'Dakin da ta gama gyarawa ta shiga ta sa kayanta daga gefe...
Nan ta takure guri guda tana mai had'a kai da k'afa,tana tunanin wannan rayuwar da ta tsinci kanta a ciki...
Zaman dirshan ta yi bacci ya gagareta,banda koran sauraye babu abunda take,wanda shima da k'yar take iya d'aga hannunta,daga k'arshe ma kasawa tayi,haka ta bar su tanaji tana gani,suke kawo mata farmaki...
Bakinta banda motsi babu abunda yake,da kallo kasan ba abunda take da ya wuce addu'a...
A daddafe tayi sallah daga zaune,ko addu'ah bata samu daman yi ba,wani wahalallen bacci yayi gaba da ita...
Cikin wani irin yanayi na mutuwar jiki haka ya mik'e ya fita,yayo alwala ya dawo,a d'aki yayi sallah ya idar,haka ya zauna yana tunani amma ya rasa mai zai tuna...
A ganinsa akwai wani abu mai muhimmanci da yake son tunawa da shi,amma ya kasa tuna wannan abun...
Badan ya soba haka ya k'yale kansa,yana mai mik'ewa yayi hanyar fita daga gidan....
***********
Sai wajen k'arfe 12:30pm KHUBRA ta farka...
Idanunta take bud'ewa a hankali,duk sun kumbure saboda bata wani samu isashshen bacciba...
Sai da ta gama bud'esu tar,sannan ta mik'e ta zauna,sai da ta zauna ta huta...
Jikinta ba kamar da dare ba,yanzun har tana iya mik'ewa sosai,kantan kuma ta d'anji sauk'insa...
Tsaf ta share gidan ta,d'ebi ruwa tayi wanka,haka ta zauna a tsakar gidan,rana sai sake matsowa inda take.....
MA'U ce ta fito daga d'aki tana mik'a,ta nufi band'aki kamar wacce ake tunkud'awa,haka ta fad'a band'akin kamar an cillata,ko addu'ah babu...
Kamar sakkowar ruwan sama haka ta saki fitsarin da shigarta...
A ranta take fad'in
''Wama ya sani ko ta fara a kwance ne?''...
***********
Ba tare da tunanin gaida mahaliccinta ba ta shiga neman abunda za taci, rashin komai a gidan, yasata bazama neman MALAM BUBA haka take cilla fasassun k'afafuwanta...
Kitchen ta sake lek'awa neman duniya tayi aciki babu komai cikinsa sai busashshen k'anzon tuwo ta tsinto...
Haka bbau komai ciki bare mahad'i tayi ta garzarsa kamar akuya har ta cinye,sannan ta fito daga ita sai d'aurin zani iya k'irjinta....
Sai bayan ta samu nutsuwa ta zo mata tukun,wani tsoro ya sakko mata,tunanin abunda ya faru jiya ya dawo mata,nan ta tafi duniyar tunani...
''Shin yanzun idan duka wannan abun ya tashi a tutar babu fa suyi yaya ?''
Tunaninta ya tsaya kan da me zata biya kud'in aikin idan har aikin yayi,nan take wani mummunan tsoro ya sake cika zuciyar LADIYO....
''Idan zaki iya ki je ki nemo garin kwaki,a shago''....
Tayi tafiya mai nisa sosai sannan da tambaya ta samu ta siyo..
Kamar kowane lokaci haka take tafiya,kanta a k'asa,tafiya take har ta kusa da gida...
Da sauri ta d'ago tana kallonsa kamar zai fad'o kanta saboda yanda yake layi....
Idanunsa sun gama rinewa uwa an watsa musu colour....
Wani dariya yayi yana mik'a hannu da shirin damk'ota,yana fad'in
''Y'an mata zo mana''...
Sunkuyawanta shi ya bashi damar dank'an iska,ya sake mik'o hannu zai sake kamota....
Tai ciki a guje sai d'akin MA'U wanda tana kwance tana jiran dawowan KHUBRA ta ji an fad'o d'akin,kamar an tsikareta ta mik'e tana dafe chest enta....
Cikin tsoro kamar ita tayi gudun ta hau haki tana fad'in
''Me ya faru?''....
''Caarrr uba dama wai abunda kikema gudu kenan,shegiya y'ar bak'in ciki,kin zo kin wuce ko kuwa sai na b'ab'b'laki.............
_____________________________
Ganin tana neman raina mata hankali yasa MA'U ta fice ta nufi d'akin shirginta...
Fitowa KHUBRAN tayi daga d'akin dan tun da taga ta fita tasan ba zasu kwashe ta dad'iba..
