofafi ya dungure kanta ya ce" haka ne Agaishat, Mutuwa gaskiya ce, Allah ya sa mu cika da imani
Ta amsa da amin...., ta ci gaba da fadin " ka ce a birni suna da wata kalar madara banda irin wannan tamu ta rakumi ko shanu? Ina so idan ka je birni ka kawo mini in kaiwa Anna ta sha ta ji itama
Kansa ya girgiza kawai, domin ya lura yau du labari ne a kunshe a bakin Agaishat, wai shi zuwa birni, shi da a yanzu salarma baya iya zuwa masalaci kafafuwa sun kiya, ga tsufa me zai je nema birni? Sai dai idan har kadarar makwoncinsa a can wannan kuwa ya san ko ta wani hali Allah zai kai shi..............
Dago kanta ta yi ta ce " ka san me?
Ya gorgiza kai alamar aa
Ta ce" wankana sau biyu, su Mariama sun bani kaya suka saka na yi wanka
Murmushi yake na jin dadi, bai taba yarda a duniya Allah na hada jinnin mutun da mutun haka kawai sai a kan yar yarinyar nan,
Jinta yake tamkar jinninsa, sonta yake har bargonsa, baya son damuwarta, fatansa Allah ya bata miji na gari komai talaucinsa domin ba zata kasa ratuwa da talaka ba, a hakan rayuwarta ta ginu, gidansu ba laifi su ba talakawanan tukuf bane domin dadaya ne gidajensu ke zagaye a garin aman ita rayuwarta irin ta yayan talakawan nan tukuf ce masu wadatar zuciya,
Tana ta zubar ta mike ta shiga dan totona dakin kamar yanda ta saba dan dudubawa da kyau ta kashe kunama, domin kunamu na cikin kasa bakaken nan wa.inda idan sukai cizo in ba.a yi gagawar shan magani ba dafin na saurin kashe mutun , sune a cikin kasar garin kamar me, yan garin sun iya rayuwa da su, domin sun san inda zasu same su sun iya kashe su tamkar yanda ake kashe cirnaku,
Ta samu ta kashe wajen hudu ta cilar waje ta dauku tulu ta ce" sai na dawo
Hannu ya daga mata yana murmushi ya ce" Allah ya tsare ki
Yana kallonta har ta fice , ya samu kansa da zirarar hawaye, ya ce" ya Allah baka barin wani dan wani ya ji dadi, Allah ka sa , ka yarda, ka aminta , ka bani ikon gannin ta shiga hannu mai kyau kafin na koma gareka .......
*Niamey*
Kan Anna kasa take tafiya domin bata son gannin irin yanda mutanen ke cuwa cuwa, a can kauye shiru ne, ba hayaniya , ba komai, sannan mutanen basu fi a kirga ba, hakan ya sa du idan ta fito daga dakin da Fatimata take koda dan ta leka ta ga safiya ce rana ne ko dare ne? Sai ta rikice
Ji ta yi ta ci karo da mutun, da sauri ta dago dan bayar da hakuri sai dai me, gani ta yi ya zaro idannuwansa yana kallonta, a hankali ya nunota da yatsarsa sai dai wani abin ya ce masa Haba docter, haba docter, wacen koda jikin manyanta ya kamata ba zata koma haka ba, kuma ita batuba ce ba buzuwa ba, wannan kuwa buzuwa ce ta sha bakaken kayanta, kai bama zai yiwu ace ita bace,
Da sauri ya ce" yi hakuri baiwar Allah
Bata san ta ina ta iya hausa ba, bata san ya aka yi ta ce" Ba komai yi hakuri kaima
Gaba ya yi yana dan waiwayenta, shi dai rabinsa da wancen dama familynta tunda aka hana masa aurenta, tun suna saurayi da budurwa, muryar wancen da wannan ba daya ba, sannan kai ka daina tunani kan matar nan mai yiwuwa matar aure ce
Da sauri ya kawar da maganar a ransa ya nufi office dinsa yana dafe kansa a fili ya furta" ya dace na ajiye aikin nan, na jima ina fama har jikin tsufa ya zo....
Tunda ta koma dakin ta yi shiru tana tunani,
Gaishat ce ta salame sallah ta juyo tana kallon maman nata ta ce" Anna me ke damunki ne??
Anna ta dan yi jim ta dago ta ce" wani yare na yi yanzu Gaishat, wanni mutun na kade ya min yare na bashi amsa tartar tamkar na iya yaren
Da mamaki Gaishat ta taso ta zauna kusa da ita ta ce" me kuka ce?????????
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
1⃣2⃣
Cikin yaren buzanci Anna ta maimaita mata abinda suka ce
Da mamaki take kara kallon Anna ta ce" kuma baki san sunnan yaren ba?
Anna ta girgiza kai, da yannayin damuwa a fuskarta ta ce" ban sani ba, kuma da dukan alama ba yaren faransanci bane domin likita ya yi ta yinsa a gabana ba wani fahimta nake ba, sannan ba yaren nan da muke ji wajen masu siyar da abinci a garinnan bane wato Zabarmanci, wannan yaren shima daban yake
Gaishat ta mike tana kallon ledar fitsarin fatimata ta ga bata cika ba ta ce" Anna, ko mu koma wajen mutumen ku kara yin yaren? Anna ko haka na da nasaba da asalinki?
Nan da nan Anna ta ji ranta ya baci, asalinta? Kennan dai yayanta ba zasu daina daga mata hankali da wannan kalmar ba, rai a bace ta ce" ina ruwanki da asalina Gaishat? Ina ruwanki? Tana gama fada ta fice a dakin don ji take zuciyarta sai tukuki take mata na bacin rai
Da kallo Gaishat ta rakata, haka ne, komai irin dadin da kake ciki da Annarsu in dai ka yi gigin neman sannin wacece ita? Zata fatatakeka ne ko waye kai komai kusancinka da ita,
Ajiyar zuciya ta sauke ta karasa kusa da Fatimata da yanzu masha Allah sosai take samun sauki dinkinta ana kula da ita sosai, likitan karshe ne , du niger ta wannan fannin da shi muke takama!
