Bayan tafiyarsu da kamar minti ashirin, Wardugu dai na nan zaune yana bin kowa da kallo ta kafurin bakin glass dinsa,
Mintuna tsakani sai kukan jiniyar sojoji ta fara yin salama wajen,
Da farko tunaninsu ficewa zasu yi, sai dai abin kara yi masu salama yake,
Hajia Aisata dake zaune saman cinyar karuwinta suna shagali aka dokowa waya,
Dagawa ta yi da yannayin duniyanci ta ce" Ya?
Masu tsaron kofar Wardugu Place ne daya ya yi kiranta a tsorace ya ce" Hajia me motocin sojoji ke yi a kofar nan? Na ga sai jeruwa suke suna didirowa da alama wani suke jira,
Ai bata san lokacin da ta diro daga saman kafar mutumen ta ce" me me me ka ce? Sojoji? A nan?
Bata tsayin jin amsarsa ba ta fito da wani irin gudu ta ce" du wanda ya san da hoda gabansa ya yi gagawar rabuwa da ita ga arnawa a kofarmu!
Nan fa wajen ya rikice, mutane du suka tsorata,
Aka fara kokarin guduwa wasu na nufar motocin su da gudun tsiya wasu na auna tsayin katangar sai dai ba halin dirawa domin ga tsayi ga abin kama barawa an zagaye wajen da ita,
Du masu jan mayan nan suka aniya gudu suna boyewa wasu na watsawa cikin ruwa wanda kadan ta rage masa ya janye abinsa, manya manyan masu fada a jin wajrn suka fara nufarta suna tambayarta me hakan ke nufi? Dama ba da lamuncewar gwamnati ta bude wajen raba masu eh yane ba? Ba wanda ya daure mata a gwamnati?!
Ita dai ta cire dogon takalmi sai bi take table table tana kara goge dan sauran hodar da wani farin tishu ita da yarenta masu aikin wajen,
Du sun haukace sai ihu take yiwa mutane kan wa.inda tsiraicinsu ya bayanna sosai sai fadi take su yi maza su saka kayan da ya fi wannan,
Sannan da gudu wata bagwariyar yarinya ta fito da abaya ta kawo mata ta luluba mata daidai nan tuni sojojin sun cafke masu tsaron kofar sun fara tura su cikin motar wasu kuwa na tsare masu bi ta hanyar da wa.inda ke zuwa a lokacin,
Wani sergent ne ya kali abokinsa ya ce" yau fa akoy buro.uba a wajen nan, domin lamarin na gida ne, fadan gida ne,
Kai ya girgiza ya ce" ai ba na gida ba, ko na waye ta tarowa kanta dan oga ya yi mata tashi daya!
A guje ta karaso table din wardugu tana babala botiran rigar tana zuwa da mamaki mamaki haushi haushi ta ce" kai waye mai hular nan ne wai? Kai ana a yi maza a kawar da komai kai kana zaune kikam , to walahi bara ku ji kaf wajen nan dan na lura hoda ta coshe tunanin ku! Du dan iskan da aka kama da ita ba ruwana, tawa kaf ta wajen nan ta bi Wc! Ta hannayen ku kuwa ban sanku bama bale na san me kuka shigo da shi, kun kuwa san wajen da girma ba lale ne sojojin su yarda da ina iya control din kowa!
A hankali ya dago yana hangen yanda ake shan tsere da mutanen tsakar wajen fa sojoji suna yi masu cafkar fara suna yin waje da su,
Ransa ne ya kara baci , me ya kai su kokowa da su? Su saka lasifika su yi magana kan du dan akuyar da ya nemi gudu za.a watsa masa tire a gaz! Aman sai wani guje guje suke da juna harma su yi tunanin mu tsarensu ne!
Gilashin idonsa ya cire a hankali ya dago da jajayen idannuwansa ya sauke saman fuskarta , murya a dake a dage ya ce " aman kuwa da kin ci amanar clients din ki *AISATA*, na ji kuna fadin client sarki ne ke kuwa kina ikirarin ba ruwanki dan an kama shi da hoda yana zuka,
Mutuwar tsaye ne Aisata ta yi, mutanen wajen kuwa gannin mai maganar sannan ya karasa mikewa tsaye du ya saka suka rude abinka da mai laifi suka fara neman hanyar fita,
A rikice ta nuno shi da yatsarta ta kusan baba ta ce" Wardugu? Wardugu! Wardugu,
Ya ce" ki ajiye yatsarki da nuna da ita, ko ki hade yatsutsanki ki nuno ni da hannun baki daya, rashin tarbiya ne nuna baban mutun da yatsa Aisata!
Wani irin juya ta fara ji, hankalinta tashe ta ce" aman kai da kanka zaka tonawa wajen nan asiri? Ka fa san mamalakin wajen,
Sergent Kabir da ya shigo da sauri ya zo dan jin me Wardugu zai fada kiran da ya tura nasa ya ja ya tsaya ya sara masa,
Wardugu ya juyo wajensa ya ce" ankwa!
Da sauri ya mika masa, sannan ya kara ja ya kame,
A bainar jama.a Wardugu ya ja hular kansa ya cire ya nufota ya ce" Madame *MARAHUT AISATA* iko ya kama ki bisa laifin buda gidan badala, yada mugayen ayuka a boye, da siyar da hoda a fili kuma a bayane, ki yi shiru ko dukan abinda kika fada zai yi aiki kan ki, kina da damar tsayar da lauya dan kare kan ki ko kwato incinki.........
Yana fada ne yana sarkafa mata ankwa irin na an kamo barawo, kafi yake turata gaba da kansa ransa bace ,
Suna fitowa ya daga murya ya ce" lasifikha sergent!
Ai kuwa da gudu aka fita aka kawo masa,
Ana kawowa tuni yan jarida sun halarta sun fara dauka abinsu,
Wardugu na amsa daidai kunenta yana rike da ita hannunsana dama ya daga, a dake kalamai a rarabe ya ce" Duk wanda ya yi gigin guduwa daga wannan waje zai jawa kansa rigima, zamu saki batkonon tsohuwa (🤣🤪), koda kana da rashin lafia kan ka! Ku hade gaba dayanku tsakiyar wajen nan minti biyar na baku, du wanda bai zo ba tawa ce ni da shi!
Ji kake wajen ya dan lafa da iface iface, nan fa dan koke koken yan matan ya fara tashi,, wasu na dora hannayensu a kai suna ihun sun mutu sun lalace yau asirinsu ya tonu, wasu na kaico da tunanin mai tsaya masu domin dama ba wani abin iyayensu gare su ba , irin sun samu dan masu kudi ne suka zubar da tarbiya aji daraja irin ta ya mace suke bin su ana shan kida, wasu samarin sun sato motar gida ne an zo a more da yan mata haka ta ritsa su, wasu manyan mutane ne masu iyalai a gida suka baro suka dauko wata yar shilar suka zo a cashe, waje dai ya fara daukan kimtsi, waje ya yi tsit sai iza keyarsu ake ana waje da su,
Murya kasa kasa Aisata ta ce" Wardugu, ka bar ni na kirayi abanka,
Bindigarsa karama ya daure a kugunsa kafin yake turata itama ya yi mota da ita,
A wannan rana Wardugu bai nufi gidan su Alhinayettt ba sai wajen karfe bakwai na dare,
Yana zuwa bai fita a motar su ta sojoji ba kira kawai ya yi suka fito ba tare da ya yiwa kowa magana ba suka duru a motar ya ja, inda Alhinayettt ta bi su da kallo ta koma tana shan dariyar mahaifiyarta na fadin" yau fa akoyta, Alhinayettt yau ana rigima a garinnan, kina ji shiru ? Ba galama basu fara kade kadensu ba
Alhinayettt ta yi dariya ta ce" Anna (Matar babansu ce), ai sai adu.a kawai, Wardugu Wardugu Kowa Wardugu, ni dai zan yi ta yi masa adu.ar Allah ya tsare shi........
Gidan Ayya ya kai su, wace ke zaune tsakar gida da waya a hannunta sai dokawa wardugu kira take aman ba.a dagawa,
Ai tana gannin sun sauko ta nufo wajen su sai dai bai tsaya ba ya yi gagawar juyawa ya fece abinsa, domin ya sani ne yanzu har an fara zuwa wajenta, bayan ta sani shima bai isa ba , shima yana bin dokar ne !
Gidansa ya yiwa tsinke,
Nan ya tarar da Mota uku a ciki bayan na kofa da aka hana shiga,
Mita daya dai ta mahaifiyar Walyn ce, biyun ne bai gane ba, dan haka ya shige bangarensa yana haharde kafafuwa yana so ya je ya zauna ya kashe du wata waya dake yi masa kuka a kunne ta hana shi sakat sai doko masa kira ake shi kuwa ba wanda zai daga kiransa domin ba wanda zai saurara, ba tonon asiri ne ya yi niyar yi masu ba, ba huce haushi ne ya yi niyar yi wa mahaifinsa ko matarsa ba, abin ne ya daje shi, ya diro masa a lokacin da bai yi tunani ba, tashin hankalinsa shi ne...ta ina ake shigo da hoda har ta gama gari haka? Ya sani ne sai sun sha masifa fa lauyoyi, inda ya san ya shige gabansu harda dan gidan banban lauya baki daya, in ya yarda ya ce a saki mutane, iyayen yara da manya masu daraja zasu sako shi a gaba ace dan da yaronsa ne !
Kansa ya shiga shafawa ya bude bangarensa ya shige ,
Kamar koda yaushe, sansanyen kamshi ne ya taro shi, wannan fa ba.a wasa da shi,
Agogon hannunsa ya fara kuncewa yana kokarin karasawa cikin dakinsa na baci dan ya samu ya yi wanka,
Wardugu" ta yi kiran sunnansa tana mikewa ta nufo shi,
Tsayawa ya yi yana kallonta, domin yanzu ya dan saka mata haushinta da yake ji na ta tafi ta bar su wai ba zata hada numfashi da yar gidan Anna ba,
Karasowa ta yi ta shige jikinsa du da yanda yake tarewa,
Murya a kasalance ya ce" Walyn bari na yi wanka , aiki na yi jikina ba tsafta,
Kai ta girgiza ta kara shigewa jikinsa tana rungume shi sosai a jikinta ta ce" baka wari kuwa Wardugu, kamshin turarenka na nan,
A hankali ya raba jikinsa da nata ya ce" aa tsaya na yi wanka, na yi zufa sosai kin ji?
Ya karasa yana mai zaunar da ita saman tsareren bed dinsa mai ruwan zeba,
Bayi ya zarce ya samu ya shige kasan shower,
Ruwa mai sanyi ya sakarwa kansa a jikinsa dan yana son jin sanyi
A hankali ya lumshe idannuwansa yana jin sanyi mai dadi na ratsa shi,
Sai da ya gama ya yi wanka na kirki ya dauro alwallah ya fito daga bayin , zuwa wannan lokacin har karfe tara ta kusa cikewa,
Yana fitowa , Walyn ta kara nufo shi
Tsayawa ya yi yana kallon yannayinta, magana ke tafe da ita domin batai masa yannayin tana bukatarsa ba,
Dan haka ya zarce ya dauko jalabiyarsa ya saka ya dauko salaya ya shinfida yana kokarin tayar da sallah,
Wardugu mana! Ta fada da yannayin damuwa,
Juyowa ya yi yana kallonta bai amsa ba,..
Ta karaso ta ce" su Mamanmu ne fa ke zaune a falona ka fito ku gaisa ,.
Wardugu yana kallonta, mamansu, har wannan lokacin?
Bai bata amsa ba ya tayar da sallarsa, dama dan ya yi shafa.i da wutiri ne,
Zama ta yi har ya karasa, ya zauna ya yi doguwar adu.o.insa na tsari da komai ya mike ya cire rigar daga shi sai gajeran wando ya yi bismillah ya haye bed,
Da mamaki take kallonsa, ranta ne ya baci ta ce" aman baka ji wace nace maka tana jira ba?,
Domin ta sani ne, yana mugun daraja mahaifiyarya, ko gaisar da ita zai yi sai ya dan duka, aman yanzu ta fada masa ta ga ya wani kwonta abinsa,
Wardugu ta kara kiransa tun karfi,
A fusace ya dago zaune , murya a bace ya ce" ba zan je na gaisar da mamanki ba, na gaji baci nake son yi ki fice mani a daki!
Ido ta kwalalo tana kallonsa, kafin take juyawa ranta in yayi dubu a bace yake, tana son tsayawa ta ja maganar aman wani abin na hanata, dan kuwa dukan alamu sun nuna idan ta yarda ta kawo masa raini komai na iya faruwa ,
Juyawa ta yi tamkar zata tashi sama ta fita a dakin,
Karamar wayarsa ya bude,
Sheik ibrahim ya danawa kira,
An jima tana ringin kafin yake dagawa da salama,
Wardugu ya gaisar da shi da tambayarsa jama.a,
Sheik ya amsa yana mai tambayar Wardugu Aiki,
Wardugu ya amsa shi a nitse ya ce" Malan, a kara saka mu a adu.a,
Sheik ya yi murmushi ya ce" Wardugu , na ganka a tv, fatan Allah ya tayaka, Allah ya baka ikon yin aikin kirki, sai dai zan kara fada maka, a duniya karka ce sai ka birge kowa, ka yi lamarinka domin Allah, kar ka saka fushi ko gaba dan Allah ya baka dama mai girma ta jan wanda ka yi niya, ka ci gaba da kawar da kanka a kwadayi , sannan ka ci gaba da jan istighfari kana kaiwa allah kukanka ka ji?
Wardugu ya amsa a mutunce sukai salama,
A hankali ya lalubo cazbaharsa fara kar tana ta kanshin turaren ruwa ya shiga ja daga kwoncen yana ta jan astghfari,
Me mijinki ke takama da shi a duniya Walyn? Ya rasa wa zai rufe sai aban iman? Ko dan yana auren yar yayata ai sai ya daga masa kafa, dan kawai ya kama da shi a wannan wajen, wajen ba na ubansa bane? Zance wajen sunnansa ma gare shi! Me yake tunani? Dan yana sanye da rigar iko shikennan ? Ai idan shine yau gobe ba shi bane zai ringa yiwa mutane rashin mutunci! Tunda haka ta faru muke gidannan aman ya zo ki wani zo ki ce wai ya gaji? Gajiyar kaniyarsa, mu da muke nan bamu gajin bane? To idan mijina ya kwana a cel nima na dauki alkawain sai na tozarta Wardugu sai na saka wardugu ya shiga uku, sai na
Aunty! Walyn ta fada tana daga murya sosai,
Da yatsarta daya ta ce" ke a wa? Wacece ke? Kike ikirarin tozarta Wardugu bayan Allah ya rike? Ke kin san da za.a shige shi da an shige shi ba yau ba Aunty! Wardugu baya zuwa maula, hukunci kuwa idan ya kama zai yiwa ko wani dan buro........ba, meye? Takamarki ki yi masa shari, ki hada shi da malame, ko ki same shi ta hanyar abin duniya?
Ban ce sihiri ba zai kama shi ba domin wanene shi, sai dai na miki alkwarin tunda kika fadi haka , sai dai mu mutu baki daya,!
Mahaifiyarta ce ta kasheta da mari, rai bace ta ce" kan namiji? Kan namiji zaki ciwa kanwata mutunci? Namijin ne ya kai dan goyo har haka? Ke Wardugun da kafin aurenku ma sai da ya karya maki hannu sau biyu shine kike daga jijiyoyin wuya dan ance za.a taba lafiarsa? Kin manta dan ya kauce ki malaki wannan daula na yarda yake tata maki rashin mutunci? Idan kin canza ra.ayi na sani da wuri dan Ubanki!
Wakyn dake yashe tun marin magaifiyarta, jikinta a mace, takan mance du wani kudirinsu idan tana tsaye gaban gwarzonta, namiji ne Wardugu, can dama tana sonsa sosai, damuwar kuna tana son kudi sosai!
Mu.azam, tashi ka kai ni ya sha maganin bakin nan ,
Ayya ta fada tana nuno masa wani dan kuli wai maganin baki ne dan kar baki ya fada masa
Mu.azam dake zaune kafa tankwashe Agaishat na koyar da shi bakara ya dago da mamaki yana kallo Ayya,
A hankali ya ce" Ayya, idan muka yarda muka fita a yau fa kama mu za.a yi a rufe, sai karfe takwas na safe za.a tsayar da kamen nan, ki rufa mana asiri Ayya kin j?
Ayya ta zaro ido ta ce" dan ubansa a rufe mun, bafa zai yi baci ba sai ya sha maganin bakin nan yau yanzu yanzu dan haka tashi mu je Mu.azam,
Mu.azam ya mike yana ayyana ta faru ta kare a ransa, dan ya san in dai suka fita titi za.a kama su ne, za.a rufe su, daga shi har Ayya har Agaishat din,
...........to fah🤣🤪🤪🤪🤪✌🏼
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
2️⃣7️⃣
Mu.azam ya ce" Ayya, ki bani na je na kai masa, kin ga ko an kama ni kadai ne za.a kama,
Ayya ta ce" yo kai na d'a bane, a hada har mu a rufe, ba yace doka ta hau kowa ba? Na tabata an hada da iyayen mutane a wajen,
Mu.azam kam ya rasa ya zai yi da Ayya , ta kuwa coge kofar daki inda Agaishat ma ta fito tace ba zai yiwu Ayya ta tafi ta barta ba,
Kallon agaishat yake kasa kasa, a hankali ya ce" idan aka rufe ki Agaishana, ba zan iya hakura ba, kar ki biyo mu na roke ki,
Irin na yara ta yi masa da kafadarta irin ta kiya, tama rigayi kowa karasawa wajen motar bayan ta amshi maganin bakin na hannun Ayya,
Haka Mu.azam ya fitar da motar dake da lambar Wardugu, ya dauko carte dinsa ta shaidar shi likita ne, da carte didentité dinsa,
Fitowa ya yi da motar Ayya ta shige baya ta hakimce, Agaishat ta shiga gaba aman a ranta a tsorace take, tana tsoron sojojin garinnan, daman ba.a saka soja a lamari a niger sai abin ya baci, su fa ba ruwansu hade kowa suke, idan ka yi masu gardama su tataka banza su barka nan zubde tamkar kayan wanki,
Tuki yake zuciyarsa kuwa sai adu.a yake, Agaishat ma adu.ar kawai take inda Ayya ke kara buga lambar wardugu aman a kashe, bata shigama bale a dauka,
Danja na tsayar da su aka haske su da cocila dall a idannuwansu,, gaba da baya sojoji suka zagaye su har mutun uku,
Na kusa da direba ne ya kwonkwasa kofa,
Mu.azam ya bude yana dubansa,
Mutumen ya ce" motar Gn ce Oga,
Ya ce" eh na gane ai,
Ya ce" malan daga ina , kuma ina zaka je? Wa ka dauko? Sannan ka bude mana bayan mota zamu yi bincike,
Mu.azam ya fara bude masu motar, sannan cikin nutsuwa ya ce" ina tare da mamanmu ne, mahaifiyar Wardugu da kanwarmu Agaishat sai ni kuma amininsa ne, daga gida muka fito zamu je gida wajensa bisa umarnin mamansa,
Menene shaidarka? Sojan ya tambaya ba alamun wasa,
Mu.azam ya mika masa cartocinsa, sannan ya sauke madubin bayan ya dayan ya leka wajen Ayya,
Kwarai kuwa itace, waye bai san Ayya ba? Mahaifiyar General,
Gaishe da ita ya yi cikin mutuntawa ya ce" yi hakuri mama muna bisa aikin mu ne, ki tabatar mana da abinda ya fada,
Ayya ta ce" eh haka ne, ina son gannin Wardugu me yanzu yanzu,
Sojan ya gyada kai yana kallonta,
Wanda ke bincika cikin motar ya shaida masu ba komai cikin motar, dan haka ya mika masa takardarsa ya basu damar su fice
Cikin ikon Allah haka sukai ta haduwa da sojojin nan suna kara titsiye su ,
Harda wanda bayan dukan bayannan nan yace ai shi bai wani san Ayyar ba a bashi shaidar da ta fi haka,
Nan fa aka sha rigima da kyar masu taya shi suka tsawatar masa ya batsu suka tafi,
Tun abin karfe tara sai kusan sha daya suka karasa gidan Wardugu nanma suka tarar da wani balakin an hana iyayen Walyn fita sai dai su kwana a nan in kuwa suka fita aka kama su toh su suka gano, sun izata sai balaki take kan wardugu ya fito ya raka su ko ya basu shaidar da zata sakasu su tafi har gida lafia,
Suma su Mu.azam sai da aka titsiye su kafin suke samun shiga gidan,
Mu.azam na tsayawa ya sauke ajiyar zuciya yana kallon hajia rigima, domin Ayya ta hade rai ta yi kicin kicin da fuska tana kallon yanda suke tsatsaye suna ta magana suna tafa hannu suna balaki,
Mu.azam ya ce" Ayya, kar ki kula koya na roke ki,
Ayya ta yi murmushi ta ce" oh yarona, yanzu kai ke yi min gargadin kar na kula kowa, ai ka san bana kula mutumen da bai iya tsawatarwa zuciyarsa ba!