Ta d'an jima a tsaye a waje kafin ta juyo ta dawo da k'arfin gwuiwarta...
Kanta a k'asa ta gagara d'agowa...
''Bani abunda kika samo''...
''Wallahi BABA banma ganshiba da na fita ''....
Tun zuwanta garin wannan shi ne karo na farko da wani abu ya shiga cikin hanjinta,baya ga k'uli² da tayi ta k'amusa....
Tana gamawa ko mintuna 10 bata k'araba a gidan tak'arawa k'afafunta wuta....
Wannan kukan kuma bana son ganinki kina min asarar wad'annan precious tears en''...
Kafin yaja hannunta yana fad'in
''Muje muyi fira toh''
Ya shiga janta zuwa wani k'ayataccen garden....
Can daga gefe wasu fararen tattabaru ne suke shawagi daga sama zuwa k'asa suna wasansu,sai kukan tsuntaaye da ya dad'a k'awata shirun gurin...
Sai wasa take da bak'in suman kansa..
Idanunsa a lumshe kamar mai bacci,zuwa can ya mirgina yana kallon fuskanta...
A hankali ya shiga bud'e eyes ensa da suke brown colour tsakiyansu da wani haske tamkar na mage...
Fuskanta ya tallafe da hannu,ya dad'a matso da ita yanda suna jin fitar numfashin juna...
Bai jira komaiba ya had'e bakinsu guri d'aya sun jima haka,kafin wasan nasu ya canja salo....
Sunyi nisa acikin wata duniyar,wanda gaba d'aya KHUBRA a tsorace take da al'amuransa...
Kuka ta fasa masa,wanda ya sashi cikata babu shiri,yana kallon cikin idonta..
Yin haka dai² yake da nuna rashin kulawarki a gareni''..
Da sauri ta rik'o hannunsa tana girgiza masa kai...
Cikin wani irin murya ya soma fad'in
''Idan har na tafi daga gareki a yau ba zan sake ko da waiwayowaba...
Wancan lokacin na juyo zuwa gareki,amma wannan karon kada kiyi tsammanin sake ganina''..
Dafe saitin zuciyanta tayi saboda wani irin matsanancin bugu da yake mata...
Ta kasa fuskantar komai da ya danganci mafarkin nata,hatta kuwa da fuskansa da ta gani,ta kasa tunawa...
Tashi tayi da niyyan yin alwala,sai dai abunda ta gani ya sata fara kuka kamar wadda ake fitarma da rai....
Tunda ta fuskanci MALAM BUBA baya gidan yau kam,kuma zaiyi wuya ta ganshi....
'Bangaren MA'U kuwa yini tayi neman abun duniya,sai sake cigiyan gidajen aiki take dan ita har ga Allah wancan ya mata arha da yawa...
Duk da bawai yau ta fara ganin hakan a tare da ita ba,haka ta zauna tana kukan...
Coz ta san halin MA'U za ta iya cewa yawon iskanci taje....
Sai bayan Maghreb sannan MA'U ta dawo a matuk'ar gajiye kamar wacce akawa duka haka ta shigo tana raba k'afa..
Haka yayi ta zamansa a waje,da yaje kasuwa ma k'odagonsa,bayan ya tashi k'in komawa yayi...
Kamar wacce aka mintsina haka tayi saurin mik'ewa tsaye tana raba ido...
Wani durowa ta nufa,daga jikinsa kuma cikin wani d'an sak'o,ta mik'a hannu,poly bag en dake wajen ta janyo ta hau bud'e cikinta,tana fito da kayan dake k'unshe a ciki...
Suphagetti ne da d'an dama dan idan basu fi 10 ba to zasu iya kaiwa hakan...
K'waya d'aya ta d'auka ta nufi hanyan fita daga d'akin,a zuciyanta kuma tana sak'e²,har ta k'idasa ficewa...
Hankalinta gaba d'aya baya tare da ita a wannnan lokaci,tayi zurfi wajen tunaninta,tana son tuno wane garima dangin mahaifiyarta suke?
Shigowar MA'U d'akin shi ya sata dawowa duniyarta babu shiri,cikin wani irin kallo ta jefeta da shi tana mai mik'o mata suphagettin dake hannunta,ba ko bayani ta sa kai ta fice..
Ita kam KHUBRA da ido ta bita dan zuwa yanzun ko dai bata gama sanin halin MA'U ba duka to tabbas ta san mafi yawan kaso daga halayentan..
Cikin sanyinta ta mik'e had'e da zare hijab en dake jikinta,ta fice tana sak'a da warwara...