A yannayin nishadi ta fito a gidansu, Abanta ya santalo Amarya yar bariki, irin a nuna masa ana son yayansa har Bak'A bata kyamata tana bata abinci bayan ya cashewa maryama kudaden da ta yi rantsuwar ba za.a shiga da matar ba sai ya bada su ......Algabitt dai na rakashewa fa amarya , yayansa na gefe suna rayuwarsu , inda bak'a ta dan samu inci na kwana biyu a gidansu domin bashi da lokacin wulakantata yana malake da amarya yan uwanta kuwa sosai suka dan sasauta mata tsanar da sukai mata
Yar waka take da yaren buzanci tana saka sunnanta a ciki, fadi take" ni bak'a yau wa zai so ni?
Bak'a nake wa zai rabe ni?
Yar bak'a haka ne sunana!
Dala biyar babu mai kaunata,
Ta yi dariya ta ce" ni ko a baiwa an rasa mai siyana a kauye da birni,
Agaishat kij cika muni....ta fadawa kanta sai kuma ta yi murmushi tana girgiza kai kawai
Algabittt, yar firit din yarinyar da ya auro ta furta kai tsaye
Shi kuwa da yake saman gadon karagarsa ya yi dadaya ya kallota ya amsata da um?
Tasowa ta yi tana juyi uwa bishiya ta karaso tana nuna masa gidan manta na shafawa ta ce" ka san yanzu muma a kauye mun yi ido, yarinyar nan jikanyar mai siyar da fura nake kawance da ita, ita na baiwa kudina ta siyo min wannan man,
Na ga fatar Agaishat ta dameka, baka son yarinyar dan bakinta, ni kuwa na hango kyakyawar yarinya ce ta karshe kawai bakin ne ya yi mata yawa, dan haka ga shawara wace in dai ka yarda ka takurata ta yi a hankali zata dawo farar mace itama mu siyar mu samu kudinmu mu yi tafiyarmu birni mu je mu rakashe mu hau mota mu saka gilashi mu dangwali kaji
Wata zabura ya yi daga konce yana kallonta, irin maganar ta fara shigarsa, ya fara aminta da shawarar amaryar tasa
Kara jujuya masa ido ta yi ta mika masa ta ce" ka ga bude ka gani, ai dai ka san wannan uban farin da na kara ba nawa bane wanda har kake son samun irina ............. ka yi mini ciki na haifa maka mai kyau ko? To sai fa wannan, ka bada na je na kai mata a siyo mata ta shashafa ka ga yanda bak'arka zata dawo yar dagwasssssss
Murmushi ya sakar mata ya jawota jikinsa ya ce" na yarda, in dai ta dawo fara sai in baki ki kai a siyo dan ubanta sai ta shafa ko bata so
Dan ture shi ta yi tana jin haushi a ranta, dan jaraba sai ya kama ya jajagulata shi ba wani nisa yake yi da lamarin ba du ya hargitsa mata tunani ya barta, haba ta yi aure ta bar jarumin maza saurayinta, aman yau sai ta gayato sho gidan nan
Dan dukan kirjinsa ta yi ta ce" ina so wani dan uwana ya zo mu wuni tare yau Algabiiiiitttttt
Ta fada tana jan sunnan
Da ido ya tsareta, wai itama nan ta iya bariki, murmushi ya yi, shi dai burinsa ta dauki ciki fa? Ina ruwansa inma 2a zqi dane mata ruwan ciki, shi dai in ta yi cikin ta haifar masa kace komin jaraba ya rike abinsa ko a shekara goma ne ya saida ya kara kama daloli, shi kam haihuwar yaya mata ta yi masa rana ( wani abu zai baku mamaki a lamarin nan, irin yanda Algabitt baya kishin matarsa? To bara ku ji readers , ban ce duka buzaye ba, ba zan ce duka ba domin mahaifina buzu ne dan tsananin kulle da yake yiwa matansa ko gidan mutuwa da ta shafi gidansu zasu je shi ke kai su da kansa ba direba ba kuma ya tsaya su fito rufrufruf uwa matan ninja baka gannin komai na jikinsa ko.ina a rufe ruf ba damar ganninsu komai kusancinka da su, sai dai kuma akoy buzayen da basu san darajar matansu ba, sam basa kishin matansu, sai su ga matarsu kwonce saman bed da kato su fice abinsu ko a kwalar rigarsu, baya hana suma in an jima su taketa abinsu doki ce dan haka suke zaune da ita ba wani abin ba! Gaskiya ce a fadeta🤷🏻♀)
Murmushi Algabit ya yi mata ya matsota sosai cikin yannayin rada ya ce" ke , kar ki damu da fada mini fan yan uwanki maza zasu zo, in dai zaki zauna da ni ki haifa mini mata masu kyau? To na baki dama!
Ai kuwa da murna ta rungumeshi ta shiga bashi kulawa daidai daukar hankalin tsufansa 🤦♀
Wannan kennan
................................................
A hankali ya jona wayar abinda zai dafa masa ruwan zafin dan ya kada madara ya sha
Komawa ya yi jikin bed ya zauna ya shiga karanta messages din Walyn, daya bayan daya,
Na farkon farkon du yannayin ranta a bace ne, harda baya jin kunyar a ce matarsa guda ta kwana a cell? Toh garin niamey ya dauka, ita yanzu kunyar zuwa auren da zata hadu da mata take, a jejefeta da habaici ya nuna ita ba kowa bace a fadin duniya
Sai daga baya kuma ta fara nuna wai ina ya je ne? Ya haka zai yi tafiya bai yi mata salama ba? Ina ya tafi?
Sai daga karshe ta sauko sosai ta yi ta turo masa alamun kuka da nuna ta yi missing dinsa yana ina ne? Tana son ganninsa ta yi missing dinsa
Murmushi ya yi a fili ya ce" Hajia Walyn matar Wardugu, Walyn mai zamani,
Girgiza kai ya yi, kai shi kansa ya sani da ace wani saunan namiji ne da tuni Walyn sai yanda ta yi da shi, kuma ba boka ba malan!
Wayarsa ya kunna wace take kiransa, ya cireta a liste noire (Black list) ya kwonta yana sauraron ruwan zafin na karar ya dafu aman ya yi masa banza, tunani yake, wai shi shugaban revel zai yiwa haka? Ya fada masa gashinnan zuwa aman ya ki zuwa? Har ya je ya yi ta zaman jiransa wai sai daga baya ya yi masa message cewa ba zai samu zuwa ba,? Ya sani sarai waye shi aman ai shima ya san waye shi! In ba dan tsufansa ba da sai ta tafka masa ashar din da zai gigita!