Bude motar ta yi ta sauka,
Ai kuwa tunkarar wajensu ta yi direct ba wani tsaye tsaye,
Tana zuwa ta ja ta tsaya itama tana yi masu kallon da suke mata,
Da yake akoy wuta ko.ina haske ya garwaye gidan kowa na gannin kowa ne,
Ayya bata fita sai ta shirya ko fitar da a rikice take ne, dan haka yanzuma sai baza kanshi take, ga lufayarta ta nada mai ruwan ja da baki, ta sha awarwarenta na zinariya,
Walyn ce ta ce" ina yini,
Ayya ta kai dubanta wajenta ta ce" lafia, sannan ta mayar da dubanta wajen iyayen Walyn din tanai masu kallon ido cikin ido,
Mahaifiyar walyn ta miko mata hannu ta ce" Hajaju ne, uwar gidan *MARAHUT* ke ce da tsakiyar daren nan??
Ayya ta sakar mata murmushi ta mika mata hannun itama ta ce" wa.alaiki salam maman Walyn, ke ce a gidan Wardugu da wurin nan haka,
Kanwar maman Walyn ta kali Walyn ta kuma kallon sirikan biyu, ta juya bangaren Walyn tana ayyana taf, lale ana cakwakiya a gidan nan,
Ita kuwa walyn kitson kanta kawai take sosawa, susar da bata san ko ta meye ba,
Ayya ce ta fara cika hannunta ta kuma kallon Walyn ta ce" Aa, Walyn yaron nan yana nan ne dai ko? Bara na shiga na gani Wardugu sarkin aiki!
Juyawa ta yi ta nufi bangaren Wardugun cike da isa, sai a lokacin Mu.azam ya lalaba Agaishat ya cire mata tsoro suka fito daga motar,
Mu.azam ruwan sanyi sai ya nufi wajen su dan gaishe su,
Walyn ta daga ta watsar da idannuwanta sannan ta zabgawa Agaishat wata muguwar Harara da kallon kyama ta juya tana riko hannun mamanta suka koma bangarenta,
Agaishat dake dafe da kirjinta jin yanda zuciyarta ke dokawa Mu.azam ya kallo,
Murmushi ya sakar mata ya ce" mu je Matar Mu.azam,
Ido ta zaro kafin take daga kafa da sauri ta yi gaba tana jin wata kunya kunya da wani irin abu game da Mu.azam din, yakan mantar da ita wacece ita ta halin nuna mata itama mutun ce mai cike da cikeken inci, yana yaba kalar fatar jikinta ta hanya kawatata da kalamai masu tsari da sence, yakan ce Allah ya datar da shi samunta, ita Agaishat yar gidan Sofo? Tana so ta biye masa tana tsoron ko wasa yake mata? Tana son ta yarda tana tsoron yan birni,
Ayya na shiga ta zarce har dakinsa na baci tana fadin" ina kake janyau, ka hargitsa mana gari ka lafe a gado, tashi tashi kaima ka yi kwanan zaune dan nema kawai!
Da wani irin sauri ya mike ya diro ya warci doguwar rigarsa yana faman sakawa ta shiga dakin,
Wardugu ya ce" Ayya, wai yaushe zaki dauna shigo min haka zaraf kawai? Me ya fito da ke a tsohon faren nan? Ya aka yi kika ratso sojawan hanyar nan? Wa ya kawo ki?
Maimakun Ayya ta bashi amsa sai cewa ta yi" baka da sutura a jikinka ne kake kwonciya Wardugu?
Wardugu ya dafe kansa ya furrta" Ya Allah,
Bakinta ta yatsina ta ce" fito ina jiranka
Sai da ya saka kayansa ya biyo bayanta,
Yana fitowa ya ga Mu.azam, da bakuwar nan ta ayya da shi ba zai iya fadin sunnanta ba dan bai wani rike ba,
Sai dai mamaki yake, yanzuma wasu kayan ne jikinta, shi abinda ke bashi mamaki yaushe ta iya saka kayan tubawa har yake bin jikinta haka? Yaushe ta iya saka kayan kansa nema ?
Kawar da kansa ya yi da sauri yana yatsina bakinsa yana ayyana ina ruwanka yo, ba dai Ayya ta daure mata ba?
Ayya ta karbi kulin maganinta ta umarci agaishat da ta bude frij dake nan falon ta fauko ruwan roba
Agaishat ta nufi frij tana tambayar kanta ina wajen budewar yake? Domin ba irin na gidan Ayya bane, wannan wani glass nema a jikinsa ko.ina tar tar yake ana hangen abubuwan dake ciki tar sai dai ba lale ka san wajen kunawarsa ba,
Ja ta yi ta tsaya tana kallo,
Ayya dake jira ta kallo wajenta ta ce" Agaishta kawo mana,
Agaishat ta juyo tana raraba idannu ta ce" Ayya, ina zan bude??
Wardugu ya girgiza kansa, Mu.azam ya mike ya je ya nuna mata ya bude mata, ta nuna masa wanda take tunanin ruwan ne?
Mu.azam ya ce mata" wannan ai jus ne, gidansa da kamarsa yake yannayin ruwa, aman kin ga jerin ruwan nan,
Nan ta dauko suka dawo wajen Ayya dake ta yiwa Wardugu fadan ya kwonta bai ci abinci ba dan ba sai ta tambaya ba ta sani ne kwonciyarsa zai yi, aman kwata kwata bata sako maganar matarsa ba ko iyayenta, bata da wannan lokacin,
Wardugu dai kallonta yake, ta bude ruwa ta tsiyaye fiye da rabi ta zuba maganin ta girgiza ta mika masa ta ce" shanye,
Wardugu ya cee" Ayya meye kuma wannan
?
Ayya ta ce" Wardugu, magannin baki ne, bakin mutane, ka san baki fa ya fi maye mugunta, baki ai ba dan uwa bane, bare yau ka janyowa kanka maganar mutane
Robar ya rike a hannunsa ya ce" Ayya, bayan walahaulan da nake yi kuma dai kin bani wannan jike jiken naki?
Ayya ta ce" walahaula hanyarta daban, wannan ma nasa daban, kai harda garin hantiti nake tafe, maza shanye ka dauko min buta a bayinka na zuba maka ka yo wanka ka turaru sai mu juya,
Ido ya zaro yana kallonta, kafin ya maido dubansa wajen Mu.azam da irin kallon kai ka kawota ko?
Mu.azam ya juyar da kai wajen Agaishat dake zaune kasa yana kallonta, domin kallonta na saka shi nishadi
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
2️⃣8️⃣
Bani da bakin da zan yi godiya a irin tarin kulawar da kuka nuna, da tashin hankalin da kuka nuna na wannan abin da ya faru, kunya ta kama ni, na ji kunyarku sosai na irin hada ni da Allah da kuka yi, wacece ni? Ni ba kowa bace da zan ki yin hakuri dan haka nake shaida maku ga *BAK'A* . Daga taku yar mutan niger
Kun yi sake , kuna gani tana zuwa ta shige dan ta samu ganninsa aman mu tun da yama muke zaune, a matsayin mu na iyayen matarsa yace ya gaji ba zai fito ba, kina ganni da takama bayan ta fada mana magana ta shige abinta,
Auntyn Walyn ke fada ranta na kara baci,
Mahaifiyar Walyn ta ja tsaki , ta ce" koma me take takama da shi ai mijin ya nuna mata iyakarta, yanzu ba da kishiyarta bace yaronta ke fada? Banza ita har ta isa ta nuna ita wata ce? Bayan an ci mata mutunci kowa ya sani?
Walyn dake zaune, gaba daya zuciyarta ke wani irin tashi, ta rasa me ke damunta kwanakin nan takan tsinci kanta a irin yannayin rashin jin dadin jiki, bata iya kara furta masu komai ba ta mike ta je dan ta saka a kara tsaftace masu wajen da zasu kwana, domin ba zata lamunci a rufe iyayenta ba, za.a samu matsala sosai,
Sai da aka sha rigima da Wardugu ya shiga wankan hantitin da Ayya ta jika a butarsa ta karfe,
Yana yin wankan ya fito yana jin yanda yake warin magannin, sai dai yana fitowa ta kuma tare shi da hayakin Hantitin nan yana ta bade shi ,
Jajayen idannuwansa kawai yake binta da su, in ba Ayya ba, wannan uwar gajiyar da ya kwaso ta zo ta tirke shi da wannan abubuwan? ,
Tana gamawa ta fita fallo da hayakin bayan ta debo turaren wutar dake jere saman coiffeuse din dakin tana tafe tana dan sakawa yana tashi a hankali,
Kansa kawai ya girgiza, ya cire jalabiyarsa ya saka rigarsa mai karamin hannun wace ta baiwa jikinsa damar bayanna ya saka wandonsa dogo fari na jalabiya saman gajeran ya fito,
Ayya dake kallon Tv, Mu.azam kuwa sai wani kara shigewa Agaishat yake yanai mata labari kasa kasa, wanin ta zaro dara daran idannuwanta, wanin ta dan yi murmushi, wanin kuwa sai dai ta rufe fuskarta da hannayenta wai kunya take ji,
Galala ya yi yana kallon kusancinsu da kuma yannayin su,
Ayya ce ta juyo wajensa , sai dai ranta ne ya baci gannin irin rigar da ya fito da ita, ita kam ya zatai da wannan sakarar dabi.a ta wardugu ta saka kannanun kaya? Sam ba al.adar batuben mutun bace, Batuben mutun yanda mace zata ji kunyar bayannar da jikinta haka shima namijin, sun fi saka manyan kaya sukan yi rawani ko su aza hula saman kansu, suna saka kananun kaya irin na zama aman dogon wando har kasa, riga mai mutunci su yi zanzaro abinsu, aman fa siri batube sai mata nai, shi ya saka take mamakin Wardugu, gatsai gatsai sai ya bi gari da wando daidai gwuiwa, riga mai yankeken hannu har yana wata takama,
Rai bace da yaren tubanci ta ce" Wardugu ! Nigey medi nubazzu ? Ay kubu nukoy ? Anna gnuduro indi hadin ? ( Wardu! damme bakajin magana , wannan wane irin rigane ? Idan mutane suka ganka me zakace?),
Wardugu ya kalli rigar jikin nasa, kansa ya shafa wanda haka kamar ya zame masa jiki, ya juya ya sako wata riga a saman wannan duda haka bai bala boturanta ba,
Yana dawowa ya zauna yana kallon Ayya,
Ayya ta girgirza kai ta ce" a gaskiya wannan abin sam bai yi ba, kai ba wani karamar kira ba , ka wani saka kananun kaya, yanzu haka a haka sirikanka suka ganka wardugu? Salon a fita da kai a baki ko?
Wardugu ya lumshe idannuwansa ya bude ya ce" basu ganni ba,
Me kake nufi da basu ganka ba?,
Wardugu ya daga kafada ya ce" ai na gaji ne, sai idan na huta Ayya,
Da kallo take binsa, a sanninta yana matukar jin kunyar iyayen matarsa yana darajasu, ko dan irin yanda sirikan namiji keda matukar daraja wajen mijin yarsu a al.adun tubawa, domin kuwa suna da dama sosai a kan mijin yarsu, aman yau yace wai ya gaji bai je ya gaisar da su ba? Ta so ta tsawatar sai kawai ta kyale, domin dai Walyn da Wardugu auren so suka yi, shi bai taba kawo mata karar matarsa ba, itama bata taba kawo masa karar rashin girmamata da Walyn bata yi ba, ai ido ba ma.auni bane abin duba ne, yana gani kuma yana sane, dan haka ta watsar ta mike tana duban Agaishat ta ce" ku tashi mu tafi kar mu kwana a gidan nan kun ji?
Wardugu ya kaleta yana talabe habarsa, ya ce" Ayya, ai yau sai dai ki yi hakuri da gorin wai kin zo gidana, yau kwana ma zaki yi Ayyar wardugu,
Ayya ta zaro ido tana kallonsa, ta ce" kai, ka rufamini asiri, ni na kwana a gidanka wardugu? Aa aa, ka tashi ka mayar da mu da kanka man,
Wardugu ya dubi Mu.azam ya ce" kai, zaka bado hankalinka nan ne? Bakin karfe dayan dare dokar ba wani karbar uzuri, motocin yan tafiya kawai za.a bari su je masaukinsu, suma sai dai su waye a can, ba zai yiwu ni na karta dokarnan ba Mu.azam zaka saka baki ko sai na ...
Mu.azam ya taso yana dariya ya ce" Ayya, karfe daya saura kadan, ki yi hakuri, mutuncinki, girmanki ya fi karfin ki je cel Ayyarmu, kuma ke ke fadin ya yi aikinsa tsakani da Allah a rayuwa, ki yi hakuri Ayya,
Ayya ta yi shiru tana kallonsu,
Dubanta ta kai wajen Agaishat, ta maido wajen Wardugu,
Kanta ta girgiza ta mike ta karaso wajen Agaishat ta kama hannunta ta ce" tashi mu je bangaren mata,
Agaishat ta mike tana biye da Ayya,
Mu.azam ya dan yi taku dan raka su Wardugu ya riko hannunsa,
Mu.azam ya dawo da baya ya ce" namiji, bangaren Walyn fa zasu je?
Wardugu ya ce" eh na gani,
Mu.azam ya ce" anya kuwa za.a kwashe lafia?
Wardugu ya yi murmushi, ya maida dubansa wajen Mu.azam da kyau, kallonsa yake yana karantarsa,
A nitse ya ce" me ke damunka da ita? Batai maka kankanta ba? Me ke jan ra.ayinka wajenta? Ko bakin nata?
Mu.azan ya dago da sauri yana kallonsa, Wardugu, yanzu mutun yanzu ba mutun ba,
Mu.azam ya ce" ban gane maganarka ba,
.......
........................
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
2️⃣9️⃣
Wardugu ya shiga dan shafa sajensa, ya gyada kai ya mike yana dan nuna alamun zan kamaka ne ya yi ciki abinsa
Mu.azam ya bishi da kallo, ya maida kansa yana duban wajen kananun fitilu fararen dake kara kawata dakin,
Murmushi ya yi shima ya lunshe ido a ransa yake ayanna zan so na rayu da ita koda na yini daya ne
Ayya na zuwa bangaren Walyn ta yi salama , ba wani hayaniya ko nuna isa ta ita mahaifiyar mai gidan ta samu waje ta zauna tana duban Walyn ta ce" Walyn muna son daki ni da y'ata , muma kwanan gidanki yau ya kama mu,
Walyn ta mike ta nufi wani dakin ba tare da ta ce komai ba, inda mahaifiyarta kuwa sai ta fara hura hanci ance gidan yarta,
Bata jima ba ta dawo ta ce" ga dakin an gyara Ayya,
Ayya ta mike Agaishatma ta mike suka nufi dakin da aka nuna masu
Suna zuwa Agaishat bayi ta nufa ta dauro alwallah,
Da nadin nan nata ta shinfida darduma ta tayar da sallar nafila domin dare ya yi sosai ya raba, ita kuwa yanzun ta zame mata jiki sai ta yita take iya rintsawa komai dare,
Kuri dai suke zaune suna kallon juna kowa da kudirinsa a kan dan uwansa, ita auntyn walyn mamaki take ashe wardugu har mahaifiyarsa, yo har mahaifiyarsa mana gashi itama dole ta kwana a gidan?
Dare ya raba , karfe biyu da rabi yayi aman wardugu ya kasa rintsawa,
A hankali yake sando ya sauka daga bed din domin nan Mu.azam ya zo ya kwonta bayan sun sha rigimar ba zai kwanar masa a gado ba yace shi kuwa nan zai kwonta,
Yana kokarin fita ya ji muryar mu.azam ya ce" ina zaka je?
Wardugu ya juyo da sauri, ganninsa zaune dare dare saman bed din ya saka shi zabga masa harara ya ja tsaki ya ce" matarka ce ni da zaka wani motsa dan na motsa? Wajen Walyn zan tafi
Mu.azam ya zaro ido ya ce" aman Wardugu baka da mutunci, wajen Walyn fa kace, bayan ka garza rashin mutuncin nan idan walyn ta kaleka komai jarabarka lale lale bata da zuciya!
Wardugu ya kama haba irin mamakin nan, ya ce" kai aman baka da mutunci, ohk dare ya raba kowa ya samu nutsuwa yana shara baci ni ina nan juye juye sai ta ki kulani dan na bata mata? Da a yau da asuba zan kara aure walahi talahi a masalaci!
Mu.azam ya zaro ido yana kallo Wardugu ya fice a dakin yana wata irin tafiya na ya kumsa masa haushi,
Kai ya girgiza ya koma kwonciyarsa
Wardugu na shiga bangaren ya tarar da su still nan saman kujeru, Walyn sai gyangyadi take, mahaifiyarta ta fara bacin itama , auntyn kuwa sai dan kada kafa take ,
Dakewa ya yi abinsa ya dan yi gyaran murya irin bai ahigo din nan ba, kafin yake yin salama ciki ciki ya shigo gaba dayansa
Su duka farkawa suka yi, yanzunma ya cire rigar ta sama sai mai karamin hannun hakan ya sa iyayen Walyn din saurin kawar da kansu,
Da idonsa ya yi mata magana, da idonsa ya isar mata da sakonsa kafin yake juyawa ya koma bangarensa,
Yana fita kasa kasa maman Walyn tace" Walyn, mijinki abubuwan da ya tara suna da yawa fa, shi ne rashin mutunci, shine fada, shine rashin kunya!
Walyn ta lumshe idannuwanta ta mike ta nufi kofa bata ce da ita komai ba
Auntyn walyn da ta kume da haushi itama bata furta su ci kansu ba ta kawar da kanta tana dan kada kafa , niya ne ta yi yau ba zata yi baci a gidan Walyn ba!