Juyewa tayi ta d'auka ta nufi cikin d'akin nata,tana ajiyewa ta juya ta fice...
Sai da ta gama k'oshi sannan ta shiga rafka mata kira...
Cikin sauri ta shigo tana sunkuyar da kanta k'asa...
Kwanciya tayi cike da son ganin mutumin ta na mafarki,tana wannan tunani har bata san lokacin da bacci yayi gaba da itaba...
Banda sak'a da warwara babu abunda take,zuciyoyinta biyu kowanne tana kawo mata shawaran da a ganinsu shi ne masalaha....
''Shin dama tana iya tashi da wuri haka,amma kullum sai ibada ta wuceta?''...
Tana nan tana tunane² har bata san lokacin da MA'U ta gama shiryawaba,sai ganinta tayi ta fito hannunta rik'e da y'ar jakarta wacce akewa lak'abi da *_(JIK'ATA GUMIN HAMMATA)_*...
Naira #50 ta mik'a mata ''ki siyo garin kwaki''...
Daga haka ta wuce ta fice,har tayi nisa ta dawo,KHUBRA dake sunkuye har tsoro abun ya bata dan bata ga lokacin da ta dawo ba,sai magana taji a bayanta....
Haka ta shud'a tayi gaba....
Ko da ya farka da safe lokacin gari har ya gama haske,rana tana shirin mamaye sararin samaniya...
Istighfari ya shiga yi,coz har aka idar da sallah bai san anayi ba,abunda a iya tsawon rayuwarsa yau ne rana ta farko da yayi rashin sallah a jam'i...
Da matuk'ar k'unar zuciya ya mik'e ya fita don d'auro alwala...
Ta gabanta ya zo zai wuce,cikin rud'ewa dan tasan zai mata fad'an rashin sallah a kan lokaci ne,ta hau fad'in
''MALAM barka da tashi''
Ba tare da tayi tsammanin zai amsa ba...
''Lafiya k'alau MALAM''
Tana yi tana kwarkwasa kamar wata tsohuwar y'ar duniya...
Ganin haka yasa itama LADIYON ta nemi guri ta k'ame kamar soja tana jiran ganin me zai kuma biyo baya...
Tana idarwa zata shiga d'aki taga ya biyo bayanta,da mamaki ta sake kallonsa,har ya shige d'akintan,ita kuma ta dafa masa baya...
''Yi sauri kisa hijab muyi jam'i''
After sun idar,ya shiga bata hak'urin abubuwan da yake mata,kamar wata uwarsa harda saka guiwoyinsa a k'asa....
Kallonsa tayi cikin mamakin hakan,ta kasa cewa komi...
Ita dai binsa take da kallo,shi kuma sai dad'a shige mata yake...
Su LADIYO da jin haka,bata san lokacin da itama ta biyewa MALAM en suka ci gaba da shafar juna,har zuwa MALAM ya samu damar da yake nema a agurinta na cilla k'wallonsa a kwando....
Ihuuu LADIYO take tana fad'in
''Aradu MALAM kasan takan wanga harka,wayyoo dad'i,MALAM ci gaba''...
Ita kuwa sai dad'a mak'alo shi take,kamar wata k'wad'uwa....
Fitowa tayi daga gidan tana tafe cikin nutsuwa kamar yanda ta saba,haka har ta isa shagon,ta mik'a kud'in ya bata abunda zai bata,ta sake kamo hanya ta dawo...
Ko da ta dawo gidan babu ruwa sosai,hakan yasa ta fita da bocket tayi ta faman jido ruwa a mak'otansu har sai da ta cika komai dake gurin...
K'ofar gidan ta je ta kulle ta dawo,d'akin MA'U ta shiga ta kwanta a saman gadon MA'U tayi d'ai²,take kuwa baccin wahala ya d'auketa....
'Dakin ya sake dawowa,bai san dalilin da yasa yake jinsa wani iri ba,kamar mara lafiya...
Tayi nisa a baccin,ta hangoshi kamar kowane lokaci cikin fararen tufafi,binsa take amma ta kasa cin masa,hakan ya sa ta durk'ushe tana kuka mai tsanani..
Gidane guda d'aya wanda ba shi da mak'ota ko k'waya...
Tunkarar gidan tayi ta shiga k'wank'wasawa ganinsa a kulle....
Murmushi tayiwa yarinyar ta bita suka shiga ciki...
A wani d'aki aka sauketa ta nemi guri ta zauna tana jiran fitowar MALAMIN...
''Na amince''
Ta fad'a tana jiran ganin,me zai biyo baya...