Wayarsa ce ta shiga kara , irin kukan bindiga ratatatttatatatatatattatatatatatatattatatatatatatatatatatatatatat
Muka hannunsa ya yi ya dauko yana karanta sunnan mai kiran
Sai da ta tsinke aka sake kira kafin ya daga bai yi magana ba
Oga, bako ne muka yi, ahi kadai yake tafe cikin duhun nan, ya zo ta hanyar boye , ragar wajen nan ta shaida zuwansa domin ta kama masa hannun shine ya fito yana fada
Kai waye ya zo? Wardugu ya katse shi da kakausar murya
Murya na rawa ya ce" Shugaban Revel!
Wardugu ya lumshe idannuwansa, a nitse ya ce" ku shigo da shi fallon farko, ku juya
Da toh suka amsa suna masu mamakin mai gidansu, yana nufin daga shi sai shi zai ganna da wannan hatsabibin mutumen? Lale Wardugu bashi da tsoro, baya dar, baya tsoron uban kowa!
Kwonciyarsa ya yi bayan ya ji wa ke jiransa,
Can cikin tunaninsa wayar ta kuma daukan kuka,
Da haushi haushi ya mike ya daga da kakausar muryar nasa ya ce" Hello!
Wardu.........ta fada cikin sanyin murya
Tsai ya yi bai amsata ba
Kuka ta fashe da shi ta ce" tu me manque (i miss you)
Ajiyar zuciya ya sauke a takaice ya ce" ki bi Nuger airlines gobe ina Agadez hotel din sojoji ki sauka nan ko bana nan ki je dakina
Yana gama fada ya kashe kiran yana shafa gefen fuskarsa da sajensa
DOGON wando ya dora saman gajeran ya saka riga fara kar ta ririke damatsunansa ya fito ya nufi fallon da aka sauke bakon dare (🤣)
Yana zuwa ya shigo kai tsaye,
Mutumen dake zaune ya sha rawani ya hakimce cikin shiga ta kamala mai daukaka darajar dan adam ya dago ya tsaida kallonsa kan Wardugu, a tarihin rayuwarsa dole ya sako wannan yaro, domin shi ne mutun na uku da ya ajiye shi jira
Murya a kausashe ya ce" Wardugu ba.a tsayar da ni jira
Shima Wardugu kai tsaye ya ce" *Rhissa agbula* ba.a ajiyeni jira!
Murmushi Rhissa ya yi, ya mike tsaye suka gaisa irin gaisuwar musulunci suka baiwa juna hannu suna yiwa juna salama
Wardugu ya ce" ya zaka zo wajena ni daya bayan ka san ya dace a tatauna da kai a bainar nasi kowa na da magana da kai harda mai zuwa da maganar shugaban kasarka
Rhissa ya ce" shugaban kasarka dai, ka san ni ba nawa ba! Sannan ni kaima da na aminta ganninka dan na fafata da kai na yarda tsaurin kanka zai je da nawa, bana musanyar yawu da matsoraci, ba.a daukana a tv haka kyauta sai kace wani sakarai!
Wardugu ya girgiza kai ya ce" ya ake ciki? Wa ke son tayarwa kasata hankali? Ina suke? Menene abubuwan yakinsu? Ana jitajitar kune kuka dawo bayan kun daina aiki a niger kace niger ta yi maka kadan sata yanzu? Me yasa ake samun gawarwakin bayin Allah a gidajensu? Masu aikata min haka baki ne! Da sun san idan na damke su zasuna kururuwar na kashe su da abinda nake masu da basu shiga gonata ba!
Wardugu ya karasa yana dukan table din glass din dake falon ya yi wani jijiga aman bai fashe ba domin irin wannan mai masifar karkon ne, sai bindiga mai tsini ke tarwatsa shi
Rhissa ya mike tsaye ya ce" ba ni bane, kuma ba yarana bane, abinda ya sa na tsayar da hankalina kennan har na baro aikina na garzayo dan ganawa da kai! Kar ka shiga yaki da ni ba ni bane! Na yi bincike tsageru ne, kan harkar siyasa ne, kuma na ga makwoncinsu, suna cancanza waje ne ina son sannin tsarin canza wajen nasu, Wardugu nima sai na yi maka maganninsu
Wardugu ya girgiza kai ya ce.....
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
1⃣3⃣
Wardugu ya girgiza kai ya ce" ka taba gannin na nemi agaji? Kokowa ai ya dace mutun yayi abinsa! Ka bani hanya kawai ka barni da sauran ai na san tsarin tsagerancin yan tsagera, idan ka yi yaki a kambacina kana so gobe su afko su aikata abinda ya fi haka? Domin sun san ba zan iya tarbansu ba? Aa ba dai Wardugu ba
Haka tataunawar Wardugu da Rhissa ta kare, kowa na ji da kansa da kuma ikirarin kansa,
Rhissa ya san abu guda Wardugu ba wai cika baki yake ba, yana fadin abinda zai iya aikatawa ne, ya san da in dai suka yarda ya ci masu kamar yanda ya fada ne sai sun gwamace mutuwarsu da rayuwarsu a hannunsa, Wardugu ya ga damar ya fitar da su jeji su fuskanci juna wanda hakan kuwa ba zai gyara su ba!
Wannan kennan
Bayan kwana biyu .......AMERICA
Docteur Mu.azam ne ke zaune yana dadana computer,
Can ya dago kansa ya duba time,
A hankali ya ajiye ya mike ya nufi bayi ya sakarwa kansa ruwa
Yana fitowa ya dauki kayansa ya saka ya saka vest dinsa ya dauki agogonsa ya daura ya fito fallonsa dan madaidaici ba wani tarkace sai kujeru da dan table da tv tankamemiya, sai hoton wasu fararan mutane mata da miji ga dukan alamu suna murmushi a hoto
Kamar yanda ya saba zuwa ya yi ganan hoton ya tsaya ya ce" Abi, amy asalamu alaikum, yauma na tashi lafia, sai dai har yanzu ya kasa hakuri ya daina fushi da ni, gashi aiki ya taso min a kasarsa banda shi da mahaifiyarsa da mahaifinsa da suka dauke ni tamkar dan cikinsu bani da kowa,
Zan kuma gwada kiransa ku taya ni da adu.a daga inda kuke, ina mai kara yi maku adu.ar Allah ya sa kuna cikin Aljannah
Shi kadai ya tsaya ya yi zubarsa kafin yake zuwa wajen wayarsa ya zauna yana dan murmushi ya shiga doka kira
Yana kallon wayar na haske ya ki dagawa, Walyn ce ta fito daga wanka ta zo ta mike abinta saman lafiyayan bed din hotel din itama tana duba saman screnn din dan gannin wa ke kiransa yake sharewa haka?