Walyn na zuwa ta yi niyar nufa dakinsa sai dai ji ta yi ya riko hannunta ba tare da ya yi mata magana ba sun nufi dakinsa,
Suna shiga ya shiga kokarin janye zip din doguwar rigarta ta atampa,
Tana tsaye tana kallonsa ya janye ya cire mata tana kallo yake kokarin janta bayi domin mafi yawancin lokuta haka ne ida zai sadu da ita sai sun je sun salo wanka kafin yake baje kolinsa,
Ja ta yi ta tsaya tana dubansa, kwarai ta so ta kiye masa sai dai ba zata manta wani lokaci da ta ki karbarsa ba irin yanda suka kwashi tsayin lokaci yana daure mata ba shi ba ita a harkar har sai da ta yi ta fama kafin ya sauko,
Rai a dan dagule ta nuna ai ita ba sai ta yi wanka ba,
Wardugu ya yi kalar tausayi ya ce" walyn wardugu, me yasa ba sai kin yi wanka ba? Kinga jiki da danshi danshi ya fi dadi tabawa😌,
Kanta ta juyar ta shiga kokarin hana kanta garza masa rashin mutunci, a sama take kwarai take tausar kanta kar ta saki hanya ta hanyar karta masa rashin mutunci,
Binsa ta yi suka yo wankan,
Suna fitowa ya jata saman bed domin shima yana so ya yi ya jishi ya saku,
Da sauri sauri ya shiga romancing dinta, sai dai ya lura bata bashi hadin kai domin sai dan zile masa take, hakan ya saka shima ya zo mata kawai kai tsaye wanda hakan na wahalar da ita ainun, idan a dadi suke yakan bita a slow da dabaru ne aman yanzun shima sai ya je ya darza son ransa,
Yana samun nutsuwa ta shiga tura shi,
A hankali ya dagata yana duban yannayinta
Rai bace ta ce" sai yanzu ka san da anfanina ko? Bayan ka gama wulakantar da ni da iyayena? Wardugu yaushe zan yi daraja a idannuwanka? Yaushe zaka daina wulakantani kai tsaye ? Dan ana fadin kai rigimame ne ai na yi tunanin kana iya zubawa kowa rigimarka banda ni!
Walyn,
Ya fada a hankali, kafin yake cin gaba" ki yi hakuri kin ji? Dare ne ki daina daga muryarki, sannan ko ba dare ba na fada maki ki daina magana tun karfi har tana fice tawa amo, mace kike, yar kwalisa ba wai wata kara zube ba, sai da na yarda da class dinki kafin na dauko ki, ki yi aiki da iliminki mana? Nifa ba ni na yi kamen nan ba! Aiki ne , doka ce ta hau du wani mai laifi,
To kawai dan nine sarkin son kai sai na ware mijin auntyn matata?,
Wardugu, kana da ikon warewar, in ka ware ba wanda zai daga maganar , kana da ikon zuwa ka fitar da shi a yanzuma ba wanda ya isa ya ja da maganar,
Wardugu ya tashi zaune, tuni hankalinsa ya fara tashi ya ce" kina nufin in na je na fido shi shikenan nine general Wardugu ba wanda ya isa ya ja da ni?
Walyn ta kale shi ta ce" karya na yi ne?
Wardugu ya girgiza kai ya ce" a niger, a duniya ba wanda ya isa ya zo ya titsiye ni walyn aman in fa a hanyata ta dawowa daga fido shi na mutu na tarda general din baki daya? Ya zata kare min? Shikennan dan ina tsoron bacin ranki da na iyayenki sai in bata tsakanina da mahalicina? Walyn wasa kike da lamarina, kina aurena aman baki san waye ni ba! Kema kin kwana a cel bare wani tsohon dan kacare! Kin san yana me na kama shi? Tare da wa? Ku kiyaye fitina sai ku zauna lafia walyn tashi ki bar min dakina!
Rai bace ta diro daga saman bed din ta saka rigarta ta bar pant din a nan, sai da ta kai kofa ta ce" inma me yake yi shi a bayanne yake yi wa ya san me wani ke aikatawa da Alhinayettt!
Tana gama fada ta yi waje da sauri abinta,
Da mamaki ya rakata da kallo,
Ya so abin ya bata masa rai sai kawai ya yi watsi da shi ya mike yana murmushi ya shiga ya tsaftato jikinta ya dawo falo ya kwonta
Tun karfe bakwai aka farka a gidan Wardugu,
Ayya ta fito da yarta su sai gida,
Mahaifiyar walyn ta fito da kanwarta su mijinsu,
Mu.azam ya fito cikin dakakiyar shadar wardugu sai kanshi yake bazawa,
Walyn na daki tana ramuwar bacin da suka kwana zaune suna masifa da iyayenta,
Agaishat dake zaune jikin Ayya, domin yanda ka san mage haka take, ta lafe jikin Ayya kanta a konce kan cinyar Ayya take hangen yanda Mu.azam ke aika mata da murmushi, ya aske gashin kansa ya yi irin askin nan na samari ya yi kyau abinsa sai daukan ido yake, a baza abubuwan kari a falon na wardugu hakama na walyn,
Takunsa ya shaida fitowarsa,
Tafiya ce yake cikin isa da takama,
Yana fitowa du suka kai dubansu wajensa,
Wani irin faduwar gaba ne ya samu Agaishat, a ranta ta ayana ya salam,
Wardugu ya karasa direct wajen Ayya,
Yana tafe ne yana kallon yarinyar dake kwonce saman cinyar Ayyarsa, wace irin gaisuwa zai yiwa mamansa ne?
Yana karasowa ya ja ya tsaya, kaki ne jikinsa tun daga hular kansa har takalmansu na sojoji, sababi ne bugagu ne na manya da galolinsa a jiki na shaidar shi din waye,
Gilashin idonsa ya cire ya saka idannuwansa cikin nata,
Wani irin tsam ta ji a gaba daya jikinta hakan ya saka ta kankame hannun Ayya,
Da ido yake nuna mata ta matsa ya yi hugin din mamarsa , aman Agaishat bata gane ba domin ba.a taba haka da ita ba,
Idannuwansa ya lumshe, a hankali ya duka ya kai hannunsa ba wani dar ko tsaye tsaye ya kama hannunta ya aniya dagata daga cinyar Ayya,
Agaishat da ta yi mutuwar kwonce🤣 ta zazaro ido tana kallonsa tartar
A hankali ya bude bakinsa ya busa mata iska wajen idannuwanta ya karasa mikar da ita kafin yake yatsina fuska,
Ayya dake kallon ikon allah ta ce" kai daina taba min hannun yarinya ita ba irin wannan kawar taka bace! Meye haka zaka hanata hutawa?
Wardugu ya turo baki sai kace wani shagwababe ya duko ya dan yi huging din Ayya, a hankali ya ce" ni ni ne na wajenki kar ki manta Ayyana, ina kwana,
Ayya ta rungume shi itama tana murmushi ta ce" sannu da tashi Wardugu , aman ka ga yarinyata yanzu na fi ji da ita kan ku, ai ku maza ne ,
Ya yi murmushi yana kallon yanda Ayya ke kokarin maido da Agaishat jikinta,
Cika Ayya ya yi ya ce" amini abin kauna,
Mu.azam dake danna waya yana faman blok din yarinyar nan docter, domin ta whatsup sai kuka take masa ta fame shi fa walahi gatannan zuwa nigeriar ta dawo da shi a yi masa aiki, ya dan dagawa Wardugu hannu,
Wardugu ya girgiza kai ya ce" tashi ka ja ku bi bayana na raka ku, aiki ne da ni fa ka sani,
Mikewa ya yi inda su Ayya ma suka fice suka nufi mota ba tare da Wardugu ya koma bangaren walyn ba domin ya san ko ya je wata rigimar ce zasu yi dan haka ya shige dankareriyar sabuwar rangrover dinsa ya ja gaba su Mu.azam na biyr da shi a baya,
Du inda suka zo gilas kawai yake saukewa ya yi nuni fa yana tare da motar su mu.azam har suka karaso gidan Ayya
Wata mahaukaciyar mota fara ce fake a kofar gidan, suna karasawa mai motar da ya juya keyarsa ya juyo yana kallonsu waya a kage a kunnesa
Datijo ne dogo fari kal, cikin manyan kaya yake ya yi rawani aman ya bude habarsa,
Gabansa ne ya yanke ya fadi gannin yaronsa cilo da ya malaka yanda ya fito daga mota ya zama cikenken namiji mai jini a hanci,
A hankali ya hango matarsa, aminiyarsa, mai kaunarsa , ta fito daga bayan motar daya ta karaso wajen wardugu,
A hankali wardugu ya rike hannayenta yana dubanta cikin ido ya ce " mahaifiyata, ban kama matar Marahut dan na hada ki rigima da shi ko dan daukan fansa ba, ta cancanci kamawar ne, ina rokon ki da kar ki biyewa kowa ciki kuwa harda Marahut!
Ayya ta rike kuncinsa , ta sakar masa murmushi ta ce" na sani, kaida ba mace ba mai zai saka ka yi aikin mata? Na yarda da kai Wardugu, mahaifinka kai ya zo nema ba ni ba domin ya san wacece ni, ba abinda zai hada shi da ni , ka je aikinka, sai dai ina kara jadada maka ka kiyaye bakin mutane , ka yi aikinka domin Allah ,
Wardu ya gyada kansa ya mayar da ita mota inda tuni mai gadi ya bude mu.azam da ya sada kansa kar Aba Marahut ya gane shi ya ja motar ya shige gidan Ayya
Agaishat dake zaune gaban motar a hankali take hangen Wardugu har ya shige tasa motar ba tare da ya nuna ya ga halitar wani a wajen ba ya tayar ya ja motarsa ya nufi wajen aiki
Murmushi marahut ya yi bayan mai gadi yana kokarin rufe gidan ya dakatar da shi ya tura ya shige daidai Ayya ta fito daga motar,
Kokarin tafiya take domin ta ga shigowarsa sai dai me,
Muryarsa ta tsinta , muryarsa mai gigitata, a hankali cikin sanyi ya ce" *asalamu alaiki anmi Wardugu!*
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3️⃣0️⃣
Dan jim Ayya ta yi, kafin take dora kafafuwanta ta fara hawa yan matatakala kwaya uku dake sadata da balbalin bangarenta,
A nitse a dake ya kuma furta" du musulmin kirki ya dace ya amsa salama koda iya abinda zai fada kennan,
Ja Ayya ta yi ta tsaya tinawa da ta yi tare take da su Mu.azam, ko ba komai bata so yarinyar da ta dauko riko, ta dauka tamkar yarta ta cikinta ta yi wani tunani a kanta, dan haka ta ja ta tsaya ta juyo a nitse tana kallonsa ido cikin ido ta ce" amen wa alaika salam,
A hankali ya kai hannunsa jikin karfen ginnin yana kallonta, matarsa uwar dansa, auren soyaya suka yi ba na hadi ba, auren fahimtar juna mai cike da nishadi, sai dai ya yi sake, ya yarda laifinsa ne hakan ta faru, a hankali ya ce" wa ya baki izinin yin tafia har kasar agadez kauyen agadez timiya ? Kika je kika yi har kusan wata biyu? Anmi wardugu banda fitar ta cikin garin Niamey yanzu kuma har kin fara yin ta nesa haka? Ba dai a so zuciyata ta huta .....
Ya karashe yana dan sada kansa,
Mamaki take, al.ajabinsa take, uhum lalema, me yake nufi da ita? Kennan yana bibiyar rayuwarta ko me?
Fuska ta yatsina kafin take fadin" gidan nan ban yarda Wardugu ya saka ko sisinsa ba dan kar watarana ka zo da takamar danka ya gina,
Marahut ya ce" bayan Allah ya halita min ziyarta inda gonata take a duk lokacin da na yi niya?
Haushi ne ya cika Ayya, yana nufin ita, dan kuwa ai matayenku kamar gonakinku ne,
Dan juyawa ta yi ta ce" ka tarda shi inda yake ba gidana ba,
Dan daga murya Marahut ya yi , domin ta tafi ya ce" ki kiyaye fita kai sake ko dan yarmu da kika dauko kar ta koyi yawo ba izinin miji idan mun yi mata aure!
Wani irin bude kofar ta yi ta rufota da karfin gaske wanda da ba dan glas din mai nauyi kuma mai karfi bane da kasa zai zubo baki dayansa.
Murmushi ya yi, a hankali ya sauko wajen su Mu.azam dake tsaye cirko cirko,
Mu.azam ya gama yarda wajen wa Wardugu ya yi gadon abubuwa,
Gashi mahaifinsa ya kai shekaru sitin da yan kai aman yana abubuwa tamkar wani bajimin matashin sarki?
Yana karasowa ya saki fuskarsa sosai ya mikawa Mu.azam hannu,
A mutunce Mu.azam ya gaisar da shi,
Marahut ya amsa yana dubansa kafin yake kai dubansa wajen Agaishat, da yaren buzanci ya ce" ina murna da kasancewa Abanki yarinyata,
Agaishat ta ji abin sabo, abin ya zo mata a bawai, ikon Allah, mutun ya wannan, ya kirata da yarinyarsa, gashi fari karkarkar ita kuwa baka kirin aman bai nuna kyamata ba, harma ya fada mata ya yi murnar kasancewarta yarinyarsa,
Baki kawai ta saki tana kallon kama, kai har yannayin girman jikin domin Ayya bata da girman jiki irin wannan ,
Hannunsa da ya dora a kafadarta na dama ya ce" sannan ki yi ta kulawa da kanki ki yiwa Ayyarki biyaya, zan yi tafia sai na dawo ...........
Agaishat da wata kwallah ta tarun mata a ido tana kallo ya fice a gidan a kafarsa domin a waje ya bar motarsa,
Yana fita ta juyo wajen Mu.azam, da tsananin murna ta ce" ka ji me ya kira ni? *Yarinyarsa*,
Mu.azam na kallonta shima da murmuahin a fuskarsa yana kallo hawayen murna ya zubo daga idannuwanta,
Cike da zumudi ta ce" kuma kuma yace ya yi murna da kasancewata tare da su, yaya Mu.azam ni *BAK'A*,
ai bai kai ga bata amsa ba ta cikashi ta shiga taka matatakalar da gudun tsiya dan zuwa fadawa Ayya cike da murna,
Sai dai tana shiga ta tarar da Ayya zaune ta hade rai tamkar an yi mata mutuwa, yannayinta ya nuna tana cikin yannayin bacin rai mai tsanani
A hankali ta shiga dan takawa dan karasawa kusa da Ayya,
Tana zuwa ta dan duka tana kallonta murya a sanyaye ta ce" Ayya, lafia?
Ayya ta dago ta yi mata wani kallo na ta barta,
Agaishat bata fahimta ba ta ce" Ayya, *WANENE WANNAN?*
Ayya ta zuba mata wani kallon, rai a hade ta ce" ki je dakinki Agaishat!
Agaishat ta mike da sauri tana kallon Ayya kafin take juyawa da sauri ta nufi dakin nata a matukar tsorace,
Tana shiga ta karasa bakin bed ta tsaya jikinta na rawa, Ayya bata taba yi mata haka ba, dan haka hankalinta ya tashi ainun,............
Wardugu dake tsaye kan kafafuwansa tun zuwansa wajen aiki yana fama da jama.a, tun daga manyan mutane masu fada a ji da suka biyo sahun nasu, da tsagerun mutane da suka zo belin yan uwansu ko abokai, sai bayin Allah talakawa da yayansu suka kai su inda basu taba tunani ba, suma sun zo da kokon bararsu kuma cikin ikon Allah wardugu na sauraron mutane du wanda ya ga abin ba wani bane a nan take yake salamarsa da kwakwaran kashedin idan suka kuma hadewa a irin wannan waje ba zatai masa da kyau ba,
Daga karshe dai Wardugu na bincike ne cikin nutsuwa yana salamar mutanen da basa bushe bushen nan bisa kashedinsa wanda da kansa yake yiwa mutun ido da ido ba aike ba!
A hankali ya fara kawowa wajen masu zuwa dan kawai su kwale, wani saurayi aka shigo masa da shi, yana zuwa ya zube kasa ya shiga gaisar da Wardugu,
Warsugu dake kallonsa, kana ganninsa ka san ba wani dan mai shi bane, aman ya tashi ya saka kansa a rayuwar halaka idan an yi magana ace kadara, ace Allah ya dora,
A dake ya ce" tashi ka zauna saman kujera,
Da sauri saurayin ya tashi ya zauna sai sasada kai yake tamkar ya yi karya gaban sarki, tsoro yake a ransa domin a gaban idonsa akaiwa wata dukan tsiya wanda ya sa har ta sume dan kirikiri ta yi ikirarin ita ko wacece ta tofar da yawu ta dura ashar ta ci alwashin gyatiminta zai zo ya fitar da ita har sai uban gidansu Wardugu ya bata hakuri hakan ya sa su kuwa suka nuna mata da gidan maza ta shigo ba gidan yara ba, suka murza kwonji a jikinta har ta some, labarin da ya kaiwa Wardugu da ya fito a gaban mutanen nan na cel ya zuba mata ruwa da kansa wanda hakan ya farfado da ita, sai dai tana tashi ya wanka mata wani marin da ya mayar da ita duniyar suma sannan ya nunata da yatsa ya ce" ban so tonawa kowa asiri ba shi yasa na saka aka shigarmin da iyayenku daga wancen dakin wanda ba wanda zai gane in an shigo da kai wanene mahaifinka kuma me ka aikata ba, sai gashi kin tonawa mahaifinki asiri a matsayinsa na dan siyasa kin kama sunansa har kin nuna mana halin kodin! Dole mu kai kararki wajen alkali kin zagi soji!
Haka aka kwasheta aka jefata cikin cel din ya koma ya ci gaba da aikinsa dan haka ne ya sa wannan saurayin kamar ya kwonta dan kadabi,
Wardugu ya ce" yaya sunanka?
Saurayin ya kalo shi kadan ya sada kai ya ce" sunana Murtala Tasiu,
Wardugu ya gyada kai ya ce" tun yaushe kake zuwa wardugu place? Kai da wa kuke zuwa? A nawa kuke biyan kudin shiga? Du sati sati kuke zuwa? Da yan mata kuke zuwa?
Murtala ya ce" ba.a fi shekara biyu ba,,
Ni da dan gidan Elhaji Dahiru muke zuwa,
Aa ba kowani sati ba dan kudin shigan da muke biya shima ba kulun yake da shi ba jika goma goma, sannan in mun shiga ga kudin kashewa , aa iya mu muke zuwa a can muke haduwa da yan mata kowani sati akoy a ciki,
Wardugu ya tsare shi da ido ya ce " tun daga bakin lokacin ka fara busa kodin?
Murtala ya shiga raraba ido, ya daga hannu zai fara rantse rantse Wardugu ya ce" murtala, ka fada mini gaskiya mai yiwuwa ka samu sasauci!
Murtala ya ce" oga, ka rufa mani asiri dan girman Allah, mahaifina gajiyaye ne, sai na bi abokin nan nawa yake bani wani dan abin na je na ciyar da mahifina da kanwata, kanwata bata gani, mahaifina kuwa ya tsufa, ba a son raina nake saka kafata wajen nan ba,
Wardugu ya ce" ban tambayeka labarinka ba Murtala, ban yi niyar wulakanta ba ina rokonka kar ka wulakantani, kar ka kawo mani shirme a nan , da farko dai du idan ka ga soji rikeken dan tasha ne domin tashanci koya mana ake mu shanye sai dai muna aiki da shi ne kan tsari, na jima a aikina hakan ya saka ana yi min karya nake ganewa, ka bani amsata ko mu baje basirar rainin hankalin ni da kai!.............