''Wannan ya nuna layun,zaki binnesu a tsakiyar hanyan da jama'a suke bi...
Shi kuma wannan k'ullin ya nuna mata garin maganin,za ki barbad'a a bakin k'ofar d'akin da kija san za ta tsallaka....
Ki tabbatar ta tsallaka shi,saboda shi ne cikon aikin ki,zai sa mata farin jini wajen mutane,sai dai babu wanda zai zo da niyyar aurenta,zaki samu mahaukatan kud'ad'e ta dalilinta''......
Jin an ambaci mahaukatan kud'i ta shiga b'are baki,dan murna....
Sannan ta mik'e,ta d'auki garin kwakinta tayi waje.....
Tayiwa Allah godiya,ta sake kwanciya,tana tunani kan wannan rikitaccen mafarkinta.....
Sai lokacin wani tsoro ya ziyarceta,take kuwa ta sake k'ulewa a d'akin MA'U....
Addu'ah ta jima tanayi,duk da babu halin tayi sallah,haka taita kai kukanta ga Allah akan neman sauk'i da sauyin rayuwa, wanda k'arshe sai da takai kusan asuba bata koma baccinba...
Da k'yar ta samu wani nannauyan bacci yayi gaba da ita....
*********
'Dakin da KHUBRA ke kwana ta nufa daga inda take a bak'in k'ofan ta lek'a sai dai duk iya hangenta bata gantaba,murna ta koma tana yi har da rawa na samun nasara...
Har za ta koma d'akinta ta dawo tunowa da maganar da MALAMIN ya mata,akan idan har wacce akayi dominta ta tsallaka babu komai dan ta bi ta wajen...
Cikin salo na bariki ta shiga tashin KHUBRA kamar da can haka take yi idan zata tashe ta....
''Yar lele tashi maza kiyi wanka,ga abinci can na tanadar miki,maza taso kiyi wanka,zanje kasuwa zan siyo miki kaya,maza yi sauri kinji ko''
Haka taita tunane²,tayi wankan ta fito,jikinta duk yayi sanyi..
Dai² lokacin MA'U ta fito daga d'aki tana fad'in
''Kiyi maza ki shirya kinji ko,zani kasuwa na dawo,kada kiyi girkifa,idan na dawo zanyi komai kinji y'ar lele''
Fuskanta a sake take ta faman zuba kamar lalatacciyar mota,har ta fice daga gidan tana magana wanda ita kam KHUBRA batama san me take fad'aba coz tayi nisa cikin duniyar tunani....
Bata tsaya b'ata lokaciba ta d'auko ta ajiye a k'asa ta shiga bud'ewa...
K'amshi ne ya daki hancinta,tabi abun da ido,indomie ne da wainan k'wai a sama,sai turiri take,take ta shiga had'iyan miyau,haka ta bud'e jug en nan kuwa ta tarar da shi cike da tea mai kauri....
Ci tayi sai da ta tabbatar ta k'oshi tayiwa Allah godiya bisa ni'imar da yayi mata,na azurta ta da irin wannan abincin da tun da tazo garin bata tab'a cin kamarsa a dad'i ba...
Tambayoyi dayawa taitayiwa kanta,sai dai babu amsa,ta barwa ranta koma mene ne ta tabbata shirin cutarta take,take kuwa ta hau kuka tana addu'ar neman tsari daga dukkan abun sharri....
Tashi tayi za ta karb'a ita kuwa MA'U ta hanata,haka ta k'yaleta,guri ta samu ta zauna nan ta shiga fito da kaya tana d'agawa tana nunawa KHUBRA sai zuba take...
Kayan marabarsu da babu d'aya,ita kuwa sai binsu take da ido daga KAYAN har MA'UN da ta siyo...
*********
_(Gareku matan aure da y'an mata masu niyyar yin aure,ba ko wane sirri ake fad'awa k'awa ba,bare kuma har ki saki baki ki fad'a mata sirrin yadda kuka kwanta ke da mijinki,ko da kuwa ciki d'aya kuka fito,ahir d'inki da fad'in wannan sirri dan gujewa fad'awa a halaka,,,,,Allah yasa mu dace)... ameen....._
Ita kuwa TABAWA dad'i ne ya cika ta jin yadda LADIYO ta kwance mata sirrinta,tana rakata da harara tana tab'e baki,dan burinta bai wuce ganin LADIYON a k'asa ba.....
**********
Ita dai kamar mai koyan kallon wani abu,irin wad'anda akayiwa aikin idanu haka ta zama ranar,duk inda MA'U tayi idanunta na kanta kamar zasu fad'o saboda kallo....