Murmushi ta yi ta juya abinta ta shiga neman baci a kasan zuciyarta tana ayanna toh fa da shima yana gaba bare ni?
Can dai ya daga ya saka a handsfree
Soja kake
Ya fada yana danne dariyar farin cikin ya daga kiransa
Murya ciki ciki ya ce" Docter kake, kuma dan rainin hankali kake
Murmushi ya yi ya ce" baka hakuri ne? Baka mantuwa ne???
Wardugu ya kawar da kansa ya ce" haka, ka san ba nine na watsa taron aurena ranar aurena dan wani gudiri nawa na shirme daga shiga ka ga amarya kafin a daura aure zaka fito ka watsa taro? Kai mahaukaci ne! Mu.azam baka da nutsuwa
Mu.azam ya bushe da dariya ya ce" Wardugu, abinda ya sa na tsalako fararan fatar, na yi doguwar tafiya niger ba dan ina son na samu *BAK'A* bane?, ni bak'ar mace nake so, ita ce ra.ayina, ita nake son zaman aure da ita! Kar ka manta ni likitan mata ne, idan ka ga na kuke abu kaima ka gwada abokina
Tsaki wardugu ya ja ya ce" kiran na menene?
Mu.azam ya kuma yin dariya ya ce" kai ka dena jin haushina mana, ai ni ban shaki mahaifin matana ba
Da sauri wardugu ya kai dubansa wajen Walyn wace ke kwonce, ta ji sarai dan haka ta yi saurin mikewa tana kallonsa,
Fuska ya hade idannuwansa cikin nata ya ce" eh haka ne na shake shi, domin a lokacin ban san mahaifinta bane, kuma na tarar da shi ya zabgawa mamanta mari , idona ya rufe ban tsaya wata wata ba na shake shi, kai dan ubanka sai yanzu ka tina?????
Ajiyar zuciya ta sauke, tana tine da ranar .....dalilin wannan action din da yayi na ta haukace kansa, wardugu jarabar duniya....komawa ta yi ta kwonta ta ja bargo tana rufe jikinta
Wardugu ya fice a dakin , yana fita ya ce" Mu.azam??
Mu.azam ya amsa da na.am?
Wardugu ya ce" kana son kashe min aure ne? Tana jinka fa
Mu.azam bai ji dadi ba aman ya ya iya har ta ji, dan tsam ya yi kafin cikin yannayin mamaki ya ce" Wardugu yamzu tsareka ake idan zaka amsa waya ko me? Lale dole na auri batuba
Kai banza ka nutsu ka ji!!
Mu.azam ya yi murmushi ya ce" dadina da soja zagi, ni dai ka fadawa Ayyata in sha Allah ina nan ina faman gama abinda nake zan shigo Niger, ka san bani da masauki sai kusa da ita dan ita ta iya kula da cikina, zan zo ba zan dawo ba sai na samu macen aure na kuma gama abindq zai kawo ni
Wardugu ya ji dadin haka dan haka ya amsa shi da murnar hakan
Satin su wardugu hudu a garin Agadez yana faman aikinsa wanda tun Anna na fada har ta kawo ido ta zuba masa, gashi ta yi ta yi aminiyarta ta barta ta koma wani wajen ta kiya ta ki fir sai ma fada da ta dauka cewar masarautar ai girma ne da ita, ba ita ba ko baki ta kawo suna da wajen zama har lokacin da suke so a masarautar Agadez
A yau suke saka ran komawa bayan ya fada masu su kiyaye, ya basu magungunna, ya kafa masu sharuda kan lafiar Fatimata,
Jirgin da ya kawo su an basu takarda dan haka suka kai aka saka su a layin wa.inda zai mayar garin agadez bisa jagorancin docter Fannata
Sun sauka lafia inda Fatimata ke dan takawa a hankali daga nan suka nemi abin hawa dan karasawa Timiya............
Timiya.....me aka kwaba? Me aka yi me ba.a yi ba? Me ake cikin yi? Timiya gari mai abin mamaki, Timiya garin bak'a,
Duka na kawo wuka a yanka Algabitt ya yi mata bisa taki shafa man da ya fitar da kudi ya saya,
Rai bace ya ce" sai na tsine maki in dai baki shafa man nan ba
Cikin kuka ta ce" Aba, ka yi hakuri ka ji? Bana son canza kalar fatana ka yi hakuri Abanna
Ni ban haifeki ba, ke ba abin alfaharinki bane yau har na yi hakuri na dube ki na nemi intaki aman ki butulce min? Uban wa ke hure maki kune ne ni?
Aba ba kyau, ba kyau, mu ji tsoron Allah
Hannu ya saka ya dake bakinta ya ce" ki rufe mini bakinkin nan mai bakin jaraba! Ke sai kin shafa
Kokarin shaketa yake dan ya shafa mata Mariama ta fito da gudu tana ihu tana nuna dakinsu
Dakatawa ya yi yana binta da kallon meye ke kuwa
Hankali tashe ta ce" Ashta ce, ashta ce, tun da ta ce maka in dai ka yi mata auren nan sai dai a kai gawarta kai kuwa kace sai me ba dai ka daura mata auren ba? Ita ce gata can sai wani abu take daga baya ta fasa motsi
Fancakalar da Bak'a ya yi, shi da amaryarsa suka nufi dakin da gudu
Daidai wannan lokacin Su Anna da sukai doguwar tafiya suka shigo gidan da salama bayan su Dogarai ne da suka tarbo gimbiyarsu wace sarki yake hakimce yana ji tamkar ya zo ya tarbi abinsa
Jin kururuwa ya saka gaban Anna ya yanke ya yi wani irin faduwa, cak ta tsaya tana sauraron magangannun dake tashi, ihun kuka yayanta biyu suke inda Bak'a ke jingine jikin garu ta daga hannunta ta dora saman kanta ta yi tamkar status tana kallon kofar dqkin nasu ,
Muryar amaryar Algabiitt ce ta tashi ta ce" ta kashe kanta, ta kashe kanta
Wani irin luuuuu Anna ta yi wanda ba wanda ya ganta sai faduwarta da aka ji , nan mutanen gidan suka ankara da dawowarsu wanda nan da nan gidan kai dama anguwar ta cika da dukan jama.a ana ta daga maganar, tabas Ashata ta rasu, ta rasu ne da bakin ciki, tana da ciwon zuciya ne wanda ya yi mata tashin kai tsaye, wanda amaryar Algabitt ta yi kazafin ta kashe kanta,
Tashin hankali!