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3️⃣1️⃣
Da sauri Murtala ya ce" Eh eh , tun daga lokacin da muka je abokina ya siya ya saka na taba tun daga lokacin nima nake sha ,
Wardugu ya shiga gyada kai ya ce" kana iya fita,
Dan mikewa ya yi, sai ya mike sai ya dan duduka sai da wani soja ya shigo ya finciko shi ya mayar da shi cel,
Da mijin Auntyn walyn aka shigo,
Mutun har mutun, sai sasada kai yake na kunya,
Warsugu ya tsare da da ido, wai tun a nan duniya ka kasa hada ido da mutanen da basu baka ko cin wuni daya ba, ya zaka kare da wanda ya haliceka ya baka dukiya dan gannin ya zaka tafiyar da ita, ya ara mata lafia, gani da ji, ya baka ikon motsi, ya baka damar magana, ya kaika kasar da ba yake yaken yu da kulun wa.inda zasu iya tayar maka da hankali , ya baka isashen lokaci dan kawai ka bauta masa ka yi masa biyaya, sai gaka tsofai tsofai a gidan badaka tare da yar shilar yarinya ta tube kusan zindir tana maka rawa tana ciyar da kai gasashen kifi, shine zakana wani sada kai a gabana kai ga cikenken dan iska! Du wardugu ke jifansa da wani matsiyacin kallo sannan yana ayyana du haka a ransa,
Wardugu ya ce" ya sunanka malan?
Mijin aunty da mamaki ya dago yana kallon wardugu ya ce" haba haba wardugu, ai ko me ake a san na gida, a fitar da na gida, ka yi hakuri kure na aikata ba zan kuma ba , ka salame ni na koma ba tare da wani bama ya ji abin kunya ne ace ka rufe mijin kanwar babar matarka!
Baki wardugu ya dan daga na mamaki, ka ji wani dogon bayani wai mijin kanwar babar matata,
Kai ya girgiza a ransa ya yi murmushi, a fili ya kuma furta" ya sunanka malan!
Yana mai dagowa da yanayin dakewa,
Mijin auntyn walyn nan ya fara zufa, yana gagawar magana ya ce" tototo, sunana Lawali , Elhaji lawali,
Wardugu ya ce" me ya kai ka Wardugu place? Kai da wa ka je? Me ka je yi? Tun yaushe ka fara zuwa? Me ka lura ana yi a wannan waje?
Lawali ya ce" ni kam wannan waje na je ne bisa tsautsayi da rabon a yi, domin dai yarinyar nan na so na aura sai take shaida min na kaita mu sha iska, to da muka je shikenan sai muka mayar da wajen wajen zuwanmu lokaci zuwa lokaci yanzun dai an kai shekara uku,
Sannan a wannan wajen gaskiya na lura ana abubuwan da bai dace irin ahaye shaye, wannan da ka ganni tana yi wai karamin ne, eh wanda muke yi shine karamin ba Allah ja da kwana....
Ya karashe yana jinjina
Wardugu ya jinjina kai, ya ce" lawali kada daga Kokin ne?
Da sauri ya dago yana duban wardugu, ya ce" bilahilazi ban taba ba, ai ni ko warinta na ji juwa ke kayar da ni, ka rufa mani asiri rashin jina bai kai can ba,
Wardugu ya dago yana dubansa, wai rashin jinsa, kai ya girgiza da hannu ya yi masa nuni da ya fita,
Yana kokarin kara magiya Marahut ya shigo inda sojan nan ya biyo bayansa yana dan kame kame ya rasa me zai yi, su dai ba wanda bai san oga Marahut mahaifin uban gidansu ba, shi ya isa ya masa iyaka ne? Tun daga babar kofa ya samu shigowa ya ratso du zone na control ba.a hana shi ba sai shi tal dake tsaye dan kula da bude kofa da kuma rufewa da kyau ne zai hana shi shigowa?
Kallon Lawali Marahut ya yi kafin yake girgiza kai yana murmushi daga cikin rawaninsa,,
Kai sade Lawali ya fice domin ya ji kunyarsa ainun
Marahut ya bi tsararen tankamemen office dan nasa, bMarahut ya ce" ya aka yi ka canza kanshin turarenmu ne Wardugu? Kuma ya aka yi ba hotona a office dinka bayan kai din dan halal ne koda shege ai ado yake da ubansa bale dan halal ,
Wardugu dake ta cika takardu yana dan dana laptop bai ce da shi ci kanka ba,
Marahut ya ce" Warsugu Abanka ne fa ni ? In ba ruwanka da mutane su ga kana min haka ba ruwanka da Allah ne??
Wardugu ya ajiye biron dake hannunsa ya dan shafa kansa ya dago da kallonsa wajen mahaifinsa wanda a kamaninsu haske ne kadan ya dan fi shi domin farin wardugu ba irin cancan din nan bane,
Warsugu ya ce" Aban Wardugu ra.ayi ne ya sa na daina anfani da turaren da ka sanni da shi, sannan ni ba mace bane da zan kawo hotonka office na buga, kuma shegema mutun ne!
Murmushi marahut ya yi ya karasa wajen kujera ya zauna ya ce" to ka fido mani matata mu tafi gida Wardugu,
Wardugu ya yi murmushi a bayane shima ya ce" ba zan so shakar iskar da kuke shaka ba ko na second daya, sai dai ya zama dole ne, matarka mai laifi ce
Meye laifinta wardugu? Me ta yi da tsanani haka? Ka san yara da kin ji suke,aman ai koma me ta yi ina gannin sai mu kashe mu birne abinmu a tsakaninmu ko wardugu? Marahut ya fada yana dubansa
Wardugu ya ce" zan so haka, sai dai ka ga rashin jin nata ne ya yi kamari, tana shigo da kwaya ne tana siyarwa wannan ba boyayiyar shaida bace, abinda nake bincike kawai na samu hanyar da take shigo da ita ko wanda ke bata sai na mika su kotu koda kuwa *kai ne*, sai dai ban san ba yin hakan ko Allah zai kama ni da shi?
Da sauri marahut ya ce" Quoi? (What?), wani irin kwaya? A Wardugu place din? Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, wardugu ka kara mani haske a lamarin nan
Wardugu da ya ji ya dan samu sasauci, domin a sama yake, jininsa a saman akaifa, tsoro yake kar a je rinjayar nata ya kai ta saka Marahut a wannan harka? Aman yanzu ko ba komai ya ji dan sanyi a ransa dan kuwa har gobe da sunnan mahaifinsa yake anfani,
Wardugu ka fada mani mana, Marahut ya fada yana dubansa da yannayin serius
Wardugu ya yi umarnin a kawo AISATA,
Shigo da ita aka yi, dare daya tak du ta fara fita hayacinta abinka da wada ya saba da hutu,
Tana gannin Marahut ta sauke ajiyar zuciya mai nauyi kafin da sauri ta nufi wajensa ta saki kukan kirsa,
Tana kukan ta ce" ka ga abinda Wardugu ya yi mini? Wannan wani irin tsana da cin mutunci ne? A gaban jama.a ya saka mini anker tamkar wada na yi sata, ai a tunanina ya dace komai ya fice tsakaninmu ko me na yi sai ya hukunta ni a gida ba wai a gaban duban mutanen da zasu yi min dariya ba,
Hannunsa ya saka ya dagota daga jikinsa yana dubanta, kadara, Aisata kadara ce mai wutsiya, a dalilin Aisata ya rabu da farin cikinsa da girmansa a idannuwan iyalinsa, maciya ce Aisata, Aisata zinari ce,
A nitse ya ce" me da me kuke aikatawa a Wardugu place?
Aisata ta yi tsam kafin ta shiga cicira ido ta kali dan ta kali uban, cikin yannayin barikinta ta ce" me muke yi kuwa banda neman kudi? A wardugu place ba abinda muke yi,
Wardugu dake rubutu a takarda ya dan yi tsam ya dago ya dube su ya maida kansa ya ci gaba da aiki,
Bai jima ba ya daga wayar office din ya danna kira,
Cikin girmamawa ya gaisar da jujun kafin yake fadin" mai girma na gama nawa binciken, yanzu ana kawo maka takardu ka duba, daga nan na mika maka su kawai ,
Amsa shi ya yi kafin yake kashewa,
Marahut da ya gama fahimtar wayar da Wardugu ya yi shima yana dubansa, cikin yannayin nutsuwarsa dai ya ce" har yanzu baka daina jin haushina kan Aisata ba?
Wardugu ya juyo da sauri, ido ya zazaro baki daya kafin yake mikewa ya tofar da yawu a nan cikin office din ya ce" kan wannan? Ya fada yana nuna aisata,
Ya girgiza kai ya ce" ai koda me daraja ce bata kai na yi anfani da damata dan wulakanta ku ba, ka gane laifi ta yi, idanma baka yarda ba ai kai din oga ne kawai ka je wajen wa.inda zan mikawa takarda idan sun baka matarka ruwansu ni dai ai na tono barnar ko? Ka fi kowa sannin waye wardugu domin kaine mutun na farko da ka rikeni a duniya bayan likitar da ta fitar da ni daga cikin mahaifiyata!
Yana gama fada ya ja kys din motarsa ya dauki gilashinsa ya fice a office din yana mai jin haushin yanda mutane ke magiya kan a bari a ci gaba da yada barna!
Jikin Ayya ne ya yi sanyi bayan korar Agaishat da ta yi, a hankali ta mike ta nufi dakinta tana mai jin wani iri me ya yi zafi harda laifin wani zai shafi wani?
Tana zuwa ta shiga da salama,
Agaishat dake zaune kasa ta dora kanta a gefen gado tana jan carbi da hannunta ta dago da sauri tana kokarin mikewa tana duban Ayya,
Karasawa Ayya ta yi ta riketa ta zaunar da ita gefen gado,
A nitse ta ce" ki yi hakuri yar gidan Ayya, ba zan kuma yi maki irin haka ba ,
Agaishat ta sauke ajiyar zuciya tana dubanta,
Ayya ta ce" bara na baki labarin mu..... na fada maki wacece *AYYA?*, na fada maki waye *MARAHUT a rayiwar Ayya?*, na fada maki wanene *WARDUGU* sannan wani irin girman daraja yake da shi a rayuwar Marahut da Ayya? Yarinta bara na baki labarin da ba kowa ya sani ba................
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3️⃣2️⃣
labarin Wardugu da tushensa a gajarce
.
........ ..................
Sunana *Zanaba SHAU*, sunnan Mahaifin Wardugu *MARAHUT ELUM*, ni marainiya ce gaba da baya, na taso a hannun kakata ta wajen uwa da ta yi min saura,
Marahut dan gata ne gaba da baya, ya kasance a lokacin anguwarmu daya domin gida uku kawai ke tsakaninmu,
Tun wayona bai gama fahimtar Marahut na sona ba har na gane domin kiri kiri idan na yarda wani lokacin na yi dan shirin atampa na yafa mayafi na fito zai rufe ido ya kora ni yana masifa,
A anguwa ana girmama kakata domin mace ce da ta san girmanta, ba abinda ya shafeta da abin hannunka, ga mutunci ga zumunci,...du juma.a zaki ga an kawowa kakata abinci daga gidajen anguwar nan ciki kuwa harda gidan su Marahut inda mahaifiyarsa shuwa arab ke turowa kakata da gurasa ta kasa, irin wace ake yi a kasa ta ainahin da miya mai dadi harma ki ga an zuba tawa miyar mai magi domin a lokacin an hana kaka shan magi.
Sosai muke soyaya da Marahut, duk da wani lokacin nakan zauna na yi shiru ina tunanin Marahut na so na kamar yanda nake son sa kuwa?
Hakan sai ya tayar min da hankali sosai domin Marahut dai jarumin namiji ne mai cike da abubuwan da mata ke marari har suna kai wawa, harma wani lokaci na kwatanta masa....
Tsareni ya yi da ido kawai, zuwa wani dan lokacin ya mike ya fice abinsa hakan ya haifar min da faduear gaban ko ya yi fushi ya bar ni ne?
Kwana biyu tsakani na dawo daga makarantar dare islamiya da nake zuwa a kusa da mu na tarar da kakata zaune tana jan carbinta da rufarta bata kwonta ba, ba kamar sauran lokutan ba,
Da sasarfa na karasa wajenta dan gannin abinda ke damunta sai dai ina zuwa ta rike hannayena tana kallona ido cikin ido ta ce" Zannaba, kina ta adu.ar neman Allah ya baki miji na garin nan kuwa?
Na amsata ina dubanta da wani irin yannayi ta ci gaba" an zo neman auren ki daga gidan Elum, Zannaba kin ji zuciyarki ta aminta da Marahut?
Wara irin kunya ce ta diro mani, domin fa Agaishat yata tubawa na da muguwar kunya, batuben mutun na da kunya harda ta mamaki, hakan ya saka na sada kaina kasa harma jikina ya fara rawa,
Kakata ta ce" kul, na hane ki da ki yi haka da ni, ke kawai gare ni kema ni kawai na rage maki, Allah shi ne gatanmu, zan so ace na bar ki hannu mai kyau, dan haka maza bani hankalin ki mu gama magana,
In takaice maki a wannan rana bamu kwonta ba du sai da muka dauki niyar istihara wace cikin kwana uku hankalin mu ya gama kwonciya har ma muka aminta da auren nan,
Marahut ya yi min gata , agaishat ya kai kudin aurena ya yi min kayan da aka jima ana labarinsa, aka daura aurena irin na kowace yar gata inda kakata ta bada mamaki ashe tana ajiye da sarkokin aurensu ita da mahaifiyata, ta kai aka buge akai min tafkekiyar sarka da abubuwan hannu na zinari irin na kowace batuba yar gata, sannan ta fitar da kadarorin mahaifanna harma da nata gaba daya ta raba aka yi min kayan daki sauran ta damkawa mai anguwar anguwarmu amana,
Wsshe garin auren mu Marahut ya dankara min wata makekiyar sarka ta zinari tatare da kwacakwablarta bisa al.adun tubawa wanda hausa ce cikin hausa, ba.a jima ba muka daga dan komawa bakin aikinsa inda aka maida shi domin baban likita ne kuma yana harkar kasuwanci da kiwo.....
Mun kasance cikin farin ciki, mutunta juna, da kaunar juna, muna tafiar da rayuwar aurenmu bisa tsarin islama muna kiyaye du wani abinda zai firgita mu sai dadaykun da baza.a rasa ba na yau da kulun!
A haka na samu cikin wardugu,
Mu kai rainon abinmu har na tashi haihuwa inda Allah ya taimake ni na haihu a hannun mijina a asibitin da yake aiki da taimakawar nurse..
.
Mun koma gida dan zanen sunna, nan Marahut ya gabatar da sunnan *WARDUGU* a matsayin sunnan da ya zaba,
Kowa ya jinjina lamarin sai dai ikonsa ne, dansa ne, aman sunnan Wardugu linzami ne ga mutun mai zuciya, mai fada, mai balaki, kai ba.a zama lafia da mai sunna wardugu, Wardugu! HUM, ko canfawa ne mun yi kuma yana bin mu, kwarai zahiri ne Wardugu duniya ne guda, ba sai an koya masa ba da abinsa aka haife shi.......
Ina wanka a gida wajen kakata, tana kula da lamarina sosai da sosai, wata rana muka wayi gari da kyautar Allah, inda mutuwa ta sake zagayowa ta tsame min wace ta min saura a tarihin iyayena,
Ayya ta yi shiru ta share kwalar da ta zubo mata,
Agaishat da ta yi lamo ta dora kanta a hannun Ayya, Ayya ta ci gaba" Agaishat na ji mutuwar baiwar Allahn nan, domin ni ita ce duniyata, ko me na kwaso ita nake fadawa a nitse ta warware min, ta rasu ta bar ni da jaririn da a lokacin bana iya daukansa da garaje dan girmansa masha Allah, ta bar ni da dan labubun yaron da yakan calara kuka wai shima nice mahaifiyarsa, na ga rana na godewa Allah,
Agaishat ta kara jimke hannun Ayya itama tana jin yanda hawayen ya zubo mata, Ayya baiwar Allah, bata da kowa gaba da baya, ashe du yanda mutun ya kai ga malakar arziki bashi da cikeken farin ciki na yanayin rayuwar yau da kulun?
Ayya ta ce" na dawo ga marahut, bani da kowa bani da komai sai Shi a nan cikin duniya,
Bayan an yi bakwai muka juya garinmu inda na dauki girma na ajiyewa kaina na karfi da yaji na ci gaba da karatun likitana da nake yi a Ensp,
Can tsakiyar dare nakan dadaba Marahut, idan ya farka sai nace" Marahut, kar ka wulakanta ni a duniya, kai ne duniyata, kai ne farin cikina,
Yakan riko ni jikinsa ya ce" ban aure ki ba sai da na gane ke ce lumfashina, a duniya baki daya me ya kai lumfashin mutun tsada? Ba zan yi garajen gannin hawayenki ba sai na kadara!
Magangannunsa da alkawarurukansa suka saka na samu nutsuwar zuciyata harma na warware na ci gaba da shagulgulana na yau da kulun tare da yarona,
Tun Wardugu na da wata bakwai ya mike, yana tafiya da kafafuwansa digir digir tamkar dan gwari,
Du inda na yarda na je da shi idan ya damki yaro ko matashi sai an kwace da kyar,
Ya kasance ba.a gardama da shi da ya warware, yana fama da ciwon athsm wace in dai na yarda ransa ya baci toh fa a kadan mu yi kwana uku a asibiti domin athsmar nan zata tashi ne ya kasance daga ta kwonta sai ta kuma tashi domin ba zai kwontar da hankalin nasa ba,
Wardugu zuciyar mahaifinsa ne, domin daga shi ko batan wata ban kuma yi ba, muna bibjyar komai nasa tamkar ranmu, kai har bama kawaici a nuna soyayarsa,
A haka Allah ya hada mu da baba tsofo, wanda kawai salama ya yi yace yana bayar da magungunnan hausa ne,
Nan muka zanta a bayan idon mahaifin Wardugu domin baya son lamarin hausan nan wai tsoro yake ya taba masa reins,
Cikin ikon Allah ya ki karbar kudina, muka ajiye magana idan Wardugu ya samu lafia zan yi masa kyauta,
Yakan zo lokaci zuwa lokaci ya kawo mana magannin da cikin ikon Allah muke bashi da nonon rakumi sabon tatsa da sasafe, tun ina boyewa har na bayannawa Marahut shima ya kama mani domin sauki kamar da wasa Wardugu na samu a hankali a hankali har ya daina lumfashi da bakinsa ya dawo yi da hancinsa,
Agaishat na kasance mutun mai shegen son mutane, ko dan na sakawa kaina bani da kowan nan a duniya sai Allah sai mijina? Ya kasance son yaya da yawan kula zumunci da jama.a,
A haka na hadu da babar aminiyata matar sarkin agadez, na hadu da kawata ta damagaran hajia Falmata, da sauran su,
Wardugu rashin lafiarsa kawai ya warke aman halaya na nan, a haka aka tsahe mu aka maido mu garin nan inda kwata kwata baba tsoho ya bace min na neme shi na rasa har muka taso aman abin na tsaye a raina sannan ina yawan tambaya,
Kwonci tashi wardugu ya tashi da niyar shi fa soja, soja, hakan ya sa mahaifinsa ya sama mana waje a Babar makarantar sojojin niger wace ke a kwalo, wace tun yaro na karami ake kai shi shikennan shi da iyayensa sai jifa jifa,
Karatu yake, sannan kwazo yake da shi ko a filin training,
Hakan ya sa babansu yake kaunarsa harma yake zumunci da mahaifinsa
Wardugu na da shekara ashirin da biyu ya fito gagarumin comandan, jikaken saurayi, kaukauran namiji, zakin zamani, yaro da kudi kamar yanda ake kirarinsa.......