Itama cikin shirinta suka fito,da tambaya suka nemi MALAMIN da yake gyaran targad'e...
Ai kuwa sunyi masa bayani,MALAM na kama k'afar MA'U ya soma matsawa,ta shiga kururuwa,bige² take da hannayenta da k'afa...
Amma MALAM bai saki ba,sai da yatabbatar ya gyara sannan ya saketa...
''Yau kuwa kin fito daga d'aki?''
''Baki gane ba ko?''
''A'a ban tashi da wuriba ai yau,sai lokacin da kika shiga sannan na tashi''...
Shiru yayi har ta gama,sannan ya sake mata bayanin da yayi mata tun farko,aikuwa saiga MA'U tana kuka,hak'uri take bashi kan idan da hali a karya abun...
Shi kuwa yace mata
''Ai aikin gama ya riga da ya gama,sai dai kuma kiyi hak'uri''....
''MALAM ina son a k'ara mata k'arfin sha'awa ta yadda duk wanda yazo mata da buk'atarsa baza ta iya jurewa ba''
Shi kuwa MALAMIN take ya bata guri yana fad'in
''Har yanzun kina da damar yi mata wani aikin''
A ranta kam ta k'udirce ko za tayi yawo tsirara sai taga bayan KHUBRA...
Nan ta lula duniyar neman mafita..........
Haka ta dawo gida,ita kuwa KHUBRA duk lokacin da zata tuna abun sai ya bata dariya,yanda MA'U taita fisge² da ana mata gyaran k'afa d'azun,ita ko dukan da ta mata bai sata jin haushin MA'UN ba,saima tayi dariya idan taga gilmawar MA'UN...
Da tasamu sarari kuwa MA'UN ta fita ta zauna taita tuntsira dariya kamar wata sabon kamu...
Kallon KHUBRA tayi da ta sunkuyar da kai k'asa kamar gaske,ae ko ta maka mata wata uwar harara,tana shigewa d'aki...
Tun da ta fito KHUBRA ke k'unshe dariya dan har mantawa take da ita a cikin gidan coz ta san ba zaman gidan take ba...
Mai NAPEP ta samu,tsaf ta masa kwatance,dai² k'ofar gidan ya sauketa,ta shiga da sallamanta...
''Ina fatan dai kin ganeni koh?''
''Kinga tunda nace zan dawo Allah bai nufaba,sai yanzun,da yake na d'anyi jinya ne shi yasa kika jini shiru''
Matar ta fad'a tana sauraron MA'U...
Kamar wancan lokacin ya zayyano musu abunda ya faru tun daga tafiyarsu kawo yau da suka dawo..
''Dalilin dawowarku shi ne,Mijin naki ya fito miki da wani hali,idan yasa k'afa ya fita baya dawowa sai tsakar dare''
Nan taita d'aga kai kamar k'adange tana fad'in
''Haka abun yake''
Burinta a yanzun bai wuce ganin KHUBRA a cikin mawuyacin hali ba,shi yasa ranta fes ta nufo titin da niyyar hawa mota..
Shiru tayi ta kasa magana,jikinta har rawa yake,lokacin da ta ganshi
''Hajiya ina zuwa ne?''
''Yi sauri ki cewa mai mashin a waje,ya shigo bani da lafiya,ke kuma ba zaki iya d'aga ni ba''
Tsawa MA'U ta kwad'a mata da yasa ta fice a guje..
Tana haki take fad'in ''dan Allah bawan Allah ka temakamin bata da lapia karta mutu''
''Fita KHUBRA zamuyi magana''
Umarnin da MA'U ta bata kenan,tuni tasa kai ta fice daga d'akin,ta koma nata tana jimamin halin da take ciki...
Tun kafin rana ta take MA'U ta kira KHUBRA akan ta had'a kayanta,baiwar Allah tayi tunanin ko gida za a kaita,tana ta murna...
''BABA MA'U ina zamuje ne?''
Ta tambayi kanta,ba tare da samun amsa ba......
A parlor suka tarar da ita ta hikimce kamar basarakiya,tana murmushi ta amsa musu,suka shigo suna zama,a k'asa kan rug KHUBRA ta zauna tana gaishe da hajiyan,ita ko MA'U ta hakimce akan sofa,suna gaisawa cikin sakin fuska..
Yanda MA'U ke k'asa da kai,sai ka rantse matar ta girme mata,ta mata bayani tsaf game da KHUBRA,lokacin da MA'U ta ambaci sunan KHUBRA matar ta bita da kallo hakan yayi dai² lokacin da KHUBRAN ta d'ago kanta....