Mota ce katuwa irin ta sojoji, direba mai iya janta kawai ya dauka kai tsaye suka karasa gidan Sarki
Ayya na zaune tana gyara akaifunta labari ya zo mata cewar ta fito su tafi
Mikewa ta yi fa hanzari tana murnar yau kam Allah ya sa ,
Tafia suke cikin mota, Walyn na zaune tunda ta cewa Ayya ina kwana bata kara magana ba sai shanshan kamshi take domin da yar tsamarsu da Ayya, gani take Ayya ke zige mata miji yana wulakantata
Tafia ce suka yi mai tsayi, cikin jeji ne sosai kafin suke shigewa sahara gaba da baya
Wani kara motar take a cikin kasar nan tana cin tafiyar wace kana ganni ka san karfi ne ke aiki
Duda a cikin mota suke aman sun yi budu budu da su domin kura sosai ke tashi sanadiyar gudun da suke a motar da kuma kasa
A hankali ya ratsa yar gadar da ta kai mutun cikin kauyen, wato *TIMIYA*..............
YA RAYUWAR ANNA?
ALGABITTTT FA?
BAK'A?????
SU WARDUGU DA AYYA DA WALYN ME YA KAWO SU TIMIYA??????? MU JE ZUWA ...........................................................na yi imanin da ba dan Allah na sakawa bawa hakuri da dangana a zuciyarsa a lokacin da ya rasa wani mutun mafi kusanci da shi da Anna ta samu tabuwar hankali ga wannan lamari na mijinta, kar ku manta na fada ba labarin mutun na dauko ba aa labarin abinda ke faruwa ne, (YA FARU!)......
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
1⃣4⃣
Bayan sun shiga garin timiya mutane suka ringa gudu suna kururuwa, wasu na fadawa gidajensu wasun kuwa na nufa gidan sarki wasu kuwa na kokarin neman hanyar da zata fitar da su daga garin ta barauniyar hanyoyi domin dai garin ba wani rufe yake ba
Da mamaki suke kallon reaction din mutanen, Warsugu da sojan dake jansu ne kawai basu yi mamaki sosai ba duba da yannayin garin motar lafia dai bata shiga sai ta sojoji ko kuwa motar mugayen mutane masu zuwa su kai hargitsi su kashe mutane
Kallonsa ya maida wajen Ayya wace ta dafe habarta ta wara idannuwanta tana mamakin nan yake mutumen kuwa? Aman gudun me suke?
Labari ya kaiwa sarki a yar fadarsa,
Tabas gabansa ya fadi da jin wannan lamari, ba a taba ba, mota har nan bata fara shiga ba,
Mikewa ya yi da dukan kokarinsa ya tatara karfinsa inda dogarawa suka shiga kabara sunai masa kallon jarumi mai tausayin talakawansa da kuma kallon marigayi
Du a bayansa suke inda yake daga kafafuwansa da kyar yana kara tunkarar motar, gannin motar ta sojoji ce hankalinda ya kara tashi, domin dai shi ya san motar tunda yana shiga gari kai gaisuwa fada, kai harma ya tafi kasa mai tsarki, me ya kawo motar sojawa Timiya? Shine tambayar da yake yiwa kansa,
To ko dai sojojin ne a cikin motar ko kuwa mugayen mutane domin idan sun kai hari ai suna karbe motocin sojawan
Wardugu ne ya bude gefen da yake zaune ya karbe hannunsa daga rikon da walyn ta yi masa ya diro daga cikin motar tsaye kan kafafuwansa
Jibgi, dankari, in ba wardugu ba zaka shiga kauye sai ka je da wando tree Carter? Sai rigar sojawa irin body din nan damatsunnan hannayensa a fili, yar karamar bindiga marar karan sautin harbi ce a kugunsa inda ya rufeta da wannan rigar ta jikinsa ya saka belt kalar kayan sojojin ya daure tam abinsa
Kansa sanye da hula baka kalar wandon sai takalminsa sandal wanda ya daura abinsa
Sun karbe shi, sun amshi jikinsa, sun kawata shi
Taku ya shiga yi da karfin jiki ya nufi Sarki da ya ja ya tsaya jikinsa na bari, ta faru ta kare, jita jitar Ashta kanwar matarsa ta kashe kanta wani ya kai birni an zo kama sirikinsa, mutuwar yau har kwana takwassss tabas wani ya kai, shikennan Alghabiitttt ya bani domin a hoto kuma a tv a birni Yana gannin wannan mutumen, an ce shugaban sojoji ne, shi da kansa ya zo kama algabiit? Algabitt ya ji haushin rayuwarsa, tunanin da Sarki ke yi kennan inda ya daskare da tare da bugun zuciyar ko wani taku na Wardugu dan nufo shi (🤦♀ in ba kauyanci irin na sarki ba, a rasa mai zuwa kama Algabiit karamin kwaro sai Wardugu? Za dai ka san waye shugaban sojojin nan hangensa kake!)
Yannayin shigarsa ta tabatarwa da Wardugu shi ne magabacin garin, dama irin haka idan an zo sarkin gari ko mai garin gari ko kuwa tsageran gari wanda ya gagari uban kowa ke zuwa ya tarbi mutanen, in da karar kwana a kansu ake farawa
Salama ya yiwa sarkin yana mika masa hannu sannan tar yana kallonsa ido cikin ido
Jiki na bari Sarki ya karbi gaisuwarsa yana tambayarsa hanya da zarcewa da magana kamar haka" mai gida, na san ba auren iri ka zo nema a wannan jeji namu ba? Koma wa ka zo kamawa ka yi hakuri, a yi mana sasauci kar a kashe mu, a kama iya mutumen a tafi, ni kaina inada kankannan yara da mata, idan aka tsame masu ni wa zai ji da su?