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3️⃣3️⃣
To tunda Wardugu ya dawo sai kuwa yan mata suka ce bismillah, ba kalar wace bata zuwa , kin dai ga yanda yake uwa kurman nan? Toh haka zasu zo su karaci haukansu sai dai su yi su gama su tafi,
Ban san ya aka yi, ta ina aka yi suke kawance da wannan mai sunna Alhinayettt wace ni hakanan nake gannin karya ne ba wani kawance may yiwuwa soyaya suke ba halin aurenta domin aurensa bai wani jima ba,
Ana haka ya amincewa yarinya daya soyayarsa, yarinyar da ta yi kundubala da sauran yan matan,
Soyaya suke ta hauka irin soyayar yayan zamani, ni ba zan shaidi yarona ba ba kuma zan ce yana aikata masha.a ba, aman a lokacin da yake kwana a gidan nan har kwana ta sha yi a wajensa dan kuwa sai da na rufe idannuwana na ci masa mutunci sannan na daina kamata a dakinsa,
Waye shi da zai rantse min ba abinda ya shiga tsakaninsu? Namiji ne, ita kuwa mace, sun kadaice a wajen da ba kowa sai su sai Allah, ai hankalina ba zai dauka ba!
Ire iren abubuwan da sukai ta faruwa kennan da yarinyar da ta gama kwana gidan mu, mamaki nake da tsoro, Wardugu ina ya zubar da kunya irin ta batube? Gaba daya wannan karatu da ya yi ya saka du ya zama wani kiritace wani tsayaye! Sam ya zubar da al.adu da dabi.un tubawa idan na yi magana sai yace ai ba wani adini bane, shi gaskiya ya girma a birni ba zai ci gaba da rayuwa irin na daji ba, ! ALLAH ya shirya,
Ana haka ya tafi karo karatu inda suka hadu da mu.azam suka kula zumunci mai ma.ana, a can ya hadu da matar da yake aure yanzu wace a lokacin ba irin azabar da bata sha ba domin shi soyayarsa tana kan *AISATA* ,
Aisata? Agaishat ta tambayi Ayya,
Ayya ta ce" kwarai Aisata dai wace ubansa ya aura,
Agaishat ta ce" aa, Ayya na shiga rudani,
Ayya ta ce" bara na warware maki,....
Haka kawai mun ci gaba da fahimtar juna alhamdulilah har wardugu ya dawo daga tafia,
Nan ya zo da maganar a tura wajen yarinya a tambayo aurenta,
Tashin farko ya dira cewar ba da yawuna ba, kuma in har ni na haife shi ba za.a yi haka da ni ba, domin yarinya bata da da.a , zan so matar da zai aura ta fari ta kasance mutuniyar kirki ko dan fadar adini ku zabawa yayanku iyaye na gari,
Nan fa aka shiga tashin hankali, yarinya ta zo har gida ta tsire ni, nan ta yi ikirarin cewa" AYYA kike ko wa? Kin dai ganni, kin ga yanda nake, nice farar mace , kwakwa! Dole na shigo gidanki ko a sarakuwarki ko a kishiyar ki!
Abin ya bani mamaki, zuciya ta kama ni na tunkareta kafin take ankara na damketa, ina faman ihun sai na nuna mata ruwa ba sa.an kwondo bane malalaciyar banza da wofi sai ga Marahut ya shigo da sauri
Kwaceta ya yi daga hannuna kafin yake fadin" ke Zannaba, baki da hankali ne? Kike ikirarin yarinya bata da tarbiya ke kina iya rantsewa waye malamin waye dalibin tsakaninta da dan naki? Ki shiga tatayinki ki daina abu tamkar wata yarinya karama!
Agaishat , a wannan rana, a gaban wannan yarinya Marahut ya wulakanta ni, ya yi min tas abinda bai taba shiga tsakaninmu ba,
Ke dai kwana biyu tamkar kura ta lafa, domin Wardugu da ya ga na nace sai kawai ya basar ya yi biris ya shiga wata sabgar gaban nasa inda ya fara kula Walyn,
Ba.a wani jima sosai ba, domin ba .a yi wata hudu tsakani ba Marahut ya zo da maganar zai yi aure,
Agaishat ban wani nuna halinmu na matan tubawa ba, na ja ajina na yi masa fatan alkhairi, na shiga rokon Allah da ya rufa min asiri kar a je dan haihuwana ya tsaya ne wani abin zai tunkaro ni,
Sannu sannu sai abubuwa ya fara bilo mani, halayen Marahut suka shiga canzawa,
Ya fara cika dare sosai a waje kafin ya shigo, ya dawo ya fara kin cin abincina sai yace baya jin yinwa tamkar wani inji,
A hankali ya kaurace min,
Na sha zuwa na duka nace da shi" menene damuwar? Wani abin na yi ne? Dan Allah ka yi hakuri , har ka manta alkawarin fa ka yi min? Marahut kace nice lumfashin ka, ka yi hakuri ka dawo min kamar da, ni ban wani hanaka aure ba, aman kar ka tayar min da hankali,
Marahut sai kawai ya yi min murmushi ya mike ya fice,
Du abin nan Wardugu bai san ubansa zai kara aure ba sai wani lokaci ya ji a gari, a lokacin ya garzayo gida da sanyin safiya ya tambayi uban, ashe auren ma a ranar sauran kwana biyu ni banma sani ba,
A wannan ranar na ga tashin hankali, na ga rikici, domin Wardugu idannuwansa sun rufe hakama na ubansa, ke sai da na fita a guje na kira direbobi da masu gadi da yaren gida du suka shigo suka yi kokarin shiga tsakannin uban da dan dan kuwa Wardugu ya rike wuka hannunsa yana ta balaki!
Agaishat, wannan bai isa ba sai da aka shigo da amarya Aisata, aisata yar buzaye, aisata yarinya kyakyawa,
A ranar wardugu ya yi dan karamin hauka, ya ja iska ya zo kusan babansa ya ce" aban Wardugu ka sake ta, ka rufa mani asiri ka saketa , kar ka yarda wani abin ya shiga tsakaninka da ita, Aba, wannan bata da tarbiya, bata da haramun! Abanna ya zaka kawo macen da ta gama talatarmin da kanta a irin yannayin da ta fado duniya ni danka a matsayin matarka? Haba Abana, me mukai maka da zafi haka?
Marahut ya dube shi ya ce" ita ba mutun bace? Kun haihu da ita ne? Na yi niya ina sonta na aureta da kudinka ne? Ka bini a sannu Wardugu, ni na haifeka kar uwarka ta zigaka ka kauce hanya!
A lokacin ni tuni na fara gannin jiri, ni Marahut? Na sha dukan kirji nace ni mijina dan goyo ne, ba zai wulakanta ni ba, sai gashi haka ta faru, ni ba aurensa ya dame ni ba, tau da gobe ai sai Allah Allah wacece ni da zan ce ba za.ai min kishiya ba? Damuwana irin auren da ya yi, ya yi shi dan ya nuna min iyakata? Dan ya wulakanta ni? Ko wani abin ke tsakaninsa da yaronsa mai zafi haka?
A lokacin Wardugu ya fara wani irin numfashi, idannuwansa suka shiga canza launi zuwa ja, suka cicika da kwallah, ina gannin hakan na tisa shi gaba da kyar na samu muka shiga motarsa na ja muka nufi gidansa,
Muna zuwa muka tarar da Wakyn ta zo nemansa, a nan ya sauke haushin kanta domin sai da ya bala mata hannu du ya kusan canza mata halita baiwar Allah da kyar aka kwaceta,
Kin ji marabina da gidan Marahut domin akai ruwa aka yi iska Wardugu ya hau, ya gindaya rantse rantse, ya juye, nima fushi, mamaki, tsoron lamarin maza ya saka na yi watsi da shi na rungumi yarona wanda na san a duniyarnan ni ce duniyarsa ,.....
Ayya ta karasa tana dan shafa kan Agaishat,
Agaishat ta dago fuska shabe shabe da hawaye,, tana duban Ayya , ta sani bata da damar da zata iya tofa wani abin a wannan lamari domij ta yi imanin ba komai Ayya ta fada mata ba, tabas ta boye wani abin ko dan karancin shekarunta,
Sai dai wannan lamari ya tuna mata mahaifiyarta, Anna baiwar Allah, yoh ita haka rayuwarta ta kare fa, kuma bata da wani mai dauketa ya matsata daga wajen da ake cuzguna mata, ita bata san bama marainiya ce ko yar dangi, bata san daga ina ta fito ba, ba abinda ta sani,
A hankali ta mayar da kanta saman cinyar Ayya , daidai lokacin da Wardugu ya shigo dakin da salama,
Daga inda take kwoncen nan take kare masa kallo, tabas wardugu ko bashi da ko sisi sai mace ta yi haukansa, ko bashi da hali zai mitsa zuciyar mata, dan farin batube mai zamani,
Idannuwanta ta lumshe a hankali wani hawayen ya kuma zubowa daga gurbin su ta mike a hankali bayan ta share hawayen ta kai dubanta wajensa , kanshin turarensa ya cika mata hanci,
A hankali ta ce" ina yini,
Gaisuwar da tunda suka daukota daga timiya shi dai bai taba jin ra yi masa ita ba, tsumamun idannuwansa ya zuba mata ba tare da ya amsata ba, yana kallonta har ta fice a dakin dan basu waje su tatauna ta nufi wajen Mu.azam dan gannin ko ya ci abinci?
Ayya ce ta lakato shi tana yi masa murmushi tana saisaita kanta ta ce" dan gidan Ayya, sannu da dawowa,
Wardugu ya juyo da sauri yana dubanta, ya yi murmushi ya ce" Ayyana, ina yini?
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3️⃣4️⃣
Amsawa ta yi tana dubansa da madaukakiyar kulawa kafin take mikewa ta kama hannunsa,
Shima biye yake da ita suka fito daga dakin Agaishat suka nufi dakinta,
Walyn ce zaune a saloon mai suna Tawaye saloon, fitacen saloon ne na manya wanda sai ka isa kake saka kafarka,
Akifunta ake gyara mata bayan an yanyanke su an wanke su sosai aka dauko na kanti zako zako din nan aka shiga dora mata,
Kawarta dake gefenta tana karanta magazine, itama ana gyara atach din da za.a yanyara mata kitso ........
Wata mata da ta tsare Walyn da kallo tunda ta shigo ce ta yatsina fuska, a ranta ta yi murmushi tana ayyana ba laifi , matar tasa bata da laifi,
Kadan ta dan muzguta ta dubi cousint dinta dan daudu wanda suka zo gyaran gashin tare da shi ta ce" ina son aikin General a rayuwana, ina son yanda yake cin uwar kananun yan iska!
Kallota ya , ya wani yi far da idannuwansa, ya yatsina fuska tamkar mace ya ce" ke kawa, ya iya tata rashin mutunci ne fa, mutumen nan kin san da matar tsohonsa ce ya rufe? Uhum ke ni ko a lahira bama fatan mu hade da General Wardugu domin bashi da mutunci, ya iya aiki da doka, ke matarsa fa ta yarda ta kai dare a waje sai ta kwana a cel!
Daman inda take so a tabo mata kennan dan haka ta maida hankalinta sosai ta kali dan daudun nan ta ce" kawaliya matar naci ta taba daraja ne?
Walyn dake kalonsu tana kada kafarta, ta kai dubanta wajen mai saloon din, ta maida wajen kawarta da ta yi kasake itama tana jiran gannin me zata yi? sai sauran matan dake wajen da yan tsirakun ya daudun dake wajen suna suba nasu sha.anin.....
Walyn ta saki murmushi mai ciwo, ta daga idannuwanta cike da isa da takama ta ce" Wardugu kennan, mijin mace daya, jarimina mai ban tsoro, Warduguna zazafa ne, kawata kin san Wardugu baya bin kadangarun bariki? Ke na yi imanin da Wardugu na bin mata zai je ya zabo zuga zuga ne, wa.inda idan ya zaga zai dire chek ba wai ya dane karamar yar bariki ya kasa iyanta harda kason shekara sanadiyar rabuwa da mace ba!
Dan daudun nan ne ya sheke da dariya yana duban matar da suka zo tare, wace ta ji abin tamkar saukar guduma domin mijinta ne ya jewa wata yar bariki ya ki biya sannan ya yi mata duka hakan ya sa harda su kaso, wani tukukin bakin ciki ne ya taso mata, bata tsamaci jin haka ba , abin ya dake ta,
Kallonta ta yi da yannayin bacin rai ta ce" ke Walyn kike ko wa? Kin san ko wacece ni?
Walyn ta fizge hannunta daga hannun mai saka mata farcen ta ce" ke ce katuwar yar barki marar aji! Sai me kuma?
Mikewa ta yi itama ta ce" ke din ba yar barikin bace? Ke naki a boye kike yi ko ji kike ba.a sani ba? Meye bambancinki da yar bariki? Ke kawai bakya yi dan kudi ne aman menene bakya yin? Ko dan kina rufe takunki ne baki san wa.inda kuke labewar da falasawa ba? Ki jika ki ajiye Wardugu General ya fi karfin zama da mace daya wace na sani ne bakima goge a kai shi wata duniyar ba! Zaki ga aikin gogagiyar yar bariki domin Wardugu katuwar kadara ne wanda malakarsa sai tsayaye ba isa ce zata kai ki ba mu je zuwa!......
Walyn ta yi murmushin rainin hankali kafin take bufe jakarta,
Yan jika goma goma ta fitar dami guda ta bale yar takardar dake zagaye da su wace itama sai kyali take, ta dauki bakin gilas dinta ta jefa katuwar wayarta a jaka ta juyo sosai wajen matar da sauran mutanen saloon din ta daga kudin nan ta sake su a iska wanda hakan ya saka du suka shiga wawusoso harda mai saloon din da yarenta kiwa na nema har wasu suka shiga dambacewa , aman banda wace ake kira da kankana!
Walyn ta bi kawayen da kankana ta zo da su da ido ta ga suma sai wawa suke harda yan daudun,
Yatsina fuskarta ta yi ta ce" abokin mai kanwa ba ya rasa burbudi, Wardugu ya daure min a niger tunda ya sakar min yayan banki, na kwana lafia koda Wardugu ya shiga tsakiyar yan bariki ba zata motsa ba domin kyankyaminku yake!
Ta kara taku har gabanta ta zaro idannuwanta ta ce" ki sauke girman kai ki duka ki kwashi kudi.....su kike kwadayi!
Iska ta ja ta kaiwa Walyn duka warda itama ta damketa suka shiga dukan junnansu,
Sai da suka lilisa junnan su sannan mutanen wajen suka shiga tsakanin su kowace na haki,
Walyn ce ta warce jakarta ta yi gaba inda kawar tata ta biyota da gudu tana kiran ta tsayata, aman ina cikinta take ji yana wani irin hautsina mata, bata san me ke damunta haka ba yanzu, ya kasance tana yawan jin abubuwa a tatare da ita,
Wardugu ya jima wajen Ayya, inda suka tatauna sosai sannan ta saka shi a gaba kan sai ya ci abinci,
Agaishat na fitowa ta nemi Mu.azam, sai dai bata ganshi ba hakan ya saka ta fice ta nufi wajen runfar Ayya mai wani ni.imtacen sanyi tana neman Mu.azam,
Nan kuwa ta same shi, ya kurawa waje daya ido, ya zurfafa sosai a tunani wanda yannayin fuskarsa ta nuna ba tunanin dadi yake yi ba,
A hankali ta karasa ta kuma maimaita salamar da ta yi ta yi masa tun daga dan nesa da shi,
A dan tsorace ya kalota kafin yake daidaita yannayin fuskar sa ya amsata yana mai kokarin gyara mata kujerar dake kusa da shi,
A hankali ta ja ta zauna tana dubansa, yannayinta ya nuna itama ta shiga damuwar da yake ciki,
A hankali ta ce" me ke damunka ya Mu.azam?
Daman ita yake kallo, dan haka ya bi bakinta da kallo yanda ta fadi maganar a hankali sannan a cicire domin dai tana faman koyon yarensa ne,
A nitse ta janye idannuwanta daga cikin nasa, domin kallo nr yake mata tamkar zai fada idannuwan nata take ji,
A hankali ya ce" Agaishat,
Ta dago tana dubansa, inda a take ta ji gabanta ya fadi da yannayinsa,
Mu.azam ya ce" kin san soyaya?
Agaishat ta zaro idannuwanta tana dubansa, tama rasa me zata ce da shi,
Mu.azam ya ce" kin taba yin saurayi wanda kika ji kina so?
Agaishat ta saki murmushi mai kama da na sakalci, domin ita abin har ga Allah dariya ma ya bata, A hankali ta maimaita kalmomin" *So, Soyaya, Saurayi?*
Mu.azam ya dan kankance idannuwansa ya ce" yeah,
Agaishat ta dube shi, duba na ido da ido kafin take fadin" *Ban san shi ba*!
Da mamaki yake kallon ta, bata san shi ba tace fa? Aman daga ina Agaishat ta fito haka? Ko dai masu son nata ne basu yi mata ba?
Yin wannan tunanin ya saka gabansa ya fadi, a ransa ya ayanna ya salam, kar dai a je nima ban yi mata ba,?
Muryarsa sanyaye ya ce" du a maneman soyayar ki ba wanda kika taba jin kina so?
Agaishat dake dubansa itama, bata dago ina ya nufa ba, domin dai ita ba.a taba kamanta za.a ce ana sonta ba, dan haka ta bashi hankalin ta sosai ta ce" ba wanda ya taba fada min ya ake so din ne,
Dariya ya shiga yi kasa kasa yanai mata wani duba kafin yake fadin" ba fa zolayana nace ki yi ba Madame,
Bata san kalmar madame ba, aman ta gane yana nufin wasa take yi masa, dan haka ta ce" ban taba yin saurayi ba, ko an zo zaben yan mata a gidan mu ba.a taba zabena ba, Ba yace dan na cika baki da muni, ni ba alkhairi bace dan baki ba alkhairi bane, hakan ya sa ba mai zabena bare a biya sadakina, har kanwata an zaba sai dai kafin auren ta rasu ita,
Dubanta yake har ta gama yi masa bayani da kwatance da komai dan ya gane da kyau, ajiyar zuciya ya sauke a ransa ya ayanna na godewa Allah ai da basu zabe kin ba da sun saka ni a ukunna,
A fili kuwa ya ce" wa ya fada maki baki ba alkhairi bane?
Agaishat ta ce" da alkhairin ne, da mahaifina bai kyamace ni ba da alkhairin ne da nima ana yi min dinkuna irin na yan uwana, da alkhairin ne da jama.ar gari sun mutunta ni a matsayina da dan adam mai daraja a cikin halitun Allah, da alkhairin ne da na yi saurayi koda mahaukaci ne a *Gida*,
Katseta ya yi da fadin" aman sai na ga kina da ilimin adini sosai, ya aka yi kika kasa imani da haka?
*Agaishat , malamata, wa ya halici fari da baki,?*
Agaishat dake dubansa ta sada kanta a hankali, kafin ta ce" Allah ne,
Shin da ya halici baki ya kawo wata ayya a alkur.ani mai girma, a hadissai ko wani litafin na adinin fake nunin bakar fatar nan da ya halita ya haliceta ne dan wani laifi? Ko mai wani laifi?