Sai da taji wani mugun fad'uwar gaba,kan tsananin kyau d'an usul da ta gani a tare da KHUBRAN,a hakanma wai dan tana matsayin y'ar k'auye,ina kuma ga ace ta waye?''
Tunani iri daban² haka haka matar da ake kira HAJIYA MURJA take a ranta,a fili kuwa sai murmushin yak'e take uwa an mata dole...
Cikin sakin fuska wanda da gani bai kai zuci ba,haka suka rabu da MA'U,ta mata alheri na Soap ne da su detergents a cewarta tayi wanki...
Cike da murna MA'U ta amshe ta k'arawa k'afafunta wuta,ko sallama bata jira sunyi da KHUBRA ba....
Dawowar matar daga rakiyan da tayiwa MA'U tana dad'a mata godiya,tayiwa KHUBRA dake zaune wani wawan kallo,ko me hakan ke nufi? ohoooo....
Da gudunsa ya nufeta yana tab'ara,ita kuwa ta biye masa
Fad'in d'aya daga cikin y'an matan
Tana yi tana tana yatsina fuska,duk da fara ce ba zaka sata a sahun masu kyauba,sai dai kawai kud'i da suka hana a gano hakan...
''Hajiya gani ASHNA tace kina kira na''
Inda hajiyan ta nuna ta kalla,aiko cike da farin ciki ta k'araso kusa da KHUBRA tana mik'a mata hannu
''Suna na ZUHRA kefa y'ar uwa?''
Cikin halin ko in kula take maganarta,murmushi KHUBRA tayi mata tana mik'a mata nata hannun
''KHUBRA suna na''
''Kinga ZUHRA ki kiyayeni wallahi bana son rawar kai,har zuwa yaushe zaki gane matsayinki?''
Ta k'arasa tana zabga mata harara
_BAKIN RIJIYA BA GURIN WASAN MAKAHO BANE_
So ki tsaya iya matsayiki,karki manta mun kawoki ne dan kiyi mana bauta,ina fatan zaki kula da aikinki''..
''Wuce ki rakata d'akin y'an aiki''
Ta fad'a a tsawace
''Dan Allah kiyi hak'uri da duk abunda hajiyanmu za tayi miki,wallahi haka halinta yake,kaf y'an aikin gidan nan basa jimawa idan ankawo,dalilin halintane suke barin aikin''
Ta d'an saurara tana kallon KHUBRAN
Har da y'an kud'ad'ensa ya kawo ya bata ita kuwa ganinsu ta dingayi kamar ya bata duniya...
ZUHRA ce ta fara sakkowa,har k'asa ta gaida hajiyan,tana amsawa da k'yar kamar ba y'ar cikinta ba...
''Me kika manta?''
Tana aiki ZUHRA na mata hiran yanda gidan nasu yake,kamar ta tambayeta,har ta kammala girkin duk da ba wani sanin abincin zamani tayiba tayi k'ok'ari,haka ta jeresu a dinning kamar yadda ZUHRA ta nuna mata,ita kuma tana tayata...
''Laaaaa!na manta ban baki labarin YAYANMU ba''
ZUHRA ta fad'a tana washe baki
Tayi maganar cike da jin dad'in yanayin da take ciki
Kwanaki sun riski KHUBRA a cikin gidansu ZUHRA wanda bayan ZUHRA babu da wanda take sakewa,bayaga haka kuwa bata wani samun sakin fuska daga sauran y'an gidan bama kamar k'ananan da kana yi musu magana zasu maka rashin kunya komai girmanka kuwa,hakan yasa ko me za suyi KHUBRA bata musu magana.........
Wannan kenan....
Duk lokacin da ta fad'a kuwa nan ZUHRA zata sata a gaba tana dariya uwa ta samu shashatau en madina....
Cikin shirinta ta fito zata gidan da KHUBRA ke aiki,dana kalleta sai da taban tsoro,saboda abun natama k'aruwa yayi,bayaga neman kasuwartata,fuskanta a kwailaye take ta sha mai,tamkar budurwa haka ta koma...
Itanma kallonsa tayi dan bata sanshi ba,tana fad'in
''Malam lafiya?''
Sai da ya gama k'are mata kallo kafin da k'yar ya soma magana muryarshi a shak'e
''Ko kece MA'U motar haya?''
Take ta bud'e k'ofan d'akin,suna shiga suka mannewa juna,dama masu jiran k'iris daga shi har itan...
Tsawon awa uku sannan suka hak'ura badan sun gajiba,sai don kiran wayarsa da ake ta fama...