Da mamaki Wardugu ke kallonsa , aman da yake Wardugu dan duniya ne sai ya ce" Kai, baka san Allah baya barin wani dan wani ya ji dadi ba?
Ai kuwa gaba daya sarki ya haukace, jiki na bari ya saki kuka ya duka kasa ya rike kafafuwan wardugu ya shiga magiya
Ayya dake cikin mota ta dake lebenta na kasa ta kali sojan nan ta ce" ka karasa da mu, na san wardugu wani lamarin ya shiga na tsawatar masa tun kafin abin ya birge shi
Walyn ce ta juyo da sauri ta kalli Ayya, a ranta ta ayanna wai ta tsawatar masa, sai son ta nuna ita kadai ta isa ta juya shi, ta ja tsaki a ranta a fili kuwa ta ce" Hum tana tabe bakinta sosai
Sojan ne ya juyo ya ce" Hajia, ki yi hakuri, nan ya ce na ja na tsaya idan na matsa bai bani umarni ba ni da shi ne
Da haushi haushi ta shiga bude motar wanda sojan bai ankara ba har sai da ya ji ta bude ya juyo da sauri , har ta sauke kafarta guda ta ga Wardugun ya dawo da saurinsa gefen da take
Yana zuwa ya ja ya tsara mata ya ce" Ayya maman Wardugu, kece ikon mai sanya Wardugu cire wando ta kai, Ayyana kar ki yi fushi kin ji? Koma motar mu karasa sai ki yi masa tambayar ai sarkinsu ne
Da mamaki ta saki baki tana kallonsa, sarkinsu? Aman me ya saka shi kuka da dukawa ya kama kafar wardugu?
Dan murmushi ya yi bayan ya saka mata lafayarta ciki ya rufe ya bada umarnin su karasa inda sarki yake
Suna karasawa Ayya ta bude tana shirin fitowa sarkin na karasowa ya dan risina yana gaisheta,
Ayya ta kalli wardugu ya dan sakar mata murmushi
Kai ta girgiza ta sauka sosai ta gaishe da sarkin kafin take fada masa abinda ya kawo su
Wata ajiyar zuciya ya sauke a bayane, ya ce" A garinnan Sofo mai bada magani kwaya daya mukeda, ya sufa sosai, gidansa da dan nisa da kasuwarnan sai mun shiga gari sosai
Ayya ta amsawa sarki da ba damuwa su je
A cikin motar nan sarki ya shiga inda yake dan hangen Wardugu ta madubi lokaci zuwa lokaci, ya yarda da ake cewa sarkin sojojin fa masifafe ne , bashi da dar, in ba rashin tsoro ba du irin yanda ake tsoron abzinawa da asiri shi a gabansa sai dai ma shi sarkin ya ji gabansa ya fadi maimakun na wardugun ya fadi, lale yaron ya sha ya jiku ya tada kai , rabonsa da kuka tunda aka zo masa da sakon Gaishat ta tafi baban birnin niger inda ya yi tunanin shikenan ta gudu me ta bar shi.....(wani lamarin dan gyara nvl dina ne fa, sarkin abzin ba wasa walahi🤣🤣)
Basu zame ko.ina ba sai anguwar baba Sofo
Suna tsayawa mutane suka cika wajen, tunda sun ga sarkinsu a tare da mutanen ai shikenan sai suka sakin jikinsu da su harma ake matsowa a shafa motar sai a kwala ihu da yaren buzanci a ce" nima na taba, mota mota a garinmu, mota har gidanmu,
Du ja sukai a lokacin da mutanen ciki suka fito gaba dayansu, suna masu binsu da kallo, girma da yannayin tsarin halitar wardugu ta basu mamaki, suna da mutane dogaye sosai sai dai ba masu fafadan kirji da manyan damatsuna haka ba, sai kuma matan dake tare da mutumen da dayen sojan, kun san dai Ayya gwadar ado ce, bale Walyn farar mace alkyabar mata, walyn farar batuba ce tas tas tas, Ayya ce ma baka domin Ayya baka ce mahaifin wardugu ne farin batube shima tas tas tas , sai sojan dake saye da kayan sojoji komai harda bindigarsa da katon takalmin nan nasu da komai sai muzurai yake
Sarki ne ya amsa gaisuwarsu kafin yake kai dubansa bukar Sofo,
Bukar kanta ta tsufa du ta zuzube sai abinda ba za.a rasa ba, ga dati sosai a dan nesa da wajen domin an yi rasuwa baka bata samu zuwa ta share masa ta gyara masa ba,
Ruwa kawai take zuwa ta dauko masa ta koma
Nuna masu wajen ya yi bayan ya samu ya shiga ya tarar yana zaune saman buzunsa da carbinsa yana ja ya kurawa waje guda ido yana ta istighfari(Allah ka bamu nitsatsen tsufa in muna da rai wanda zai kara kusanta mu da kai ya Allah)
Gaishe shi ya yi ya juya inda sofo ke bin kofar da kallon mamaki, me ya kawo Sarki har wajena? Kuma hayaniyar me nake ji haka?
Ku shigo;
Sarki ya fada yana dubansu
wardugu ya ce" anya kuwa? Me zai hana ya fito???
Ayya ta kallo shi ta ce" Wardug.....
Da sauri ya yi gaba ya fara nufar yar bukar sofon a ransa yana ayyana ai idan Ayya ta nadaka toh fa tana yi da kai
Shishiga sukai banda sojan nan,
Walyn na saka kanta ta yi baya tana kakarin amai da coshe hanci, a fili ta furta" kai ina , ba zan iya ba!