A hankali ta kuma fadin" aa, ban karanci haka ba,
Mu.azam dake dubanta ya ce" Bilal, bawan Allah, wacece kalar fatarsa? Ya darajarsa take?
Dago da idannuwanta ta yi ta ce" baba tsofo ya ce shi ne ya fara kiran sallah , ya ce mutun ne mai daraja, makusancin fiyayen halita,
Mu.azam ya gyada mata kai kafin yake ciro wayarsa ya samo hoton ka.aba ya ce" zo ki ga ka.aba a hoto Agaishat, zo ki gani...
A hankali ta matsa tana kallo, kalar bakin ya tafi da imaninta, abin ya yi mata kyau a ido, a hankali ta kai yatsarta ta dan shafa hoton,
A hankali ya ce" ba wani bawan da ya fi daraja, ya fi kusanci fa ubangijinsa sai mai yi masa biyaya, mai tsoron shi, mai kiyaye dokokinsa, a cikin nan kin ji an ce *Farar fata ta fi bak'a?*
Agaishat da take jin wani yamyamyam a jikinta na dadi ta girgiza kanta,
Mu.azam ya ce" makafi ne ko kwakwaluwar su bata ja? Ya aka yi basu yiwa abin kaunata wawa ba?
Da sauri ta kallo shi,
Kansa ya dan sada ya ce" kina da tsararen kyau, fitinanan kyau, baki da tsayi Agaishat...baki da kiba har can, yannayin jikin ki ya tafi da yannayin tsayin ki,
Bakin ki ba mai tabo bane bare shaida, gaba daya ya tafi iri daya ne baki mai haske mai nutsuwa, agaishat, fuskar ki yar doguwa ce mai dauke da dara daran idannuwan da a kowani yannayi kike su kadai sun ishi mutun, Agaishat Allah ya tsara ki da hanci mai tsayi mai yan kofofi wanda ya yi das da dan madaidaicin bakin ki,
Rashin hayanniyar ki ya hadu ya kara kawata halitar ki, ke da ba dan kar na kauce hanya ba da na fada maki sauran tsaruwar ki,
Dan dakatawa ya yi gannin yanda ta zuba masa ido, sai a lokacin ya tuna ya saki baki sai zuba yake mata,
Dan kimtsa kansa ya yi a hankali ya ce" Agaishat arrrakam (Agaishat ina son ki),
Wata irin faduwa gabanta ya yi, da wani irin firgici ta akle shi, tsoro, mamaki, surprise, murna suka hade suka saka jikinta ya dan fara rawa, So na? Ji ta yi wani nauyinsa ya diri mata,da sauri ta sada kanta kasa, kafin take mikewa da wani irin sauri ta jua inda Mu.azam ya mike yana kiran sunnanta daidai Wardugu ya yi kokarin kawar da kansa dan kar su ganshi bayan ya jima wajen,
Ganninsa ta yi yana ta faman taba labulen ayya wanda ke gyare tsaf a wajen aman kamar wanda yake gyara shi,
Kanta ta shiga sosawa kafin take dan rabar gefensa ta shige ta taka matatakalar da gudu gudu ta nufi dakin ta,
Da ido ya bita, da wani irin kallo, a hankali ya lumshe idannuwansa ya juya ya fice a dakin ya nufi wajen mu.azam da ya koma ya zauna ya dan dafe kansa da hannunsa cike da tsoron kar a je ta ki karbar sa,
Gaban wardugu ya ji na wani irin gudu wanda har ya ji wata yar zufa ta karyo masa,
A dan hanzarce ya karasa wajen amininsa yana mai cike da zulumin yannayinsa, a nitse ya kai hannunsa ya ce" Mu.azam?
Agaishat na shiga dakinta ta karasa da sauri wajen madubi, lufayar jikinta ta warware ta tsurawa kanta ido, du abinda ya fada take son gani sai dai ita bata wani gannin kyanta, , .....
A hankali ta kai zaune ta cuje abinda ta daure gashinta da shi wanda hakan ya baiwa gashin damar zubowa baki dayansa ya yi lumbuk a jikinta, hannayenta ta cusa ta fashe da wani kuka mai zafi, a hankali, muryarta na rawa ta ce" Anna, ina kike? Anna wai yana so na? Ashe nima mutun ce Anna? Anna wai ina da kyau, wai nima mai daraja ce, Anna nima na yi saurayi...........tana kukan kuma ta shiga dariya a hankali ta furta" Mu.azam, nawa😌😌😌😌😊😊😊😊😊😊😊
I.m sowi fans , jiki da jinni ne 🤦♀
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3️⃣5️⃣
A hankali Wardugu ya kai hannunsa ya taba Mu.azam, murya a sanyaye ya ce" Mu.azam?
Da sauri ya dago da kansa daga yannayin da ya afka, ya kali Wardugu da kyau kafin yake sakar masa murmushi,
Wardugu ya ce" me me ke damun ka?
Mu.azam dake dubansa ya dan sada kai, ya kuma dagowa yana dubansa ya ce" jinta nake a raina har jikina Wardugu, sai dai ban san ba ko zata aminta ta aure ni a dan kankanin lokaci kafin mai yiwuwa ta yiwu da ni?
Wardugu ya ji gabansa ya fadi, Allah yana ganni idan da abinda ke tayar masa da hankali a yanzu bai fi rashin lafiar Mu.Azam ba, lamarin na girgiza shi in ya tuna, yakan tsinci kansa ba karfi bare laka a jikinsa idan ya tuna, .......
Duk da ya fahimci wa yake nufi aman sai ya kashe ido guda yana kallon Mu.azam ya ce" kai, soyaya ka afka daga zuwa garin mu? Fada mini wacece mai sa.ar samun abokina ?
Mu.azam ya lumshe idannuwansa ya ce" Wardugu, na kan ji wani iri idan muna hira da kai a yanzu, domin du ka canza min kan da, a da idan muna hira tamkar yaki muke, ka warto ni na tsokaneka mu yi ta shirirta har sai an shiga tsakanin mu, aman a yanzu du abinda zan maka sai na ga ka wani yi shiru ka kyale ni ko kuwa ka wani lalaba ni, malan matarka ne ni? Ko dan bani da lafia? Ni irin yanda muke da ya fi birge ni, sai ka wani dawo ladabi?
Wardugu dake kallonsa ya ji zuciyarsa ta mugun karye, hakan ya saka wata zufa ta karyo masa, a yanzu da suke zaune a haka ba mamakin shi wardugun shi ne gawar fari, aman kuma rashin lafiar Mu.azam da ta bayana kanta ne ake kiran kisan mumuke, domin dai ta hana kowa walwala tsakanin mutane ukun nan, Mu.azan din, docternsa, sai Wardugu da ya sani shima,
Wardugu ya saka hannunsa ya share gumin da yake , ya miko hannunsa kusan na Mu.azam ya ce" wa kake so? Ko yar gidan waye, ko wa take takama da shi nan duniya sai ta aure ka, kuma dole ta so ka!
Mu.azam ya kwace hannunsa yana dubansa da yannayin tausayi, ya san waye Wardugu farin sani, wannan yannayin da yake ciki yayi imanin da ace zai samu kuka da ya koka tun karfinsa ko zai samu sauki,
Goshinsa ya dafe yana dubansa, ya ce" ka daina damuwa da lafiata Wardugu,
Wardugu ya katse shi da fadin" idan muka gwada aikin nan fa?
Mu.azam ya ce" bayan ka tirsasa ni shan lemun tsami cikin ruwa masu zafi, kana tirsasani cin tafarnuwa, kuma zaka bijiro da maganar aikin da na guduwa ? Wardugu aikin nan fa mai yiwuwa shigar da za.a yi da ni a fitar maku da gawata,
Wardugu ya ce" kuma tana iya yiwuwa a fitar mana da kai ras ka sami lafia,
Mu.azam ya ce" mafi akasari idan Allah ya yi an sami lafiar ma kwakwaluwa na tabuwa, ko a samu shafewar tunani, cikin kaso dari bai fi 2/100 suke mikewa garas ba Wardugu, na fi son idan ta Allahn ce zata kasance da ni nan kusa ya kasance ina kusa da mutanen da nake so suke so na,
Wardugu ya kura masa ido, kallon cikin ido, ya ce" ba zan iya ba, zuciyata mai mugun rauni ce a kanka, ina jin rashin karfi a abinda ya shafe ka, baka yi min adalci ba idan har ka yi min haka, !
Ya mike ya dauki kys dinsa, ya dora hanayensa saman table din yana dubansa ya ce" baka isa ka min haka ba, ba zan taba barinka ka yi min haka ba! Zan nemi karin bayani ......
Juyawa ya yi ya fice inda yake jin kansa na mugun sara masa,
Mu.azam ya girgiza kansa bayan ya bi shi da kallo, a hankali ya furta" ban so ka ji ba, sai dai rigumarka ta saka ka tankalo abinda zai hana maka nutsuwa!, ya hana maka jin dadi!
Tukin garari ya yi wanda ikon Allah kawai ya kai shi gidansa lafia,
Yana zuwa ya sauka daga motar ya rufe ya nufi bangarensa kansa duke yana mai jin yanda yake sara masa,
Har zai bude ya shiga, sai ya fasa ya dubi bangaren Walyn,
A hankali ya juya akalar tafiar tasa ya nufi bangarenta yana wata irin tafia wace da ka gani zaka fahimci da karfi ne ake yinta ba dan ana jin dadinta ba,
Wardugu na shiga ya zarce falonta baba inda kamshin turaren da aka turara ya yi masa salama.
A hankali ya shige yana hangenta kwonce saman doguwar kujerar falon nata tana danna waya ranta da yannayin bace, sannan da maganin zazabi mai tafasa a gefe da alama dai ita ta sha bata jin jikinta,
Da sauri sauri ya karasa gareta yana mai cire rigar tasa ta sama ko zai ji dan sanyi sanyi ya karasa wajen Walyn da ta zabura ta mike tana dubansa da wani irin yannayi mai fasara abu uku, na farko ganninsa a bangarenta, na biyu yannayinsa ya firgitata, na uku mugun haushinsa da take ji domin yanzun ma a cikin grup dinsu na manyan mata ne ake tatauna maganar har wata na ikirarin ita walahi a duniya ba wanda ya yi mata irin wardugu halayensa na kasheta da dadi, idan ta kali hotonsa takan jita a wata duniya, tunani take wannan mutumen ya kasance hazarsa a gabanta kadai ya isheta, duda an kwabeta cewar da matarsa a gidan fa , kamar an zungureta ne an tirata domin a lokacin ne ma ta ce" Wardugu ai mijin mace hudu ne wanda Allah ya halita masa ba wani shege ba, duniya kuwa idan takamarka sauko wani a can ya kwana,
Tana wannan tunanin wardugu ya karaso jikinta, batai tunani ba ta ji ya rungumeta da karfi wanda sai da ta ji kamar numfashinta zai tsaya dan ya kanainayeta ya hana ta motsi,
A hankali ta rungume shin itama, ta shiga sauke ajiyar zuciya tana shakar turaran jikinsa wanda koda ya yi zufa bata hadewa da turaran ta bayar da wari wari, turaran ke cin karfinta bama zaka gane ba sai dai idan mafi kusanci da shi ta ji gishiri gishiri a jikinsa a irin wannan yannayi 🤣,
Gajiya ta yi da tsayuwar domin daman ba wani karfin jikinta take ji ba,
A hankali ya bita saman kujerar domin shi a wannan lokacin bashi da bukatar komai sai na ya jima a jikinta , ta rungume shi, yana so ne kawai ya ji shi a jikinta ba komai ba,
Haushi Walyn ta ji, aa me wardugu ya dauketa ne? Jiya ya gama wulakantata, ya fanshi jikinta, ya tashi ya yi tafiyarsa, ta je saloon ta kwashi rashin mutunci dan shi, ta zo gida mata na wawarsa shi oga! Yanzu ya kuma dawo mata da bukatar sa? (Domin a tunanin ta , bukatuwa ce ta dawo da shi a irin wannan lokacin ),
A hankali ta zame jikinta tana dubansa yanda ya yake ringeshe jikin kujerar idannuwansa du a lumshe,
Baki ta dan yatsina, a fili ta ce" ka san yau a saloon wata karuwa ke ikirarin sai ka aureta?
Daga yanda yake kwonce yake dubanta, a hankali ya ce" ki zo gare ni Walyn.....
Ya mika mata hannunsa,
Kafadarta ta make irin na yangar nan na mata ta ci gaba da fadin" ka saurare ni mana, ina maka hira ka wani basar,
A hankali ya kai hannunsa wajen goshinsa kafin yake mata alama da ta ci gaba, domin ya lura kwata kwata matar tasa bata lura da yannayinsa ba, bata da niyar fara sauraronsa, zata tiso abinda ke damun nata wato *kishi da isa*,
Zamanta ta gyara tana mai dubanda da kyau ta ce" ni kuwa na bata amsar cewa , Wardugu mijin mace daya ne, ba zai kula wace ta san mutuncin kanta bama bare ita karamar yar bariki, Wardugu nawa ne ni kadai!
A hankali, ba tare da wani damuwa ba ya ce" *wa ya yi miki wannan albishir?*,
Da sauri ta dubo shi, da yannayin mamaki ta ce" me kake nufi?
Dagowa ya yi yana dubanta ya ce" *Auten zobe muka yi da ke?*,
Walyn ta kara zabura da mamaki ta ce" kana nufin sai ka kula wata macen?
Wardugu ya buda idannuwansa da kyau, ya ce" *To waye ni?* , an fada maki ni ba mutun bane? ,
Yanzu sai ka ci amanata Wardugu? Sai ka dubi wata macen da sunan so?
Kallon kar ki raina min wayo ya yo mata sannan ya ce" tunda hirar kike so mu yi bari ki ji, da farko dai ni mutun ne dan Adam wanda nake tara ba goma ba wanda nake cike da laifuka , nake dauke da zuciya mugun nama, wanda na kwonta da sannin Allah ya halasta min auren hudu na jera, nake da sannin ina da wajen saka su, ina da abinda zan ciyar da su, na tufatar da su, sannan ....ya yi murmushi ya ci gaba da fadin" na sauke hakinsu saman lit (bed) ba tare da gajiyawa ba! Ke kin san wa kike aure shi ya sa kike kishi! To a haka da nake, akoy wa.inda ban yi masu ba, sam bana gabansu, bana cikin tsarin da zan samu koda gaisuwarsu ne! Walyn, ana aure dan soyaya, da tausayi, dan sha.awa, dan arziki, ba zan maki karya ba, ba zan yi maki rantsuwar ni na isa na kauce kaina daga kan *mace yar dagwas dagwas mai dorinar dukan maza ba* , ciki kuwa koda yar barikin ce da kike fadi mai yiwuwa na zama silar shiryuwarta!
Gaba daya har Walyn ta fara fita a hayacinta , ta hayayako ta ce" me na gaza da shi Wardugu da kake kiran min sunnan wata a gabana?, *Kyau, fari, tsafta, girki, iya tarairayarka,* wane na gaza a cikin nan?
Haushi ya kara kama shi, itace ke ikirarin iya tarairayarsa bayan yanzu ya shigo mata a wani yannayi maimakun ta dubi halin da yake ciki ta zauna a kusa da shi aa, sai ma ta tsankalo kabarun banza da wofi, kai da Walyn a wajen aikinsa take kai koda ficewa take ta hanyar da an kwashi yan kalo da ita da matan dake kai masa ziyara, wai kuma ta yi ikirarin ita ta san kanta ita mai kyau me memememe, *Isarta* ta hanata ta duka masa yanda ya dace, takamarta da halitarta sun hanata gane ainahin biyayar aure, sai idan baki ya bude ta shiga zubo masa abubuwa mararsa tsari, dan haka da yannayin haushin nan ya mike yana daukan rigarsa ya ce" *Kin san dadin miya ke sakawa a yi kari!*
Wai wai wai wai , shin fans zaku kuwa iya zama da mai hali irin na wardugu🤦♀🤦♀🤦♀,
Su waye wardugu ke ikirarin ko arzikin gaisuwa baya samu daga wajen su? Me ke damun wardugu?
Me ke damun kwakwaluwar Wakyn? Ta hada kyau, fari, tsafta, kanshi, girki, bata isa ta daki kirjin mijinta na ita kadai bane?🤔
Mu.azam, zai kai labari kuwa?
Agaishat Ayya, Anna, Ba, Marahut, ya labarin su ne?🤔🤔🤔
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3️⃣6️⃣
Rigarsa ya rataya a kafadarsa, ya juya da niyar barin mata bangarenta domin bai ga dalilin fa zai saka a caza masa kwakwaluwa a waje, ya zo wajenta dan samun nutsuwar zucuya itama ta caza masa, yana bauwa Walyn damarta ta mace, na ta yi korafi a kan abinda bai mata ba, ya sha duba korafinta ya nuna mata ya tuba a aikantance ta hanyar daina abinda ta kawo masa korafin a kai, sai dai abubuwa na damunsa na irin yanda ita ba abinda ya sha kanta da damuwa da damuwarsa, bata wani damu da yannayin da zata ganshi ba indai da abin fada zata rufe ido ta fada da gatsali,
Murmushi ya yi yana girgiza kai bayan ya kare mata kallo du ta fice a hayacinta daga wannan yar maganar? To idan Allah ya kadarto min kara aure yaya zamu kwashe da Walyn?
Rai bace tana kokarin fashewa ta kuka ta ce" Wardugu, idan ka yarda, idan ka saki, ka yi saken kula wata mace sai dai a kwashi gawarwakin mu baki daya! Wardugu kamar yanda Batuben namiji zai iya suka da wuka dan an kali matarsa toh zan iya suka da wuka dan an rabe ka!
Tsayawa ya yi yana dubanta, iya gaskiyarta ta fada domin a tsaye take tana dubansa ido cikin ido, jikinsa ya ji ya dan yi sanyi, karasawa ya yi kusa da ita , ya dan sasauta murya aman a cunkushe ya ce" Walyn, bakya aiki da adini ne ke? Kin san da sunnar ma.aiki ce? Me ya sa zaki daukarwa kanki zafi haka? A haka Walyn ban ma nuna zan yin ba idan zan yi fa?
Idannuwanta ta dago dan sakawa cikin nasa domin ya darata tsayi, ta ce" na tsinci kaina a zazafar kaunarka, haka na wayi gari na ganni zundum , na shanye wulakanci kala kala dominka, kai da kanka ka sha wulakanta ni mai girma, karaya uku ka min a gabai na, du na shanye! Kai a tunaninka ba zan shanye azabar kawar da du wata tsagerar da ta tunkaroka ba? Wardugu, mahaukaciya ce ni a kanka! Sakara ce da a yaren ka! , kamar yanda ka sumar da saurayin da ya yaba maka ni, ni kuwa ka yi min marin da na yi ta ihu sai da kyar jina ya dawo dan na yi kwaliyar da aka yaba ni, haka zan iya rike makigwaron du wata yar iskar da ta yabe ka!
Kansa kawai yake dan girgizawa yana dubanta, Walyn, walyn Wardugu...ya saki murmushi ya juya,
Haushi ya kara rike mata zuciya ta daga murya ta ce" ciki kuwa harda wannan tsohuwar kilakin da ta ki aure take binka gida ma.aikata, anguwa! *Alhinayett*, ciki harda ita,
Dawowa ya yi ya tsura mata ido, kafin yake fadin" ki daina zagin Alhinayett domin mai son ki ce, tana yaki kan ki, tana yi min fada kan ki,
Karuwancin kennan! Karuwancin kennan Wardugu! Ta shiga jikinka har ka ji in ba ka kasance da ita ba , ba zaka ji nutsuwa ba!