Ya saki wata uwar dariya yana kallon MA'U da tayi laga² akan gadontan,duk ta wani bud'e k'afafu...
''Yahhh!ko kina buk'atar k'ari ne? naga kin kasa tashi''
Yanayi yana sid'e leb'e,an gama oga,ya fice yana zabga masa harara..
MA'U banda ihu ba abunda take,dan kuwa wannan mutumin maimakon ya nemeta ta gaba,shi biyu ya had'a,sai da ya gamsu son ransa sannan ya kyaleta..
Shi kuma ya fice da alk'awarin dawowa zuwa dare............
.
''Haka dai kullum kike gani,a zatonki ba zan gane ba ko?''
Ta juya taga ita ASHNA ke kallo,hakan ya tabbatar mata da cewa da ita take,kanta a k'asa ta je inda take...
''Kije d'akina zakiga kayan wanki na ki d'ebo ki wankemin,bani da kayan sawa''
Tana gama fad'in haka tayi hanyar d'akin HAJIYA MURJA tana rafka mata kira uwa wata sa'arta ba mahaifiyarta ba..
''Ya akayi y'ar lele?''
Ta tambayeta tana fitowa daga toilet..
Uwa za ta fashe kan haushi...
Tafice uwa zata tsaga ginin da take takawa...
''Ke don ubanki har kin isa a saki aiki a gidan nan kik'i yi?wace ce ke da zaki k'i?''
Sosai taji wani abu na sauka a ranta jin zagin da akayiwa mahaifinta da take tsananin so a duniyarta,duk da ranta ya b'aci da zagin,haka ta daure ta soma bawa hajiyan hak'uri
''Wollahi hajiya ba yi ne bazanba,kawai cewa nayi mata tayi hak'uri wanki baya cikin aikin da zanyi a gidan nan''...
Wani mari da hajiyan ta mata shi ya katse mata magana,take ko ta dafe gurin tana dad'a sunkuyar da kanta..
''Maza ki wuce ki d'ebo kayan,duk da babu shi a yau na k'ara miki dashi acikin aikin naki''
Tana gama fad'a ta juya tayi wucewarta tabar KHUBRA da dafe da kunci...
A washing machine taita sawa tana wankewa,da yake tana taya ZUHRA wani lokacin,kuma itama takan wanke nata,haka ta b'ata lokaci mai tsawo tana fama da kayan...
Tana cikin wanki ta jiyo muryan ZUHRA na kiranta,tana daga cikin toilet en ta amsata,aiko ta shigo...
Da mamaki ta kalleta tana fad'in
''Me kuma ya had'oki da wanki yau?''
Murmushi kad'ai tayi,bata iya cewa komaiba,haka taita fama da wankin ita kuma ZUHRAN na tayata matse kayan,tsaf ta gama lokacin ana kiran sallan isha..
''Kiyi maza kije d'akin mai gidanki,kisan yadda za kiyi ku samu wata alak'a ta shiga tsakaninki da shi a yanzun kafin b'illowar alfijir idan kikayi haka,duka buk'atunki sun gama biya kenan''......
Da yake bai da magagi ya bud'e ido,suna yin arba da juna tayi cilli da zanin jikinta...
''Sannu MALAM ciwo kan ke maka?''
Wani uban tsaki ta doka tana ficewa zuwa d'akin MALAM en...
Har aka kira sallah tana kan abun sallanta,sai da tayi sallah sannan ta d'an kwanta,aiko take bacci mai dad'i ya sake d'aukanta...
Sai lokacin nutsuwa tazo mata,ganin ta kammala cikin lokaci k'alilan,tayiwa Allah godiya,sannan ta fita ta shirya musu dinning..
A cikin kitchen en ta ci nata abincin,tana gamawa ta hau wanke²..
Dai² lokacin ZUHRA ta shigo,sad'af² ta biyo ta bayanta ta rufe mata ido...
Murmushi tayi tace
''Habaaa ZUHRA kinma mai dani wata abar tsokanar ki kenan,kina tsammanin bazan gane bane?''
*K'*afafunta saboda tsabar kid'imewa da tayi har neman kasa d'aukarta suke,kamar an cillota ta fad'o d'akin aiko bata jiraba ta afka kan MALAM dake ta sharara bacci abunsa...
Shafa shi ta shiga yi shi ko maimakon ya farka kamar yadda yayi d'azun saima dad'a gyara kwanciya da yayi,yana sakin numfashi abunsa...
Yanayin kwanciyar da suka yi kai da gani kasan ba shiryawa baccin suka yiba,dan kam da gani kasan suna tsaka da harka baccin yayi awon gaba da su.....