Ayya ta karasa a hankali kusan tsofon dake zaune ya zuba masu ido gaba dayansu yana mai binsu da kallo, ko gezau bai yi ba daga zaman da yake sannan yana jan carbinsa cikin nutsuwa
A hankali ya amsa salamar Ayya da ta nufo shi cikin nutsuwa ta tsugunna dan nesa da shi aman suna facing din juna
A hankali ta ce" lokaci mai tafiyar da abubuwa, lokaci mai bayanna abubuwa, lokaci mai rarabe abubuwa,
Baba tsufa ya zo haka? Allah ya sa mu cika da kyau da imani
Murmushi ya yi na gano wacece ita, tabas ya ganeta, idan ba zai manta ba shekaru sun kai talatin da suka shude ya sha kai mata magannin athsma na yaronta da bai fi shekara hudu a lokacin ba tana karbar masa aman ya ki karbar komai da sharadin sai yaro ya samu lafia
Murya na rawa baba tsoho ya ce" y'ata ke ce a garin timiya? Ya jikin yaronki? Na koma ban same ku ba sai na yi adu.ar Allah ya sa ya warke
Ayya da murna ta janyo hannun Wardugu dake tsaye kikam ta ce" baba ai gashi, kana ganni soja ne, cikin ikon Allah magannin nan mun ji dadinsa, nima a raina kake, na nemeka Allah bai yi ba, kwanan nan na yawaita mafarkinka, a sifarka ta da hakan ya daga hankalina na saka aka nemo min inda kake, shi ne na zo na yi godiya sannan na yi salama kamar yanda na dauki alkawari,
Baba na murmushi yana kallon wardugu wanda shima zuwa lokacin ya risina, yana kallon tsohon yana kidaya shekarunsa a ransa, ya yi imanin a kadan ya linkasa uku da rabi,
Baba ya maido kallonsa wajenta, kafin yake bin dakin da yake zaune da kallo, ya yi murmushi bai ce komai ba
Ayya ta ce" Baba ka yi magana mana,
Baba ya dago yana dubanta ya ce" kaya y'ata, ki dubi dakin da nake ciki a zaune a yanzu, me ya rage min? Me zan yi da arziki? Kyakyawan karshe kawai nake nema, shekaruna dari da ashirin da uku a duniya a hasashe mai yiwuwa na fi,
Kallonsa kawai suke suna masu adu.a a ransu, adu.a suke da Allah ya datar da su da irin tsufan nan, wanda zaka yi ram da kai da carbinka,
Jikin ayya ya yi sanyi sosai , a hankali ta zauna a kasar dake dakin tana kallonsa, murya a sanyaye ta ce" haka ne baba, Allah ya sa mu cika da imani......
Aman na so na yi maka wani abin da zai faranta maka, da zaka aminta ma da mun tafi da kai mun kula da kai
Baba tsofo da kansa ke kasa cikin rawaninsa ya dago yana kare masu kallo, ya yi imanin wannan matar da muguwa ce da bata bi bayan alkawarin da ta yiwa talaka futuk kamarsa domin ta san bai isa ja da ita ba domin zamani ya zama mai abu shi ne sarki, shi ya isa shi ke da magana ya dora doka, aman du ta manta ta tako ta ci gari da gari, ta ratso sahara du dan ta yi masa godiya sannan ta cika alkawarin da ta dauka,? Sannan ya san ba yar yankan kai bace domin ba da kansu suke nema ba kawo masu ake har gida, shi kam ji yayi gaba daya ya samu nutsuwa a zuciyarsa da shawarar sa,
Murya a sanyaye ya ce" tabas ina da bukata mau girma baiwar Allah, sai dai ban san ta inda zan fara ba, banma san ko za.a dace ba,
Hankalinta ta maida kansa ta ce" Mecece ita?????????????........
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
1⃣5⃣
Baba cikin yannayin damuwa ya ce" me zai hana na baki auren y'a?
A nitse ayya ta ce" Auren Ya baba?
Baba tsoho ya ce" eh, domin shi kawai zan nema a bada yarinyar dindindin ,
Aman baba wace yarinya ce wannan??
Baba ya sauke ajiyar zuciya ya ce" yarinya ce mai tarbiya mai ladabi da biyaya, yarinya ce mai nutsuwa, bata da kwaramniya, inda aka ajiyeta ta zauna kennan sai an ce ta tashi, yarinyar nan ina jinta a raina tamkar yar da na haifa, a kulun damuwana na mutu na barta a wannan hali, tana cikin halin matsi dan kawai Allah ya yita *BAK'A* sai dai ni murnar hakan nake domin fatarta ya sa har ta kai warhaka sai dai har yanzu bata samu mijin da zai aureta ba a kauye ta girma sosai shekarunta goma sha takwas a duniya ,
Jim Ayya ta yi tana kallonsa, kafin take cewa " me dinka ce Baba?
Baba tsofo ya kalli Sarki dake kallonsa shima cike da rausayawa, da wani ne duda tsufanda in dai yana iya magana yana gane wasu abubuwan da gudu zai karbe makuden kudin da aka baza masa, sai dai shi bawan Allah ta yarinyar fake tare da shi tun tana yar shekara shida a duniya yake, irin tunanin da iyaye zasu kwana su tashi da shi na gannin yayansu sun samu mijin aure mai nagarta wanda zai kula da yayansu, toh haka baba tsofo yake kasancewa, du motsinsa itace a ransa, tambayar kansa yake ina? Ta yaya? Wanene wanda zai rike masa Agaishat mudin ranta cikin mutuntawa da kauna? Ya hanga ya hango bai samu ba, har almajirinsa ya tuntuba aman ya watsa masa kasa a ido, hakan ya saka shi dukufa wajen kai kukansa wajen Allah, yana rokonsa da ya bili masa da hanya ta inda baya zato baya tsamani, ya bilo masa da hanyar da zata zamo alkhairi gareta,,,,
Sarki ya ce" kanwar matana ce, Sunnanta *AGAISHAT*
Kana nufin farar buzuwa? Ayya ta tambaya
Sarki ya ce" buzuwar ce tabas, sai dai ita wannan Bak'ar buzuwa ce,
Ayya ta kai dubanta wajen Baba Tsofo da ya yi kododo yana kallonsu, kallonta ta maida wajen Wardugu dake tsaye ya tsareta da ido yana jiran jin me zata ce,? Ya san halin mamansa, ya san Ayya da daukarwa kai, !
Murya a sanyaye ta ce" Warduggggggggg..........