Wardugu ya zauna saman kujerar dakin ya ce" Walyn, Alhinayett ba yar bariki bace, mutun ce mai daraja, mutunci ne tsakanina da ita, ke kin san da soyaya ne da tuni na auri abina na kilace, jimawarta ba aure kuwa Allah ne bai kawo lokaci ba, aman an kusa saka aurenta, ki daina magangannu irin haka Walyn , ke macece, ko a kan ki ba haihuwa zaki yi watarana, ba.a so mutun ya cika izgili,
Kai ta kawar ta ce" wardugu, gaskiya ne baka so? Alhinayett ai kowa ya san kilakin ka ce!
Wardugu ya mike a karo na uku kennan, ya karasa kusan Walyn yana mai binta da kallo, hannunta ya damko ya bude yana dubawa, ya riko fuskarta ya daga idannuwanta yana dubawa, ya gwale bakinta ya saka yatsunsa ya ciro harsanta yana dubawa, ya saki ya kama rigar dake jikinta ya dage sosai har biyu suka bayanna, nan ya tsura masu ido yanai masu kallon kurullah,
Cikata ya yi , ya dan taka ya tako kafin yake nunota da yatsarsa manuniya, muryarsa ya saki baki daya ya ce" Ba karuwa bace! Aminiyata ce, du wanda ya zagar min ita zan bata ransa! Kika kuma kiranta da karuwa na rantse da girman mahalicina sai na aureta koda kuwa ta tsane ni , koda mutuwa zata yi dan kina na kawota na kwana da ita saman gadon ki! Ke da ba dan ina hangen kamar mai shigar ciki ba yau da na nuna maki tsagwaron rashin mutunci! Ya ina taro ki kina raina min hankali? Walyn ni in ban kara aure ba ni ba dan babana bane!, ni ba jinin tubawa bane! Walyn dole ki zauna da kishiya in baki kona mu ba ke ba yar babanki ba ce!
Fuuuuuu ya juya ya fice yana jin kamar ya koma ya yi kwalo da ita, sai dai yana tsoron kar a je ciki ne da ita, ta ja ya yi mata lahani bayan adu.arsa kennan shima allah ya azurta shi da haihuwa, yar bakin ciki kawai take jan sa masifa salon ya biye mata idan cikin ne su barar su shiga uku!
Haka ya koma bangarensa ya zube a falon sa ya yi ruf da ciki ya dora hannayen sa saman kansa yana yamutsawa yana tunanukan rayuwa,, walyn ba wayo , haka ya ayyana a ransa kafin ya kuma fadin....ta saka sai na kara zama da wata macen? Walyn shirme shirme🤦♀,
*Timiya*
Amai take kwararawa har kamar ta shide, inda *Ba* ke tsaye ya dan duka dan tsayinsa, da rawaninsa yana dubanta,
Gefe guda kuwa su Anna ne da yayanta yauma Gaishat ta kawo mata ziyara da dan cikinta da ya tasa kafan wanda sarki ke mugun zumudi kansa tkar shi ne dansa ma fari,
Suna kasan bishiyar gidan suna zaman su suna yar hirar su , domin yanzu da safiya ta yi Mariama ke fitowa ta gyara wajen ta shinfida tabarmar kabar da Anna ta siyo daga garin agadez ta dauki du abinda zasu bukata su koma can su yini abinsu , nan suke sallah su ci abinci, ta dauki na baba tsofo ta kai masa domin Gaishat na tsaye kan abinda zasu ci, sarki baya wasa da ta nuna tana da bukata ake kwasa a kai mata itama ta kwasa ta kaiwa mahaifiyarta, inda ta saka sarki ya yiwa *Ba* gargadin kar ya kuma kwashe masu abincin su,
Bakinsa yake motsawa ya juya ya karewa Anna kallo da yarenta su uku sun zagayeta, ya juyo wajen amarya dake maida lumfashin kadangare bayan ta gama sheka amanta,
Tabar sansaninsa ce yake gumtsa a bakinsa,
Bakin ya bude ya totofar da yawu, domin du mai shan tabar sansani ya kasance yana tofe tofen yawu, ya juyo wajen amarya ya ce" sannu *Uwar mai uba biyu*,
Kallon kasan ido ta yi masa kafin ta kada kai,
Juya kansa ya yi wajen Anna ya ce" duniya, anai min kallon ina yiwa yarana aure suna tafia birni, ke gashi kin dauki yar santal ki badata yawon kilaki!
Da sauri Anna ta kallo shi, gabanta ya fadi,
Kura mata ido ya yi ya ce" karya na yi? Ke yanzu zaki daki kirjin yarinya na hannun kirki? To ni dai in tana aiko wani abin ake boyewa ana ci Allah ya isa! Dan ko dan ciyar da ita da na yi ya isa a yaga mini wani abin ba a rufe ni da baibai hannu ba!
Gaba dayansu dubansa suke,
Ya tako da fararan kafafuwansa da sukai fari fat na kasar garin ya dubi Gaishat ya ce" ke kuwa fa? Haka zaki saka mini ko? Kin samu na aura maki sarki , ya nada ki sarauniya aman ni kika saka kafa ki ka shure ni sai wannan tsohuwar matar kike baiwa abinki ko? Ai dukan ku Allah na kallon ku! Ko hakin ciyar da ku da na yi zai bi ku,
Ya kara tofar da yawu yana duban Mariama dake bin sa da wani mugun kalli itama da sansanninta a bakinta kamar na sauran yan uwanta da Anna, ya ce" ke kuwa ke ce gagarara ko? Mai tarda ni wajen majalisa ki tirke ni gaban abokaina, ke mai karfi wace ta fi kowa iya rashin kunya, a gaban yan uba kika yi ikirarin zaki ga ubanda zai maki aure ko? Ba laifi, ba laifi Mariama, in sun zo sai mu basu gidan su saya su tafi mu kuwa mu koma zaman titi ,
Mariama ta yatsina bakinta ta kawar da kanta,
Babar rigarsa ya kabe ya ce" kudinku yanzu na fara ci, ni da ku ba shari.a domin ni na haife ku! Dole na yi maku aure na mori kudin ku! ,
Ke kuwa, ya nuna Anna da take jan dan karamin carbinta tana shamaninta ya ce" kin ji kunya, anai maki kallon saliha sai gashi kun hada baki da tsohon can kun tura yarinya nema; ana zaton wuta a makera su Annar yara sun kunata a masaka.
Yana gama fada ya fice a gidan yana ta tofe tofensa,
Mariama ta dantsa yatsarta a bakinta tana yiwa yayarsu kallo mai kama da harara, domin ita ta yi masu kashedin kar ta kuma gannin wani ya biye masa, dan ta lura hakan na masa dadi
Gaishat ta yi murmushi tana dubansu ta ce" baku lura ya fara yin sanyi ba?
Mariama dake hararar Amaryar Ba ta ce" sanyi? A wannan tsohin najad.....
Bige bakinta da Anna ta yi ya saka ta kasa karasawa tana turo baki,
Da yannayin bacin rai ta ce" in kina irin magangannun nan hankalina tashi yake, mahaifin ki ne fa, ko me ta zama adu.a ce tsakanin ki da shi, ya zaki ringa halaya irin na wace bata da tarbiya? Bana so Mariama ,
Aman Anna, kina ganni abinda yake yi fa, ke tsoronsa kike , to ni bana tsoron sa,
Kuma bakya tsoron Allah? Gaishat ta fada tana dubanta, hakin dake tsakanin ki da shi na matsayinsa na uba Allah ba zai bar maki ba, ki bi shi, ki yi masa biyaya, ki bar shi idan shi gobensa bata dame shi ba kai nasa,
Shiru ta yi tana duban fatimata dake dan zane a kasa ta ce" wacen matar ciki ne da ita fa? Kuma kum san ba cikin Ba bane,
Anna ta kwalalo ido tana dubansu, a dan harzuke ta ce" na ga mai isata yau da yaren nan, kun yi da shi ne? Bama wannan ba sa.anku ne? Du wace ta kuma gigin muguwar magana a kan mahaifin ku a gabana zamu bata da ita! Ba ruwana ban koya maku ba, baku ga ina yi ba, kuma idan na ji tsoronsa ai ba laifi ba, shugana ne, wanda aljannata ke karkashin kafafuwansa, a haka ma ya muka kare da shi bare na yi masa gatsali? Ku daina bana so!
Ta karasa tana dan dafe kanta domin har ya sara mata maganar nan da ta yi,
Da dadaya suke bata hakuri suna masu lura da yannayinta.............
Daga inda yake ringeshe yake biya bagara a fili hannunsa a kan zuciyarsa,
Sai da ya kai karshe ya samu ya dan daga ya jingina yana duban hanya dan ya san yanzu Mariama ta zo,
Yana jin dadin lamarin mariama sai dai ita ba.a hira da ita, kimkim take masa har yanzu haushinsa take ji, bata san irin yanda shima hankalinsa ke kan Agaishat ba, adu.arsa a gareta ne, da fatan saduwar fuskokinsu kafin ya koma ga mahalicinsa,
Jama.a Wardugu na neman karin aure🤣, du mai son karya kafa ta shigo layi🤦♀🤦♀🤦♀................... dan Allah aunty Alhinayett kar ki tura masa wannan page din wollah lalla batai kwari ba kar ya karya min kafar nima😟😟😟
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3️⃣7️⃣
Yana nan zaunen kuwa sai gata ta shigo da salamarta ciki ciki,
Ajiye masa robar abincin ta yi bayan ta dan jefa masa wani kallo ,
Wajen ruwa ta je ta dibo masa ta zo ta tsuguna ya wanke hannunsa ta kuma cikowa ta ajiye ,
Dakin ta tatare kamar kulun shi kuwa yana cin abincin yana duban yannayinta, Mariama akoy shiru shiru sai dai yannayinta na yau kamar ranta a bace ne,
A hankali ya ce" me ke damun Mariama?
Tana gurza goron hannunta ta dan dago ta dube shi, ta ci gaba da gurzar abinta,
Can ta ce" idan ta zo hankalinta a tashe, ranta a bace, idan ta fada maka ka taba yi mata maganin damuwarta ne sofo?
Baba tsofo da ya gane Agaishat take nufi sai ya girgiza kansa a hankali , kafin ya ce" ban taba magance mata damuwarta ba Mariama, sai dai nakan saurare ta, na ji damuwarta, na yi mata nasiha a musulunce da girma, nakan ji ciwon damuwarta a raina na nuna mata ba dadi, aman kuma sai na nuna mata girman hakuri,
Shiru ta yi tana jinsa, can ta ce" wai dan na kire shi da mumunan sunna Anna ta dake min baki bayan bata taba koda shakunana ba, kana da labarin irin manya manyan munana halayansa, aman sai ta wani tare mashi?
Baba tsoho dai kallonta yake , har ta dasa aya tana hucin bacin rai, a nitse ya ce" su iyaye, sune masu madaukakiyar daraja in kika cire Allah da mazon sa a wajen dan adam, su iyaye Allah ya ce a bi su a yi masu biyaya banda hanyar sabonsa,
Shi abinda yake ba sobon Allahn bane yake?, ta fada tana duban Baba tsofo,
Baba ya gyada kansa yana dubanta ya ce" ya taba daukan y'a ya bayar ba.a daura aure ba?
Mariama ta girgiza kai,
Ya ci gaba da fadin" yana yin aurwn yayansa dan dukiya, adini bai jaramta hakan ba sai dai ta yannayin da yake yi ne,
Yana yi ne tamkar yana siyar da yayan,
Wa ke tafe da duniya da abinda ke cikinta Mariama?
Ya kuma watso mata tambaya,
Mariama ta ce" Allah,
Shin baki da labarin ya fi gannin abinda kike aikatawa? Ya fi ki jin abinda ke wakana a tare da ke?
Na sani , ta fada tana kawar da kanta,
Baba tsofo ya ce" shi zai kare ku!
Yana fadin hakan ya yi shiru tamkar ba shi ba,
Da mamaki take dubansa, bata san lokacin da ta dawo facing dinsa ba ta riko hannunsa tana dubansa ta ce" shikenan? Hukuncinsa kennan?
Baba ya yi mata murmushi ya ce " ke kika halice shi da zaki hukunta shi?
A hankali ta sada kanta, muryarta ne ya yi rauni ta ce" ya cika cin zalinmu, bai san darajar matarsa ba wace take mahaifiya a wajen mu, mu yayansa yakan dauke mu ne ya yi kudin mu, yanzu ya tare da matar da wani ke ziyara a kan idannuwansa, shin yaya ake so dole dole sai na daraja wannan mutun?
Baba tsofo yana dubanta ya sada kansa shima, ya dago ya ce" muna tursasa ki yi masa biyaya ne dan goben ki, kar ki ga duban laifukan da kike hange nasa, idan kika taka hakinsa a kanki na matsayinsa uba a gare ki, Allah ba zai bar ki ba, ki yi masa biyaya, sai ki ga Allah ya jibanci lamuran ki Mariama,
A hankali ta cika hannun Baba tsofo ta juya ta hado goronsa ta kule sauran ta kula a harshen zannin ta,
Miko masa ta yi wanda ta gurzan ta duka gabansa tana dubansa ta ce"ya aka yi mutun mai mutunci irinka ya rayu shi kadai? Ni tunda aka haife ni kai kadai nake gani sai almajiranka wa.inda da sun fara tasawa suke tafiarsu birni neman kudi, ya aka yi baka da mata da yara?
Dubanta yake da mamakin ashe dai ta iya magana, sai dai tambaya ne da Mariama tamkar me, komai so take ta gane ya aka yi ? Ta ina aka bi aka yi? Wa ya yi? Su waye shaida? 😅,
Iyayena yaki ya tafi da su,
Na tashi ni daya sai Allahna,
Na yi aure sau biyu a rayuwana, sai dai rashin haihuwa ya saka matan na guduna,
Me ke birge ka a rayuwar wannan daji kai daya kwal da ranka?
Tsareta ya yi da ido kafin ya ce" nan ne muhalin da Allah ya ara min,
Kalonsa take da wani yannayi na tsoro, a hankali ta mike tana dan duban yannayin dakin baba tsofo,
Fitowa ta yi ta hangi anguwar ba wani mutun mai gitawa bukar baba tsofo a tsakiyar rana take sannan nesa da jama.a,
A hankali ta waiwaya bayanta ta tsurawa kofar bukar ido, a ranta ta ayanna " *Wannan mutun ne ko aljan?*
(🥺🚶🏻♀️😳😳😳😳🚶🏻♀️🚶🏻♀️🚶🏻♀️🚶🏻♀️🚶🏻♀️)
Rakiyar Aghali aeroport tamkar za.a raka shi tafiar da ba zai dawo ba,
Idan ma ya yi salama da iyayensa kuma yin salama suke ,
Har aka fara harama kiraye kirayen suna wanda hakan ya saka shi komawa wajen mahaifiyarsa ya dan duka kansa ya ce" Allah ya ja zamanin sarauniyar garin Agadez, sai Allah ya dawo da ni.
Dago da habarsa ta yi tana dubansa ta ce" Allah ya kai ka lafia yarimana, ka gaisar min da aminiyata domin ban lamunci ka sauka hotel ba bayan gata a gari,
Murmushi ya yi mata yana daga mata kansa , kafin ya juya wajen matarsa ya sakarwa yarinyarsa kiss a goshi da kunci, itama matar ya yi mata kiss a goshinta a hankali ya ce" *Tarhanine* (masoyiya)
Dago da kanta ta yi ta dube shi, da dara daran idannuwanta ta yi masa salama kafin take juyawa ta nufi dankareroyar rangrover din su
Sauka lafia Yarima Aghali .
Yai tunda ta farka a barci ta ahige bayi ta yo wankanta ta fito ta kimtsa jikinta domin ta farka da al.adarta wace ta zo mata tsakiyar dare,
Bayan ta gama ta kuma rufa ta turara turaren wutar da ya zame mata jiki karfi da yaji Ayya ta koyar da ita saka turaran wuta a jikinta da kowani lokaci, barema idan ta fito a wanka sai ta turaru kafin ta bushe,
Sai da ta gama turaruwa ta dawo ta ciro doguwar rigar atampa , jar atampa ce mai adon baki baki a jikinta, An yi mata dinkin mai turmi , saman ya dan rike daidai kirjinta ya yi mata das sai ya bude kasan , ,
A hankali ta zauna saman yar kujerar gaban madubin ta caje gashinta wanda Ayya tace yau za.a kitsa shi, domin ana kitsawa yana warwarewa ne Ayya kuwa tace sai an yi kitso mace ce dole ta yi kitso,
A ranta ta ayanna , ina yake? Ya ya kwana? Har yanzu yana kan bakansa? (Domin rabonta da Mu.azam tun guduwar da ta yi jiya,) yanzu har karfe goma ya gita na safe, tana jin lokacin da Ayya ta shigo take fadin zasu je su dauko Aghali dan aminiyarta , sannan ta ji lokacin da mai aiki ta shigo tana fadin Wardugu ya zo Ayya bata nan, aman ina ita barci ya ci kargfinta domin idan tana al.ada takan yi wani barci mai nauyi ne,
A hankali ta saki murmushi ta kuma furta "Mu.azam nawa ,
Ji ta yi an turo kofarta dan haka ta mike tana duban kofar,
Shigowa ya yi da salama a bakinsa, da sauri ta kai dubanta saman bed dinta, Allah ya so ta abin shinfidar ya rufe pant dinta da ta ciro ta zabi wanda zai riketa da kyau ta saka, bata rigaya ta mayar da sauran ba,
A hankali ta mayar da dubanta wajensa, kafin murya a sanyaye ta ce" i....i.ina kwana ,
Yauma bai amsata ba, sai kallo da yake binta da shi na mamakin yaushe ta iya saka kaya haka? Yana gannin yan aikin gidansa har kulun su shigarsu tamkar an tsamo su daga rafi, domin Walyn nata daukan yan aiki yan birni sai yan kauye, baya taba gannin sun waye su kulun tamkar mahaukata, shi ya sa koda wasa ya hana su taba wani abin a bangarensa, hakan ya sa ta samo masa namiji mai aikace aikacen bangarensa wanda ta yi ta rantsuwar ba dan daudu bane, shi kuwa dan daudu ne idan ya shigo gidan ne yake namiji!
A hankali ta karasa ta dauki dan kwalin atampar ta daure gashin kanta da kyar , wanda yake lumbuk gaban goshinta, ta koma gaban madubin ta zauna abinta ta shiga daure gashin kanta,
Wani irin mamaki ne zai kashe wardugu dake tsaye yana biye da ita da kallo, kai! Ya fada a ransa, ya shigo ne dan ya tambayeta kys din dakin Ayya dan ya san ita zata barwa, sai dai mamakinsa, ya hadu da macen da bata nuna tsoronsa, kakahin ta birge shi, shishigi a gare shi ba, ita bata nuna tana tsoronsa ba , ita bata nuna bata tsoronsa ba, ita dai ta gaishe shi, gaisuwar da ya tsana wai wani *Ina kwana*, sai kace wani sa.anta!