Jiki ba k'wari ta fita tayi wanka,bata tashe shiba dan kansa ya tashi yayi wanka,lokacin ko a takure ya ganta wanda ita kad'ai tasan halin da take ciki...
Sai da ya gama shirin ficewa tukun ya dawo
''Yahhh!d'an kawo wani abu mana''
''Ko zaki cemin oga bai sallamekiba?''
''Sai kin ganni''
Bata ko d'aga ido ta kalleshi ba bare ta bashi amsa.........
A parlor ta tarar da ita tayi shirim cikin sofa,har zata fita ta kwad'a mata wata tsawa,ba shiri KHUBRAN ta dawo dan ita kam a yanzun baza ta so abunda zai rabata da gidan ba,dan ko shi ne rufin asirinta a wannan halin da take ciki...
ZAHRA kam dama tuni ta riga kowa shigowa,nan tai ta mata sannu,haka suka shiga ciki...
Ko cikakken mintuna talatin batayi ba ta fito ta dawo gurinta aiko tare suka ci gaba da aikin shanya,har malaminsu na islamiyya ya zo,a nan ne ta barta ta tafi,har suka dawo bata kammala ba,k'arshe dai yinin ranar haka ya shud'e mata tana abu d'aya..
Wajen k'arfe goma na dare ta tattara ta ajiye su akan ta k'arasa idan Allah ya kaimu washe gari........
Da sauri ZAHRA ta rik'eta tana jan hannunta suka nufi kitchen,aikinta ta fara suna ta hira,duka yau tana kula da yanayin ZAHRA wani murna take tayi ita kuma tak'i tambayan dalilin,suna ta aikin su,can ZAHRA ta d'ago tana kallon KHUBRA...
''Wai kam sis kin san wani abu?''
Kai kad'ai ta kad'a mata kafin ta bud'e baki tayi magana ZAHRA ta katse ta da fad 'in
''Cikin month ennan YAYANMU zai dawo fa''
''Eeyyahh!Allah dawo da shi lafiya,yasa ya samo abunda yaje nema''
''Ameen dear,aiko zai sha labarinki duk ranan da mukayi waya''
Ita dai KHUBRA bata sake magana ba,ta ci gaba da aikinta,ZAHRA kuwa nan taita bata labarin YAYAN nasu,wanda har zuwa yau bata tab'a tsintar sunansa ba..
Tsawon awanni da dama suna ta aikin kafin suka kammala,ficewa suka yi bayan sun gama shirya table kafin kowa ya kama hanyarsa...
''Oyoyo my son''
Cike da ladabi uwa ba wanda ya fito daga k'asar turawaba ya gaidata,tana amsawa fuskarta da fara'a wacce ban tab'a zaton tana da ita ba...
Sam basu ji shigowar motor ensu ASHNA ba,sai shewansu suke KHUBRA na bata labarin k'auyensu,ita ko ZAHRA sai kwasar dariya take...
Tab'e baki tayi kafin cikin b'acin rai ta iya furta
''Tana can tare da wannan shashashar yarinyar''
''Wace wannan kuma?''
Yayi maganar yana yamutsa fuska...
''Wata ce''
Daga haka ko ta bar maganar ba tare da ta sake furta komai ba ta ja bakinta tayi shiru...
''Laaa!sis kinga lokaci ya tafi nasanma yanzu haka BB ya dawo,taso muje dan Allah''
Tana tafe da d'an gudunta ta shiga parlorn,idanunta na sauka kansa ta fasa wani ihu da gudu kuma ta fad'a jikinsa....
''Matsamin a nan,ai ke kam fushi nake da ke''
Ta fad'a tana narke fuska za ta masa kuka
Tana d'an murmushi had'e da lek'en fuskansa da ya kawar da ita gefe...
''Laaa!YAYANAH taso kaga abunda muka maka''
Ta kama hannunsa tana jaa zuwa dinning,a hankali ya bita har gurin tarin warmers en ya kallah yana tab'e baki,yasan dai wannan kam sai dai ko idan y'an aiki suka yi amma ba MAMAN ba bare kuma wad'ancan sangartattun biyu...
Drink en da take tsiyayawa a cup shi yabi da kallo sai k'amshi yake,murmushi yayi mata ganin yadda take ta rawar k'afa a kansa ya juya parlor ya kallesu duk sun zuba musu ido suna jiran ganin abunda zai faru,juyowa yayi ya sake kallonta yanda take masa yasa ya k'udirce a ransa ba zai bata kunya ba,ko da zai ci ya haras da shi zai gwada...
''YAH bismillah!''