Fuskarsa a hade ya ce" Lalalalala,
Daga haka ya tamke fuska yana kallon su
Ajiyar zuciya ta sauke tana kallon kasa ta afka tunani (Tabas a al.adar Tubawa ba.a yiwa namiji auren dole, bake Wardugu, sannan idan namiji ya yi aure sai matarsa ta yi haihuwa kamar uku zuwa hudu kafin ya yi mata kishiya idan kuwa bata haihun ba sai ta dauki shekaru kafin ya yi mata kishiya, wannan haka ne ba ja, haka al.adar garin yake, ) Ayya ta kuma kallon su, ya zata yi?
A hankali ta ce" baba, wannan yaron shi daya Allah ya bani a duniya,
Sannan bai jima da yin aure ba,
Ban ki ba, ina so idan da hali a bani yarinyar a matsayin yar rikona, yar amanata, in sha Allah zata ci abinda na ci ta kwonta a makwoncin da na kwonta ko wani iri ne, kafata kafarta Har Allah ya bata miji, zan yi dukan abinda ake yiwa ko wace y'a na kaita gidan miji sannan zan bi dukan lamuranta a gidan miji mudin raina
Baba tsoho ya jima yana nazarin maganarta, baya shakun za.a bada AGaishat in dai sarki ya yi magana, damuwar shi ne: Agaishat zata so bin bakin fuska duda irin matsin da take ciki? Gida fa gida ne, sannan mahaifiyarta zata yarda da radin kanta a rabata da yarinyarta budurwa ba da wani dalilin aure ba ko dangi na jini haka kawai a tafi da ita tare da mutanen da bata sani ba? Ko wannan karon ma isar za.a nuna mata a kuma kwace mata *Y'A*?
Duda haka baba ya kai dubansa wajen sarki,
Irin kallon da baba ke yi masa sai da ya saka ya ji kunya, ya ce" abinda za.a yi, zamu kama baba a je da shi da ku baki daya ga mahaifiyar yarinya da mahaifinta, du yanda hali ya kama zuwa ya fi aike
Sun lamunce da hakan inda Wardugu ya kama baba a hankali ya mikar da shi sarki ya kama masa suka fito yana dan dingisa kafarsa har suka karasa wajen motar inda sojan nan ya bude wardugu ya daga baba a hankali ya saka shi gidan gaba sarki ya shiga suka shishige gaba dayansu Walyn da binsa da kallon meye kuma haka? Shima kallon Ayya dai yake,
Basu zame ko.ina ba sai kofar gidan Algabiitt
...................... .................
Anna, ki yi hakuri haka kin ji? Ki daina damuwarnan kin ji Anna?
Agaishat ta fada tana miko mata gurasa ta kasa da aka kawo sadaka gidan mutuwar
Anna ta lumshe idannuwanta bata karba ba ta bude tana kara bin yayan nata da kallo,
Mutuwar nan da aka yi bai saka Algabiitt ya yi sanyi a lamuransa ba, ya sako Agaishat gaba dole sai ta yi shafe shafe itama ya samo mata miji kamar yan uwanta tamkar damuwarsa ta yi auren ne,
Yarinyar bata isa ta wulga ba sai ya dura mata zagi
Ya hana a yi zaman makoki sai yayanta dake zagaye da ita
Amarya kuwa idan yau wannan ya zo ta ce dan uwanta ne , gobe sai wancen ya zo ta ce kaninta ne, ta mayar da gidan filin kawo kwartayenta ba tare da wani dar ba domin mai gidan ya bata lamuni....
Anna murya a shake ta ce" bana so ya kashe mini wani cikin ku,
Mariama ta juyo fuska du ta yi mata ja abin kuka ta ce" to ki biyo mu mu bar masa gidan mana, dan mi ba zaki bi mu mu yi tafiarmu ba? Kin san abinda ke daure mu a nan ke ce,
Hankalinta tashe ta ce" a duk lokacin da kuka ambata mini abubuwan nan biyu asalina da barin Algabiit bara ku ji na fada maku yau abinda nake ji! Ji nake tamkar lumfashina zai tsaya idan na ji an ce na bar inda Algabiit yake in dai ba da yawunsa ba, ji nake zan fada halaka, ji nake duniyara shi ne, ji nake in ba inda yake ba ba ni! Wani duhu ke rufe mini ido kaina ya dauki nauyi idan na takura sai na tuno wacece ni? Nakan fada damuwa mai tsanani juwa ta ringa dibana du idan aka yi maganar dangina, kun ji damuwata
Suke suke kallonta, Agaishat (Bak'a) kanta na saman cinyar Gaishat, Mariama na zaune gefensu, Fatimata na jingine da garu tana facing dinsu,
Jiki a sanyaye Fatimata ta ce" me ke damunki haka Anna? Wannan ba soyaya bace,
Mariama ta kallota ta ce" wace soyaya? Ai koda an yita a baya a yanzu Ya kasheta da kansa, Me ke damun Annarmu?
GAISHAT ta buda baki zatai magana sai ga Algabiit bugum ya fado dakin yana dan dudukewa dan tsayi
Direct ya zarce gurin Anna bakinsa na rawa ya ce" sai dai su tafi da ke da tsinaniyar yar ki! Ba wanda zai kama ni, ba abinda na yi!
Da sauri ta mike tana dafe kirjinta, tsinaniyar yarki ke mata yawo a kwakwaluwa, wacece kuma? Me aka yi? Su wa zasu tafi da su?
Bata kai ga tambaya ba ya duko ya dago Bak'a da gashinta ya mikar da ita,
Yawun bakinsa ya tatara mai cike da warin Sansani ya tofa mata a fuska ya ce" ga dan iskan tsohon da kike wuni wajensa tare da sojoji, to ki sani sai dai su kama uwarki
Janyeta Anna ta yi da karfi sannan ta yo fallon nasu da sauri dan jin lafia?
Gaba daya yayan nata suka biyota inda Algabitt ya labe yana leke yana kuma sauraron abinda ake fadi
Da kallo Anna ke bin su, sukai mata salama suka shiga gaisar da ita da yaren buzanci,
Ayya ta kalli wardugu dake karewa kowa na wajen kallo, ta ce" ban san bama da wani yare zamu tatauna da ita da alama buzanci kawai take ji
Anna dake tsaye ta ji komai abinda aka fada da yaren da ba zata ce ga sunansa ba, kuma ba yaren da suka yi da likitan nan a asibiti bane............................................