Yana nan tsaye har ta gama daurin dan kwalin da ya boye baki daya gashin kanta, ta dauki turaren ruwa ta kuma fesawa a jikinta mai sanyin kanshi wanda Ayya ta sayi kwali guda irinsa sunnansa princesse ,
Kwali ta dadage ta saka sannan ta shafa dan man lebe kadan, ,
Mikewa ta yi ta juyo facing dinsa tana dubansa yana dubanta, a hankali ta shiga takawa tana nufo shi, wanda du takunta daya sai ya ji gabansa ya dadage ya fadi , da sauri ya kawar da dubansa a kanta daidai nan ya jiyo muryar Ayya,
Tamkar an hankada shi haka ya fito daga dakinta wanda har ya waiwaya da sauri yana duban kofar, hankali ya furta" innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, abinda Wardugu ya furta kennan kafin yake tura dakin Mu.azam dake kasa kadan da dakunnan su Ayya ya shige ya rufo ya nufi gaban madubi da sauri,
Duban kansa ya tsaya yi, kaki ne a jikinsa, sosai yannayinsa na ban tsoro ya bayana a jikinsa, sai dai kaki din wandon ne kawai sai bakar rigar da ya saka, a fili ya furta" ko dai makauniya ce?
😳😳😳😳😳😳
Ba laifi yau kun yi comment, dan haka ga kari😍😍😍😍😍😍
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3️⃣8️⃣
Murmushi ya yi bayan ya tabatarwa kansa da yarinyar ba makauniya bace tana gani sosai,
To aman ayar tambayar shi ne me ya sa bata tsoronsa? Ko ta tsaya ta shagalta a kallon sa kamar yanda du yawancin mata da mata ke yi? Bale ita da ga irin wajen da ta fito wato kauye zai kasance shi ya zama abin kallo a wajenta, sai dai abin mamaki tamkar ba.a yi halitarsa a gabanta ba,
Kansa ya girgiza a fili ya furta" Ayya kwashe kwashe, idan kuma aljana kika kwaso mana ba sai ki huta ba🥴.
Sai da ya gama abubuwansa sannan ya juya ya fice ya tafi falo domin yana jin hayaniyar samarin biyu da muryar Annarsa.
Agaishat tsam ta yi bayan fitarsa ta sauke ajiyar zuciya, murmushi ya kubuce mata a fili ta furta" idan Mu.azam nawa zai aure ni, cikin abokan ango da zasu zo daukana a rakumi (🙁😕😟 ke malama a birni kike🙄), harda wannan mai kama da mutanen cikin alon nuno mutane (tv),
Dariya ta yi tana dafe goshinta ta ce" kai aman katoto ne, kuma wai dan Ayya ne🤦♀, ko ta yaya ta goya shi?
Kys din Ayya ta dauko ta juyo zata fita, ta ja ta tsaya ta dubi wajen da Wardugu ya tsaya ya zuba mata ido, nuna wajen ta yi da hannunta ta ce" kai katoto, ka daina irin kallon nan, baba sofo yace ba kyau irin kallon nan da kake!
Yatsina fuskarta ta yi , ambaton sunnan baba sofo da ta yi ya sace mata lakar jiki, a hankali ta shiga takawa da zancen zucin ko ya yake? Ya Annarta? Ya yan uwanta? Ko da wasa bata tuna yannayin mahaifinta, sai ta tuna da baba tsofo sau dari bata kawo sunnan Ba a layin zuciyarta ba, tsananin tsoronsa da ya dasa mata ya saka har a zuciyarta idan ta yi kamar ta tuna shi sai ta gargadi kanta cewar ki kula Agaishat kiyayarsa gare ki madaukakiya ce.
Agaishat na saukowa, kanshin turaranta ya fara karasowa, kafin a hankali ta idasa fitowa fallon,
Da murmushi Ayya ke kallon ta, domin ta ji dadin irin yanda yar tata ta koyi saka kaya da wuri haka,
Mu.azam da ya dago daga hirar da yake yiwa Wardugu ya zuba mata mayatatun idannuwansa , zuciyarsa na luguden kida yana dubanta da wani yannayi mai nuni da " kin azabtar da ni,
Wardugu dake gefensa yana sauraron sa, jin ya yi shiru ya saka shi duba wajen nasa, nan ya bi abinda ya tsurawa ido, ya kai dubansa wajen Aghali da yana tsakar waya da mamansa yana shaida mata ya sauka lafia, aman ya tsaya mamakin wai yarinyar da Ayya ta dauko ce haka?
Da sauri Wardugu ya mayar da dubansa wajen Mu.azam, shima zuba masa idon ya yi yanai masa kallo mai cike da ma.anoni,
Salama ta yi , kafin ta zarce wajen Ayya , inda a takaice ta ce" ina kwana.......... (wannan na cikin abubuwan da Ayya ta koya mata, cewar ta ringa kiyaye sakin baki, kai ko gaisar da bako zatai ta takaita , in dai ta yi salama cikakiya halas!)
Tana zuwa ta zauna inda Ayya ta nuna mata,
Hannunta Ayya ta kama tana duba faratunnanta , domin ta umarce ta da sakawa yatsutsanta jan lale,
Ta kuwa saka , ya kama yai mata das a hannun ,
Ayya ta saki hannun ta lakaci kuncinta, kafin ta yi kiran Hanne, kan ta kawowa yarinyarta abin kari,
Kai Wardugu ya girgiza, ya mike yana daukan wayarsa ya kai dubansa wajen samarin dan ya ankarar da su , da haushi haushi ya ce" ni zan tafi,
Da sauri Aghali ya mike yana fadin" zamu tafi dai oga,
Wardugu ya ce" a mashin fa nake Aghali,
Aghali ya dafe kansa, ya kai duban sa wajen Mu.azam ya ce" docter tashi mu je ka kai ni ,
Mu.azam ya dubo su, irin yanda Wardugu ya yi kicin kicin da fuska ya san ko sun bi shi walahi zai bace masu ne, dan haka ya ce" ni sai na karya,
Idan kana so ka karye! Wardugu ya fada ya juya yana fadin" premiere dame (First lady, wato Ayyarsa), sai na dawo ,
Ayya ta amsa shi da" ka dawo lafia *War*,
Haka ya fice a gidan cike da takaicin girman kan yarinyar, domin shi kawai ya ajiye haka a matsayin girman kai, wai su *Ashak* ko? Ba buzuwa ba dai, su waye ma su buzayen nan da suka raina mutane har suke yiwa mutane Ashak?
Sosai ya kunsa a lamarin Agaishat ya bashi mamaki, wanda hakan ya saka ya dauki aniyar nazartarta a tsanake, shi zai koya mata ladabi da biyaya a haukace! (Toh fa),
Kuka take na tashin hankali tun da ta shiga bayin da kamar minti biyar, da gudu ta fito ta mikowa mamanta abinda ta yi gwajin fitsarin nata dan gannin ko ciki ne da ita? Domin tunda Wardugu ya yi maganar komai nata ya tsaya ya daina aiki,
Da yannayin farin ciki uwar ke dubanta, ta ce" kukan murna kike ko na me Walyn??
Da madaukakin tashin hankali ta ce" ba zan haihu yanzu ba, bana son cikin nan walahi sai an zubar da shi, bana so!
Da mamaki uwar ta mike tana dubanta, kafin take nunota da yatsa ta ce" ke ke ke, da hankalin ki kuwa?
Walyn ta dan tsagaita kukanta ta dubi uwar, kafin take kara barkewa da wani kukan ta ce" ba zan yarda na dauki ciki da Wardugu a wannan lokacin ba, a bai tabatar ina da ciki bama ya yi min rantsuwar sai ya yi mini kishiya ina da ya gane ina dauke da ciki?
La haula wala kuwata ila bilah, maman Walyn ta fada, ke bashi da hankali? Yaushe ma aka yi auren da har ya fara yi maki maganar zai maki kishiya? Me kikai masa da zafi? Ki bakya barinsa zuwa wajen ki yanda ya dace?, fada mani me ki kai masa da zafi haka?
Nan walyn ta warwarewa mahaifiyarta yanda suka yi da Wardugu,
Haushi kamar uwar zata dake ta ta ce" yaushe zaki gane mahaukaci ki ke aure ki iya takun ki da iya zama da shi?
Da sauri Walyn ta ce" Ma, Wardugu ba mahaukaci bane !
Uwar ta yatsina fuska tana dubanta ta ce" toh dan uban ki ba mahaukacin bane, aman wannan cikin ko aman jini kike sai kin haife shi kin sama mana magaji, ke ko me zaki yi sai kin kawo shi duniya, bara ma ki ga na fada masa, ai shi kina tsoron sa tamkar ran ki! banza sakarya marar tunani!.....
Rigima ta kirki suka kwasa kafin da kyar ta samu ta zaunar da ita ta ce" Walyn , kina bani kunya a rayuwa, wani lokacin har kokonto nake ko dai an canza min ke a asibiti ne? Ina yi bakin kokarina dan gannin kin yi fice a gidan ki aman a kulun sai da hadu da abin takaici abin mamakin da zai saka ni jin kunya,
Matar Batube, ta kasance tamkar abinda ya malaka kwalin kwal a duniya, wanda tamkar numfashinsa ne, yana ririta ta, yana kulawa da lamarin ta kafin na kowa, na sani ci sha sutura kilacewa, kayan burga ba wanda baki da, matsalar daya ne baki isa ki saka mijin ki ko ki hana shi ba! Menene dalilin haka? Na kasa ganewa, na kasa ganewa walyn,
Walyn dake zaune du ta hade jikinta, a ranta kuwa ayannawa take ko da jaraba sai ta zubar da wani tsinanan ciki, a haka ma tana cas cas dinta yanai mata maganar kishiya, ina da ta haife? Bama zai yiwu ba, idan ta haifi guda ai ta kama hanya, kofa ta budu, sauran zasu zo ko fa balaki ne, kennan shikenan kishiya ta tabata a gare ta ? Duda tana tsoron lamarin wardugu, ya yi aure haka ba tare da ya cika al.ada ba ba damunsa zai yi ba, tsohuwar uwarsa kuwa ba tirsasa shi zatai ba!
Mrning alll
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3️⃣9️⃣
*baki ba zai iya misalta maku irin yanda zuciya ke cike da farin cikin karanta ku Bak'a fans, Allah ya bar kauna baki daya*
Ya Allah, kar ka kai labarin mutuwarmu zuwa kunnen da baki ba zai fadi alkhairi kan gawarmu ba 👏🏻👏🏻👏🏻👏🏻😭
Haka Walyn ta wuni wajen mahaifiyarta , inda uwar ke kwatanta mata yanda zata yi ta ci ribar zama da wardugu, ita kuwa tana tsara yanda zata rabu da ciki!
Tana komawa gidanta ta zauna falo, ko kayan bata iya cirewa ba tsabar tana cikin tashin hankali, fatar jikinta kuwa du ta yi ja abinka da jan mutun,
Tv ta kunna ta kamo tashar labaru,
An yi sa.a kuwa ana watso labarun su Aisata kan an yi bincike har an fara cafko masu shigo da kwayar, inda alkali zai yanke masu hukunci, , nan aka hasko sunnanta baro baro hade da sunnan mahaifin wardugu, aka fadi cewar ta bada hadin kai wajen kamo wasu masu harkar dan haka zata samu sasauci kan hukuncin da aka yanke mata,
Tsaki ta ja ta kashe tv din ta mike nan ta shiga baci domin ji take tamkar idannuwanta na dauke da yaji ne dan tsabar nauyin da su kai mata.
Wardugu na tsaka da aikinsa aka shigo aka shaida masa Marahut na son ganninsa, a shigo da shi ko kuwa?
Wardugu ya dafe goshinsa, a ransa ya ayanna me ke damun Elhaj Marahut ne da zai mayar min da office wajen zuwa haka?
Umarnin a shigo da shi ya bayar , ya ci gaba da aiyukansa yana hada takardun wasu yan gudun hijira ne da aka kamo , ya duduba da kyau ya ga du yawanci yan libia italia da dai sauran su, yana son mika su hannun likitoci a duba lafiarsu kafin su yi masu takardun tafia su juya garuruwan su!
Shigowa Marahut ya yi ya zo ya zauna saman kujerar zaman mutun daya yana duban Wardugu,
Kai shima yana alfahari da namijin yaron nasa, suna mugun kama aman ko a zamanin da yana saurayo bai kai Wardugu tsayi da yannayin karfi da cikowa irin nasa haka ba,
Murmushi ya yi masa ya miko masa hannu ya ce" Asalamu alaika Wardugu
Dago da kansa ya yi , a nitse ya miko masa hannun shima ya amsa da" amine wa.alaika salam *Elhaj Marahut*.
Murmushi ya kuma yi ya rike hannun na wardugu, sam baya son sakin hannun, rabonsa da rike hannun yaron har ya manta,
Da ido Wardugu ya yi masa nuni da ya cika shi mana?
Sakin hannun ya yi , a nitse ya ce" Wardugu sunana kake kamawa haka ko?
Wardugu ya dube shi, ya yi masa murmushi ya mayar da dubansa kan takardarsa,
Ka saka baki wajen alkalin nan ya sasauta mata hukuncin da ya dauka a kanta, kaso har na shekara biyar ya yi tsauri Wardugu,
Wardugu ya dago yana dubansa , ya ce" ka san ba hurumina bane, sannan bana saka hanuna a irin haka, kaima ai kana da hanyar hanata yin kason ma domin ka fi ni fada a ji a wajen su,
Wardugu sunana zai bace Wardugu, sannan hakinta a kaina yake! Marahut ya fada yana dubansa da yannayin iya gaskiyarsa kennan
Wardugu ya ce" ni nawa sunnan sai na kai na dulmiya ko? Ah koda yake daman sunana a bace yake a bakin al.umar da suka aikata laifi, sai ya yi ta baci jar a bakin wa.inda basu taka dokar bama?
Marahut ya dafe goshinsa, ransa ya fara baci ya ce" har sai yaushe zaka daina mugun fushin nan a kaina? Ni fa na haife ka! Baka tsoron goben ka? Kai idan naka suka ki yi maka biyaya fa? Wardugu ba laifina bane abinda ya faru a baya ,
Wardugu ya dube shi ido cikin ido ya ce" wannan tsohuwar magana ce Marahut, kana iya tafia ba zan saka bakina a maganar iyalinka ba!
Wardugu! Ya fada da dan karfi yana mikewa,
Wardugu ma ya mike ya ce" Marahut!
Marahut ya tsura masa ido, a hankali ya ce" dan na kula wata, na aureta , ba laifina bane, laifin uwarka ne! Sannan dalilin halayan da na gane nata na rabu fa ita yanzu,
Wardugu ya hadiye abinda ya tsaya masa a wuya, ya karya kansa ya ce" sai dai yanzu Wardugu bashi da budurwa bare ka kwace,
Marahut ya daga hannunsa ya zabga masa mari wanda ya yi mugun kara kara, ji kake tas, ya maya masa a gefen kuncinsa wanda hakan ya sa hularsa dagawa,
Kan Wardugu a kasa a hankali ya dago jajayen idannuwansa ya sauke a fuskar mahaifinsa, Mahaifinsa, ubansa, wanda ya haife shi, a yau ya so a ce wani ne ya kai hannunsa jikinsa, kai kai kai, balaki,
Ido cikin ido suke duban juna, Marahut ya ce" ko me ka zama, ko me kake takama da shi dai haihuwarka aka yi, na yi tunanin rashin mutuncin naka zai saka ka daga hannu ka rama! Ka rama marin mana Wardugu!
Wardugu ya sakar masa murmushi mai ciwo , a hankali ya ce" ko shege mai mutunci ba zai rama ba bare kai da ka haifi dan halal ka bashi tarbiya?, kar ka daga murya yarana su ji, domin ban san in zan iya rike kowa, wai ina gudun ba nan gaban idona ba, ka san soja shegen yawo ne da shi, gashi da ramuwar gaya,
Ka je kawai Marahut.
Jikin Marahut ne ya yi sanyi, ji yake dama da hali da ya rungume shi ya shafa wajen da ya mare shi ya bashi hakuri,
A hankali zuciyarsa ke sauka har ya ji dumbin kaunar dan ta kuma mamaye khalbinsa bashi da wani , baya tunanin zai samu daga shi, fatansa su sauko daga dokin zuciyar da suka hau bisa gangancinsa, sai dai ya rasa yaya zai yi, shi ba zai duka gabansu ya basu hakuri dan ya kara aure ba, su ya dace su yi hankali su zubar da makaman yakin su, yanzuma ba wai ya zo ne dan Wardugu ya yi magana harkar Aisata ba, shima yana iya sakawa a saketa aman ya barta ta je ta yi kasonta kawai domin ta taka doka, ciki harda ta musulunci , da aurensa a kanta take bin wasu mazan.
Ya zo me dan ya kara ganninsa su sami hira ta kusanci na da da uba, sai dai ga yanda ta kare,
A hankali ya juya dan barin Office din,
Ja ya yi ya tsaya, a hankali ya dawo ya dube shi, hularsa da ta dage ya janyo ya gyara masa a kansa, ya gyara masa gaban rigarsa da kyau ya ce" Allah ya yi maka albarka, na yafe maka dukan abinda ka yi min wanda na sani da wanda ban sani ba, Allah ya kare gabanka da bayanka!
Yana gama fadar haka ya juya ya fice a office din,
Ran Wardugu a cakule ya hade takardun ya fito gaba dayansa a haukace ya mikawa Lieutenan Jalo takardun bai masa magana ba yana kallon mashin dinsa ya fice ya bar shi a wajen aikin ya kama tafia a kafarsa cikin sauri, ya yi niya a kafa zai je gidansa ba zai hau mota ko mashin ba, ya ki din , kai bama zai kuma hawa ba! Zai je a kafarsa , du wanda ya fasa kawo masa wargi ya ki Allah! (🥴 wani da laifi , wani da shan duka? Tap🤔),
Bayan kwana biyu, fitina ta dan lafa gefen Wardugu,
Juma.a ce yau, ranar da ake bada damar shiga gannin yan gidan kaso harma a dan jima a wajen su,
A wannan ranar ne mutane ke cika prison dan gannin nasu,
Wannan damar Walyn ta rike ta yi shiga irin ta larabawa ta yane kanta da dan kwalin bakar abayar da ta saka ta yane har habarta sannan ta saka bakin gilas,
A kafa ta samu ta fito bakin titi nan ta ja ta tsayar da mai taxi ta yi shatar ita daya.
Basu zame ko.ina ba sai justice ta ciri takardar gannin dan prison ya dauketa ya sadata da gidan kason,
A hankali ta cire gilas din idonta, sannan ta dan ja mayafin dan bude habarta dan kar ta jawa kanta matsala da masu tsaron gidan kason
Takarda ta nuna, ta je saman kuje ta zauna inda aka shiga aka kirawo mata wanda ta zo nema,
A hankali take takowa har ta karaso wajen warda aka nuna mata a matsayin uta ke nemanta,
Kallonta take, irin kallon san sannin wacece? Hakan ya sa Walyn ta bude rufarta dan ta shaida ta,
Murmushi Aisata ta yi tana dubanta, aman a kasan zuciyarta mugun kishin Walyn take, kai da tana da dama da ita ce ajalin yarinyar da ta auri gwarzonta!
Walyn ta kare mata kallo sama da kasa, cike da yanka da jan aji ta ce" *wanene shi*?
Bata amsa ba , sai da girarta irin na rikakun yan duniya da suka san kansu ta yi mata tambayar *Wane?*
Walyn ta fara shaka ta dubeta da kyau ta ce" *waye malamin da ya miki aiki kan Wardugu da mahaifinsa?* waye shi?, idan kika fada mani komai, zan saka a fitar da ke daga wajen nan.
Murmushin rainin hankali ta yi tana dubanta, cikin kissa ta ce" kina da damar sakawa a fitar da ni din ne kika shigo cikin gidan kaso dan samu adress din malamina?
Kina son samun kanki ne a wajen Gwarzona?
.........